Chapter 46
Chapter 46
wanda yake sa mana ido yana gayawa wani Abokin shi wai ‘kar a had’a mu da kowa Granpa d’in yayi waya yace a ware mu.’ Inaga yana gudun kar wani ya gane mu ne. Amman fa kin san zancen duniya ba ya b’uya, wacce irin kunya kike tunanin zamu kwasa idan k’awayenmu sukaji labari?”. Ajiyar zuciya Mom ta sauk’e kafin tace “Shikenan ba damuwa, amman kinada tabbacin ba zata kwab’e mana ba ko?” D’aga mata kai kawai tayi alamar ‘eh’ Shikenan nima zan gwada yiwa Auwal magana, inaga maybe ya taimaka, dan naga kamar abun ya dameshi. In kuma yak’i, to ko sark’ata ce zance ya duba ya d’auki d’aya ya saida sai ya kawo kud’in” Cewar Mom. “Allah ya shige mana gaba”Mammy tace Daganan suka ci gaba da maganganunsu, ita kam Ummi tun d’azu bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita, ata dalilin allurar da akayi mata..... Tabbas su Ummi basu kyautaba amman a nata tunanin bai kamata ayi musu haka ba! Hukuncin yayi yawa kuma abunda akai musu d’in tabbas zai jawo mata bak’in jini a wajen y’ay’ansu ne, besides ita tama yafe musu har k’asan zuciyarta…… Tana waennan tunanin suka isa munjibir park, sun sha doguwar tafiya ba kad’an ba, ita Huda jikinta ma duk ya fara ciwo. Parking yayi duk suka fito, sai da ya gama komai ya siyaawa Sudais ice cream d’inshi, ya d’aura shi a lilo tukunna ya dawo inda take tsaye. Kallonta yayi kafin yace “Ko kema lilon kike son hawa k’atuwa dake??” Kauda kai tayi ta girgiza kai, kawai. Murmushi yayi kafin yace “Ta kwancen, itace wacce aka saki Mamanki a dalilinta! Matar Abbanki har a yanzu.” Taji zafin maganar amman ta shareshi kawai… “Wadda ta bani sak’o kuma, na san daga maganar da tayi mini kin fahimci Mahaifiyar Arshaad da Aaima ce! D’ayar kuma Mom d’ita ce! Ummi, ko dan su Sudais da kike pretending kina so, ya kamata ki tausaya mata. Mammy kuwa ko Arshaad ya kauda kai saboda son da yake yi miki, to ina tausaya miki In Aaima ta dawo dan sam ba za kiji dad’i ba at all. Mom d’ina kuwa, to be sincere ba ma wani shiri da ita, but blood is thick! And you should know me by now I’m capable of anything.. Huda! All you need to do Is talk to your stubborn father ya san abun yi… Idan ba haka ba kuma Wallahi! Ni kaina ina jin tsoron abunda zan yi miki!… A matsayin ki na so called cousin d’ina yasanya nayi deciding in baki warning first akan in aiwatar da abunda nayi niyya akanki kai tsaye. Idan kika yi min abunda nakeso to kin tsira In kuma kika yi taurin kai! To fa gaskiya i can’t save you from me. Lastly, kar ki kuskura kiyi mentioning cell d’in da kika je yau, to anyone.” Ya k’arashe maganar yana kallon cikin idonta. Da sauri tayi k’asa da kanta… Tabbas ta hango b’acin rai a cikin idanuwanshi, gashi har colour d’insu ya soma chanza wa. Bud’e baki yayi zai yi magana yaji an dafa shi ta baya. Kafin ya juya ita ta zxagayo gabanshi ta tsaya tsakaninshi da Huda. Murmushi yayi kafin yace “Har kin iso?” Yayi maganan yana mai rik’o waist d’inta ya d’an jawota jikinshi. Yadda Huda ta zabura zaka d’auka ita aka janyo.. D’an jaa da baya budurwar tayi ta d’an juyo tana kallon Hudan kafin tace “Who’s she??” Tayi masa tambayar ba tare data kalleshi ba, da d’an alamun b’acin rai a fuskarta. Murmushi yayi kafin yace “Relax! She’s just a cousin, daga k’auye tazo shine Daddy yace In kawota ta ga gari.” Ture hannunshi da yake rik’e da waist d’inta tayi, har yanzu idonta nakan Hudan wadda ita ma ta kasa d’auke idanunta akan su tana kallon ikon Allah, budurwar tace “Cousin and more, ha?” Dariya sosai yayi this time around kafin ya matso da fuskarshi dede tata tukun yace “If she’s cousin and more would I do dis in front of her?” Ya k’arashe maganan da kissing lips d’inta lightly….. Da sauri Hudan ta bar wajen tana had’a hanya. Kujerun data gani a gefe chan taje ta zauna tana haki tana istighfari. A chaan wajen su Auwal kuwa murmushin jin dad’i budurwar tayi sannan suka shiga sabgogin gabansu.......... A tap d’in wajen tayi alwala, wasu mata manya ta gani da darduma sun shinfida k’atuwa suna zazzaune ga kuloli alamun picnic suka fito, dan haka ta k’arasa tayi musu sallama tace “Dan Allah tanaso za tayi sallah” Da fara’a suka tarbeta suka matsa mata d’ayar ta fiddo hijabi a jakanta ta bata.. Bayan ta idar suka yi mata tayin abinci, gorar ruwa kawai ta d’auka ta sha tayi musu godiya a wajen ta ci gaba da zamanta a wajen, tana hango Sudais yanata wasanshi, chan gefe kuma Auwal da budurwarshi an cika musu gaba da kayan kwalama kala kala amman ita ko ruwan sha ya kasa bata… Ganin bata da abunyi yasa ta bud’e wayarta ta hau karatunta ragowar ruwan da ta sha d’an mitsitsi ta rage ta tofa a ciki.. Sai da aka fara kiraye kirayen sallar Magrib tukunna taga ya taso… Yana tasowa ta mik’e ta hau sallarta dan ta lura In suka kama hanya yanzu sai sun kusan 40min suna tafiya. Takaici, kamar ya kifa mata mari haka yaji, ba yadda ya iya shima yaje yayi alwalla yayi iya magribar d’in daya tarar maza sunyi jam’i suna yi. Tare suka jero da budurwar da Sudais da yaje ya d’auko, suka nufota. Sallama da godiya ta yiwa matan da suma suketa shirin tashi, ta rik’e hannun Sudais wanda ya iso gareta da sauri suka nufi inda suka yi parking. Sai da ya k’araso ya bud’e motar tukunna suka shiga Ita da Sudais suka zauna a baya shi da budurwar suka zauna a gaba. Sai da suka biya wani gida a lamido crescent flat mai kyau suka ajjiyeta tukunna suka wuce…Abunda ya d’aurewa Hudan kai shine shi Auwal d’inne ya bawa budurwar makullan gidan! Ita dai batayi magana ba, ta yi shiru kawai tana mamakin shi.. Ko da yace wani ya koma gaba, Sudais ta matsawa ya tsallaka. A gajiye suka isa gida yana ajjiye su yayi reverse ya sake fita. A parlourn ta tarar da Arshaad wanda suna dawowa daga kai Amarya ya had’u da Aslam cikin hira yake gaya mishi ‘Hudan sun fita munjibir da Auwal!’ Ko wanka kasa yi yayi ya taho gidan… Yana tunanin bin bayan su kenan suka shigo. Ajiyar zuciyar daya sauk’e lokacin da suka shigo sai da taji, sarai ta lura dashi amman ta d’auke kai tayi wucewarta….ganin yadda ta bawa iska ajiyarshi kuwa hakan yayi mugun bak’anta mishi rai! At least in tana jin haushinshi ai ko darajar kallo yaci ace ya samu. Sai da ta raka Sudais d’akin shi tukunna ta nufi side d’inta. Tana shiga parlourn ta saki jakarta ta tafi da gudu tana ihun murna. Rungume juna sukayi suna dariya kafin tace “tun yaushe kika zo?” Dariya itama Sakina tayi tace “D’azu Abbas yaje da kanshi ya d’auko ni hala ke kikayi mishi kwatance ko?” “Eh” tace tana sake hugging d’inta, sannan ta jata suka nufi bedroom. “Ma shaa Allah, Ubangiji mai zamani” Sakina tace. Sannan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96