Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 15

Chapter 15

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

shi da Hudan yake k’ok’arin toshe duk wata hanyar da zata kawo musu matsala, yanzu haka ya ware millions zai siya musu gida, ta yadda In su Mammy sun zo ba zasu samu abun kushewa ba balle har Granpa yaji ya hana, su Abba kuwa ya san su zasu zo nema mishi aure, so gidan uncle Muhammad ba zai zama matsala ba! Dan anan aka shirya za a had’u dan ba daban jiran Dad d’in da suka tsaya yi ba ma to da tuni sun zo an gama magana. Har ga Allah ba zai tab’a iya rayuwa babu Hudan ba, kwata kwata, shi baya jin ma a tarihi akwai wani mahaluk’in da ya tab’a yiwa wata kalar son da yake yiwa Huda since day 1, gashi kuma yau Mahaifiyarta da kanta ta kalle shi tace ‘zata rabashi da ita!’ Bai ankaraba kawai yaji hawaye yana wanke mishi fuska! Sunayen Allah ya fara ambata yanayi yana kuka, kamar k’aramin Yaro. Da kyar ya samu zuciyar data yunk’ura mishi ta d’an lafa. Ganin babu Mama ba labarin ta, ya sanya kawai ya yanke shawarar komawa gida yayi wanka daga nan ya kira Ummu a san abunyi! Dan in ba ruwa ya samu ya sakarwa kanshi ba baya jin kalmar ‘A’ zata iya futowa daga bakinshi a halin da yake ciki........... BULAMA ✍️ So da Buri Free Book 37 Kamar yadda Arshaad ya tsara, sai da ya lallab’a yayi wanka da kyar tare da hutun awa d’aya! Tukunna yaji d’an dama dama, cikin tsantsar mutuwar jiki ya lalubo wayarshi ya danna kiran Ummu. Sai da ta kusan katsewa tukunna aka d’auka, a tunanin shi ko hayaniyar biki ne yasa ta jinkirin amsawa sai dai kuma tana d’auka yaji hayaniya da koke koke! Cike da fargaba ya hau tambayarta, nan take gayamishi..... ....”Suna shirin shigowa Kano, wani Abokin Junaidu ya kira Baba! Bayan sun gaisa ne yake ce mishi ‘dama ya kira ne a kan maganar Junaidu! Wai an sake shi tun satin baya da ya wuce sai dai kuma babu irin kalar binciken da basu yi ba amman an rasa shi! Wajen kwana uku kenan yau. Lokacin da aka sallameshi yayi mishi waya yace ‘zai zo gidanshi, ya d’an kimtsa tukunna ya wuce Kano, bayaso ya sanar da kowa dan surprise zai yi musu’. Yayi ta zaman jiran nashi amma shiru! Sau daga baya yaji labarin accident da aka samu a garin guda uku ata wajajen k’iri k’iri d’in! mota biyu ta y’an kasuwa ce, d’ayar kuwa ta prisoners d’in ne waenda aka saki sai dai kuma duk sun k’one k’urmus! Dan ko iya tantancesu ba a yi! Yayi shiru ya tsaya bai fad’a musu ba domin yanaso yayi bincike sosai tukunna dan shi tunanin shi yana bashi ba lalle har da Junaidun ba amman duk wani investigation yana tabbatar da akwai gawar Junaidun a ciki! Shiyasa kawai ya yanke shawarar kira ya fad’a musu..’ Gashinan yanzu haka a mutuary in babu damuwa wasu a cikinsu suzo dan ana da buk’atar su wajen tantance gawar da kuma ragowar abubuwan da ya kamata!!’.” (Da kyar Baba ya iya k’arasawa gida ya d’auki kud’ad’e da atms da abun buk’ata ya mik’a Ja’afar wajen K’asimu suka kama hanyar Lagos! Suma su Abba Madu suna ajjiyesu a gidan Baaba Talatu ya juya shi da su Ya Jamilu. Yanzu haka sun kama hanyar Lagos d’in.) “Innalillahi wa inna ilaihirrajiun” Shine abunda Arshaad yayi ta maimaitawa, yana jiwo Sadiya tana ihu tana wallahi “sai tayi sharia da y’an sanda da sojojin da suka rik’e mata Yaro bayan sun gano bashi da laifin komai! Inda ace sun bari ranar su Madu sun dawo da shi ai da duk haka ba ta faru ba! Allah ya isanta” Baba Talatu ce ta hau yi mata fad’a, tana cewa “Bata da tawakkali ne? In Allah ya riga ya tsara abu dole sai ya faru! Ta daina yi mishi kururuwa da ihu…” Amman inaaa, bata ji bata gani sai rafka kuka da kururuwar kawai take yi. Jin yadda gidan ya hautsine ne ya sanya kawai yanke shawarar zai nemo Mama da kanshi in shaa Allah, dan haka yayiwa Ummu gaisuwa, kafin ya kashe wayar. .............. Kusan a tare motar Abba da ta Aslam suka k’araso cikin estate d’in! Basu shiga ko wanne gida ba suka yi parking a babban parking lot d’in estate d’in kamar had’in baki. Abba ne ya fara fitowa kafin Aslam, yana k’arasowa inda yake yace “Ka kaita wajen Gwaggo Asabe. Zan nemaku zuwa anjima.” “Ok” Shine abinda Aslam d’in yace sannan ya juya ya fara k’ok’arin bud’e inda Huda take zaune tana kuka har yanzun, shi kuma Abba ya juya ya nufi gidan Ummi. Hannunta ya sake fincika bayan ya bud’e motar ya fito da ita!! Sannan ya zaro wayarshi ya danna kiran Gwaggo Asabe ya kara wayar a kunnenshi… Fisge hannunta tayi da duk k’arfin ta! Sannan ta juya ta bud’e motar ta d’au wayarta tana dubawa dan ita a nata tunanin ma ta fashe ne saboda yadda Aslam d’in ya had’a wayar da hannunta ya runtse a nasa hannunt tun lokacin da yace ‘Mama ba zata tafi da ita ba’ har sanda ya kaita mota…. Rad’ad’i da zugin da hannunta yake mata da kuma tsananin tashin hankalin da take a ciki ne suka hanata d’aukar wayar data fad’i daga hannunta tun shigar ta motar, sai yanzu Ajiyar zuciya ta sauk’e ganin bata yi komai ba hakan yasa ta rufe motar ta d’an juyo da niyyar kiran Mama. D’an satar kallonshi tayi, ganin ya tsareta da dara daran idanuwanshi ne ya sanya ta yin k’asa da kanta sannan tace “Ko baka ja ni ba zan bika! Wayata kawai na d’auka” Tayi maganar cikin muryar kuka. Murmushin rainin wayo yayi mata, kafin yace “Better!” Sannan ya juya ya fara tafiya yana cewa “Gwaggon ta fito, yanada bak’uwar da zai bata, ta same shi a gate!” Hudan kuwa wata zuciyar ce take ce mata ‘ta d’iba a guje ta fice a estate din!’ Amman kuma ta na juyawa tayi ido hud’u da sojoji har hud’u a wajen gate d’in suna zazzaune. Wani sabon kuka ta fashe da shi kafin ta durk’ushe a wajen abun tausayi… A hankali kuma sai ta d’ago wayar tata ta fara k’ok’arin kiran Mama tana adduar Allah yasa taga purse d’inta ta d’auka a cikin d’akin, dan lokacin da Aslam ya jawota purse d’in ta fad’i a k’asa. Aslam kuwa jin da yayi kamar ba mutun a bayan shi ne ya sanya ya juyo dai dai ita kuma da d’ago kanta sukai ido biyu! A zuciye ya taho gadan gadan yana nad’e hannun rigar shi, Ta san me yake shirin yi hakan yasa ta mik’e da sauri, kafin ya k’araso ita tayi hanyar da taga yayi….. Rashin kwarin jiki da kukan da taci ne yasa har yazo ya gota ta ya zamana ita take binshi a baya. Kamar yadda suka yi a bakin Gate d’in ya tarar da Gwaggo Asabe tana jira, nuna mata Hudan kawai yayi sannan yace “Zuwa anjima zan kiraki!” Da mamaki tab fuskarta take kallon Hudan ganin yadda yake kallonta ne ya sata kawai jan hannunta suka shige ciki shi kuma ya nufi gidan Mammy a falon ta na sama ya samu doguwar

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});