Chapter 65
Chapter 65
wani had’add’en fari k’al d’in yadi d’inkin boda, yayi matuk’ar karb’ar jikinshi, ya murza sky blue d’in hula zanna bukar sai kyalli take yi, sawunshi sanye cikin farin takalmi sau ciki mai mugun kyau, sai silver agogo da ya d’aura a tsintsiyar hannunshi. K’amshin turarenshi ne ya sanar da Aslam fitowarshi! Dan haka ya bud’e idanuwanshi da suka yi jaa ya zuba mishi. Suna had’a ido Arshaad ya d’auke kai ya tamke fuska yayi hanyar fita. Murmushi Aslam d’in yayi kafin yace “Irin wannan tamke fuska haka! So kake idan kaje ka firgitata?” Banza Arshaad yayi da shi ya ci gaba da tafiyar shi. “You promised Aaima akan za kuyi magana kuma zaka kaita wajen Mammy, remember?” Arshaad ya sake jin muryar Aslam d’in. Ajiyar zuciya Arshaad ya sauk’e, bayan ya tsaya cak! Ba tare da ya juyo ba dan har ya kai k’ofa. Yafi 1 minute a hakan, kafin chaan! Ya juyo ya fara takawa zuwa inda Aslam d’in yake zaune. A kan 3 seater yake zaune dan haka shima ya zauna a kai a gefen shi kad’an, cikin nutsuwa yace “Are you ready to talk?” Murmushi Aslam d’in yayi kafin yace “About?” Cikin d’an b’acin rai Arshaad yace “Ok!! Shikenan, kaga tafiya ta.” Ya fad’a yana mik’ewa tsaye. A hankali Aslam yace “Ka san dai akwai abubuwa da yawa a kaina ko? How kake tunanin zan fahimci wanne kake nufi?” Iska Arshaad ya furzar kafin ya komo ya zauna sannan cikin kulawa yace “Akan abunda yake damun ka kwana biyun nan nake so muyi magana! Ka chanja Aslam, Abba ma sai da ya kira ya tambayeni ko akwai abunda na sani yana damunka, dan ya tambayeka kace mishi ba komai!. Na tambayeka tun a waya kace ba komai, yanzu gani nan face to face so talk! Ka gaya min ko menene idan na addua ne in tayaka idan kuma na taimakone in taimaka maka I hate to see you like this! Dan Allah ka gaya mini ko menene i promise to help.” Murmushi Aslam yayi kafin yace “Ba komai fa Arshaad. Kawai matsalan Mommy ne daga shi ba komai. Ko kuna ganin halin da muke ciki ni da ita for years bai kai ya maidani haka ba?” Ya k’arashe maganar yana kafeshi da kyawawan idanuwanshi da har yanzu basu gama dawowa dai dai ba. Ajiyar zuciya Arshaad ya sauk’e dan ya fahimci Aslam bai shirya fad’a mishi matsalarshi ba tunda yayi haka kuma ya san ko ya tilasta ba sani zai yi ba….. Yana cikin wannan tunanin Aaima ta sauk’o, ta shirya tsaf cikin abaya blue black tayi rolling, tayi masifar yin kyau. A hankali ta k’araso inda suke tace “Ya Arshaad muje” Tana gama fad’in haka ta juya zata wuce Aslam ya rik’o hannunta. Sai da ta turo baki tukun ta juyo ta kalleshi. Bata san lokacin da murmushi ya sub’uce mata ba ganin ya kama kunnenshi d’aya da hannu d’aya yayi kalar tausayi. Zare hannun nata tayi da ke a cikin nashi kafin ta zauna tukunna tace “Allah ya Aslam gani nayi gaba d’aya kamar haushina kake ji, tunda fa ka d’auko ni kake ta wani hantara ta, kamar irin ka tsaneni d’innan. Ni Ina chan a skul ba ni da labarin da ya wuce naku amman na dawo duk baku ma yi murna da ganina ba.” Murmushi kawai Aslam d’in yayi kafin yace “Sorry Auta. Mun yi murna sosai. We good?” Murmushi ta d’anyi itama sannan ta d’aga mishi kai alamar ‘eh’. D’an guntun smiling Arshaad yayi tukun yace “Aaima mun samu newest member a family d’innan! Daughter d’in Abba. Na san kin san labarin Anty Maryam ko? To tanada y’a Hudan!” Cikin murmushi ya k’ara da cewa “Hudan dai da kika sani” Cikin zaro ido Aaima tace “Ma shaa Allah! Haba no wonder! Dama ba nayi ta ce maka tana kama da Abba da Ya Aslam ba kwanaki kace min a’a idonane kawai.” Ta fad’a haka da tsantsar farin ciki kwance akan kyakkyawar fuskarta. Kafin ta tashi ta fara juyi da d’n tsalle tana cewa “Alhamdulillah nima nayi y’ar uwa! Yanzu Gramma sai ta daina yi min tsiya ta daina cemin k’anwar maza yayar maza.. Tana Ina (Hudan)?” Sai kuma ta d’anyi jim! Tayi shiru daga baya ta zauna tukunna tace “Mai yasa Abba bai fad’a ba? Tun farko?” Ajiyar zuciya Arshaad ya sauk’e kafin yace “Anan za kiji dalilin da yasa baki ga Mammy a gidan nan ba!” ….Tiryan tiryan haka ya zayyano mata abunda ya faru tun daga farko har k’arshe!… Sharkaf haka fuskar Aaima ta jik’e da hawaye kafin ya k’arasa bata labarin. Yana yin shiru tace “Mammy tana cell? Yaya ka san inane cell kuwa?. Ina Hudan take? Ashe shiyasa na daina ganinta a wasapp rannan har kiran ta nayi tak’i d’auka, munafuka!!!” Cikin b’acin rai Arshaad yace “Watch your words, Aaima! Ni na hanata ta fad’a miki komai, ita kuma tace ba zata iya chattn dake ba tana yi miki b’oye b’oye, shiyasa na d’auki wayoyinsu ita da Sakina nayi blocking d’inki ba tare da su kansu sun sani ba! Na fi so sai mun had’u ido da ido tukunna in yi miki bayanin komai da kaina saboda na san haka ce zata faru! Ku mata k’aramar kwakwalwa gareku ba zaki duba circumstances da situations ba kawai wanda yake naki shi za kiyi sopporting! Yanzu ki nutsu tukun mu yi magana…” Mik’ewa Aaima tayi taje gabanshi ta tsaya idanuwanta na tsiyayar da ruwan hawaye ba k’akk’autawa wani nabin wani tace “Kenan kai supporting Hudan kake ko Yaya? Over Mammy, Yaya Mammy fa!!!” Ta k’arashe maganar cikin tsawa. Mikewa shima Arshaad yayi cikin fad’a yace “Bana sopporting kowa! In fact case d’innan ba a hannuna yake ba kuma ba a hannun Abba ko ita Hudan yake ba! A hannun Granpa yake dan haka in kinga zaki iya kina iya zuwa kiyi mishi wannan haukar..” Yana gama fad’an hakan ya juya ya fice fuuuu kamar zai tashi sama. A hankali ta durk’ushe a wajen ta na wani irin kuka mai chin rai. A hankali Aslam ya mik’e ya k’arasa inda take ya d’ago ta ya zaunar a kan kujera kafin shima ya zauna, ya fara lallashinta… Cikin kuka tace , “Ya aslam Hudan is bad news! Kaga fa daga zuwanta gidannan abunda ya faru.. Na tsaneta wallahi” “Shhhhh” Aslam yace, yana sauk’e ajiyar zuciya kafin yace “She’s his fiance, dole in kin fara jin haushinta tun yanzu zai yi fushi dake And Aaima zai fi miki sauk’i idan kika rungumi Hudan kuka zauna lafiya dan she’s family kuma gashi za ta sake zama family.” Cikin rashin fahimta tace “Noo Ya Aslam, kalla fa ka gani bata riga ta zama fiancé d’intasa ba amma ji yanda yake yi a kanta, what if ta zama?”. Murmushi yayi kafin yace “Saura sati uku bikin.” Da sauri Aaima ta kalle shi sai kuma ta fashe da kuka tana cewa “Kaga irin abunda rashin Mammy a kusa kan jawo ko? Ni Ina ma na san da wani engagement balle maganar aure! Kana gani fa Ya Aslam muna waya muna chattn kusan kullum amman no one even bothers to tell me…da ga zuwan Yarinya ta hargitsa gida yanzu tana shirin hargitsa zumunci sannan a haka kace ba
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96