Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 82

Chapter 82

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Da sauri Mammy tace “Wallahi Hajiya Hudan ba k’aramin alhaki bace ba! Ki dubafa ki ga tun daga ranar data shigo estate d’innan nake cikin tashin hankali..” Cikin d’an b’acin rai Maman nata tace “To yanzu ya za ki yi? Kinga fa wannan abun da muka san za kiyi wallahi shiyasa muka k’i mu fad’a miki maganar auren tun kina cell! Ki tsaya ki danne zuciyarki yanda kika saba, ki fara gano matsalar da ta shiga tsakaninki da Mijinki a samu a gyara a shawo kanshi in yaso daga baya sai kiyi yadda kikeso Amman yanzu idan kikayi yunk’urin hana auren nan, wallahi kowa bak’in ki zai gani, kuma hatta Arshaad d’in dakike ta haukar ‘kar Hudan ta janye miki shi’ Ke ce da kanki gashi kike k’ok’arin kawo matsala a tsakaninku da kanki gashi kina turashi away from you dan Wallahi kinji na rantse miki yadda Arshaad ya kwallafa rai akan Yarinyar nan muddin kika sake kika zama silar da ya rasata to kuwa ba zai tab’a yafe miki ba! Kuma sai kin yi dana sani. Ki bari ayi auren sai mu san abunyi. Yanzu kar ki fito b’aro b’aro a matsayin wadda ta hanashi aurent....” Cikin katseta Mammy tace “Ki kwantar da hankalinki ni na san ta inda zan b’ullo mishi yana jin maganata ai yana yi min biyayya. Matsalar da za a samu shine In har na bari ya aureta! D’azu fa muka gama waya da Adama wai ashe ma k’asar za su bari gaba d’aya! Haba dan Allah taya ba zan yi kuka ba? D’ana kwalli d’aya a duniya zata d’auke shi su tafi sai ta gama mallakeshi tukun a dawo min da fanko? Dama yanzun ma ya aka k’are?? Ballantana kuma yaje yayi spending years da ita! Ni kawai ku kyaleni dan girman Allah, dan na tabbatar ranar da Arshaad ya aureta to ni kuma zan iya barin duniyar nan a ranar.” Ta k’arashe tana sake fashewa da wani sabon kuka. Cikin fad’a Maman nata tace “Baki rabu da su Adaman nan ba har yanzu ko? Na ce miki ki tsaya ku fara shiryawa da Mijinki ki fara gano matsalar da ta shig..........” Da sauri Mammy tace “Matsalata da Dad, Aisha ce! Na rigada na sani. Ki bari kawai in fara kashe wannan boss d’in after that idan na tashi bi ta kan Aisha wallahi duk wanda ya ce zai shiga tsakani sai na had’a da shi”. BULAMA ✍️ So da Buri Free Book 52 Cikin fad’a Maman nata tace “Baki rabu da su Adaman nan ba har yanzu ko? Na ce miki ki tsaya ku fara shiryawa da Mijinki ki fara gano matsalar da ta shig..........” Da sauri Mammy tace “Matsalata da Dad, Aisha ce! Na rigada na sani. Ki bari kawai in fara kashe wannan boss d’in after that idan na tashi bi ta kan Aisha wallahi duk wanda ya ce zai shiga tsakani sai na had’a da shi”. Tana gama fad’in haka ta juya ta fice da sauri tana share hawayenta. Ko bi ta kan y’an parlourn bata yi ba, ta wuce sama abunta tana huci. Tana fita Maman nata ta sauk’e ajiyar zuciya! A hankali ta kalli Hajiya Binta tace “Allah ya rufa asiri..tunda tak’i jin maganata ni uwarta! Ni zan tafi yanzu, idan ta yarda aje wajen event d’in su Amaryar to ku rakashi Idan kuma ta hana sai ku zuba mata ido. Sannan ki samu y’an uwanki ki jasu gefe kice nace ‘ko me zata yi kar wanda yayi yunk’urin hanata’ Ita ta sani. Taje tayi yadda taga ya dace.” Tana gama fad’in haka itama tayi hanyar waje cikin y’ar tafiyar su ta tsoffi... Sallama ta yiwa matan dake babban parlourn daga nan ta wuce abunta. Har k’ofar mota ragowar sister’s d’in Mammy guda biyu k’annenta suka rakata, suka bud’e mata gidan baya ta shiga suka rufe driver yaja suka tafi. Su duk basu san wainar da ake toyawa ba Hajiya Binta wadda ta kasa fitowa parlourn tun tafiyar Mahaifiyar tasu ce kawai ta sani dan haka suna komawa aka shiga bidiri ana ciye ciye ana ta hotuna! Fitowar Ango da Aaima ne ya k’arawa abun armashi, ba a dad’e ba Mom da Ummi wadda ta d’an ji sauk’i suka shigo, nan suka had’u aka yi ta hotuna…. After kamar 30 minutes haka, aka fara shirye shiryen tafiya gidan su Amarya, anata had’a gifts.. Dai dai nan Mammy ta sauk’o. Sai da gaban Arshaad ya yanke ya fad’i amman ya dake ya k’arasa inda take ya fara k’ok’arin jan hannunta yana cewa “ta zo su yi hoto” Ko alamar zata motsa bata yi ba dan haka ya tsaya ya d’an kalleta yace “Mammy dan Allah mana, mutane suna kallo fa, ki zo muje” Ya fad’a yana sake k’ok’arin janta. Suna a haka sisters d’inta da Aaima suka iso wajen. Fisgewa tayi da mugun k’arfi, kafin tace masa “Idan baka je ka cire wannan wata kalar shigar ba wallahi Arshaad sai na ci ubanka!! Sannan ni za ka mayar y’ar iska mai magana biyu? Mu gama magana da kai amma ka je ka wani shirya tsaf sannan dan tsabar raini kazo kana ce min wani muje muyi hoto? Da kai da hoton kun ci kutumar ubanku!” Runtse idanunsa yayi da mugun k’arfi! Dai dai nan Mommy da Aslam waenda suka shigo yanzun suka nufo su, suka k’araso! Kusan duk sun ji furucinta. Da mamaki suke kallonta, a hankali Aslam yad’an dafa kafad’ar Arshaad d’in, dukda bai gama sanin wainar da ake toyawa ba amman yad’an fahimci wani abun, hakan ya sanya shi jin mugun tausayinsa ya rufeshi.... Da mamaki Mommy take kallon Mammy kafin tace “Lafiya kuwa? Me naji kamar kin ce?” “Amin, wa alaiki Assalam Aisha!” Mammy ta fad’a cikin tsareta da ido tana jin wani mugun tsanarta na taso mata… Murmushi Mommy tayi kafin tace “Assalam alaikom, me yake faruwa ne Arshaad?” Ta yi maganar tana me mayar da akalar tambayar tata kan Arshaad saboda tsananin mamakin Mammy da ya rufeta.. Tunda suke tare ko da wasa Mammy bata tab’a yi mata kwatankwacin irin haka ba. Arshaad Yana shirin yin magana Mom ta k’araso tace “Ya dai? Kukayi cirko cirko duk anan?” Kafin ta kalli Mommy tace “Ina ta yi miki magana Mommy, kika k’i kulani kika wuce. Ina wuni.” Dai dai nan Ummi itama ta k’araso wajen nasu. Cikin kulawa Mommy tace “Yi hak’uri Adama, hankalina ya yo kansu ne dan naga kamar ba k’alau ba.” Da sauri Mammy tace “K’alau d’in....” Cikin katseta da d’an k’arfi Mom tace “Haba k’alau ne mana, komai normal Ina?” Ta fad’i hakan tana kallon Mammy da d’an sign d’in tayi calming down mana… Tsaf Mammy ta fahimceta.. Itafa ta rasa gane dalilin da yasa su Adama da y’an uwanta suke tunanin zata iya yin wata kissa a wannan stage d’in! Taya ma zata iya danne wannan duka dubu d’in da akai mata? Ya an dake ta kuma suna so su hana ta kuka??… Mom na shirin yin magana taji Ummi tace “Arshaad akwai matsala ne? Yi magana mana, kar lokaci ya k’ure! Kaga yanzu tafiya za mu yi.” Da sauri Mommy tace “Dankuwa har na cewa Maryam d’in ma mun kusan fitowa, na san mu suke jira yanzu haka.” Ajiyar

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});