Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 80

Chapter 80

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,197 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

remind her!. Sannan ya san ta inda zai b’ullo mata ta yarda dan yaga alamun ba lalle ta yarda cikin sauk’i ba gashi babu enough time!…. Ya jima a wajen kafin ya juya ya wuce sama da niyyar d’an bata time Kafin ya sake ganinta! Yana da full hope d’in zai yi nasara bi izinillahi. Mammy na sauk’a k’asan ta fara shan mamaki.. Kulolin abinci kala kala da su drinks ake ta shigowa da su! Bata ida fita daga wannan mamakin ba taga friends d’inta da sisters d’inta har da Mahaifiyarta suna ta shigowa har da ankon super d’in su da suka yi a jikinsu…. Da sauri ta k’arasa kusa da yayarta ta kamota tace “Me kenan? Wats the big idea?” Murmushi Haj Binta tayi kafin tace “Wunin d’an mu za muyi mana! Anjima kad’an kuma muje muga Amarya naji Dad yace za suyi traditional day d’insu suma daga nan mu bata kyaututtuka Naga ke baki son zancen shiyasa ma na zagayeki na kira Dad. Anko kuwa ni na fitar kuma gashi kowa yayi, ni da su Hajiya ( Mahaifiyar su) tun lokacin da aka sa rana dama muke ta shirye shiryen mu. Matsowa Mahaifiyar tasu tayi kusa da su ( ita da sister d’in tata ) kafin itama ta fara magana “Ki nutsu ki bari ayi komai a gama daga nan sai a san abun yi! Ni na hanasu su fad’a miki komai akan lamarin auren, gudun samun matsala dan na san halinki. In dai ni na haifeki to inaso ki kwantar da hankalinki kiyi hak’uri, ni kaina ba wai son had’in nake yi ba! Amman ki bar ni da su kawai ai in sun san wata basu san wata ba! Kuma kar ki bari kowa ya fahimci halin da ake ciki, ki nuna kina so inda hali ma ki shirya muje ki bawa ita Yarinyar kyauta da hannunki a gaban kowa…” Ganin friends d’in Mammyn sun tunkarosu ne yasa Mahaifiyar tata yin shiru ta fara yak’e.. Suna zuwa kuwa suka hau tayata murna kowa na farin ciki tare da yi mata ya jiki (dan ce musu aka yi ita da su Mom duk sun yi inhealing dangerous abu shine aka fitar da su k’asar waje suka yi jinya sai jiya suka dawo). Haka nan suka k’arasa tsakar falon aka zazzauna… Masu decoration suka shigo suka hau d’an gyaggyara parlourn Yayar tata ce tace “bara taje ta ajjiye abu daga nan ta cewa Arshaad ya shirya, su d’anyi hotuna a nan kafin a tafi event d’in su Hudan..” Sama ta nufa da niyyar ajjiye abu tukun ta je ta kira Arshaad d’in Tana shirin hawa suka had’u da Dad yana sauk’owa… Cikin mutunta juna da barkwanci suka gaisa daga nan yace mata “Ta kirawo masa Mammy, su sameshi su biyu a side d’in Arshaad.” Mammy na zaune a cikin friends da y’an uwanta amman kwata kwata hankalinta baya a garesu! K’ok’ari take taga ta tirsasa zuciyarta ta aminta da abinda Mamanta tace mata yanzun, amman furr ta kasa... A wannan yanayin sister d’in nata tazo ta rad’a mata sak’on Dad a kunne daga nan ta wuce ta nufi parlourn Arshaad. Da kyar Mammy ta iya mik’ewa tabi bayan ta.. Sauk’owar Arshaad kenan yaga sun nufi side d’inshi, A ranshi yace “perfect” Duk fa bai san me za suyi anan d’in ba. K’arasawa yayi ya gaggaisa da bak’in, kakarshi tana ta tsokanarshi, daga nan ya wuce shima. A parlourn suka tarar da Dad yanata faman kai kawo.. Suna shigowa ba tare da b’ata lokaci ba yace “Binta, ga y’ar uwarki nan, ki tayani tambayarta.. Akwai abunda suke b’oye min ita da Arshaad wanda ban sani ba! Na san halinta da sanabe kala kala dan haka idan akwai wani abun gara tun farko ta fito ta fad’a kar taje ta yiwa mutane shirme!..” Hajiya Binta tana shirin yin magana Mammy tayi caraf ta amshe ta fara magana “Ai kai da kanka yanzu me kace? Muna b’oye maka, ko? To kuwa ai kaga tunda muka b’oye maka d’in to bai shafeka ba kenan! Infact babu abunda ma ya shafeka na daga rayuwar ni da y’ay’ana. Da kace kana kirana i thought welcoming d’ina zaka yi” Murmushin takaici tayi kafin ta juya ga Hajiya Binta tace mata “Ko kin san tun jiya dana dawo ban ga k’eyar bawan Allah n nan a kusa da ni ba balle ya tambayeni lafiyata ko ya nake? Ai ko ni kad’ai na aikata laifin b’oye y’ar gold d’inku wallahi ban chanchanci haka daga gareka ba ko dan darajar Arshaad da Aaima!” Ta fad’i haka tana takawa inda yake, daga nan taci gaba “Sannan yanzu ka wani kwaso k’afa kazo kana wani waye waye… Kai har kana da kunyar yi min wannan maganar? Bayan abunda ka yi? To bari kaji bai shafe ka ba! Ka zuba ido zaka gani tare da kowa idan Allah ya kaimu gobe.” Tana gama fad’in haka ta juya ta nufi hanyar fita. “Idan kika taka k’afarki kika bar min parlourn nan ba tare da kin fad’a min abunda nake son ji ba to a bakin auran ki.” Ba mammy ba hatta Hajiya Binta sai da gabanta ya yanke ya fad’i. Juyowa tayi tana kallonshi da idanuwanta da suka fara chanja launi, cikin tsananin takaici tace “Namiji k’anin ajali! Ai Aisha ta dawo dole ka yi min haka. To bari kaji in gaya maka wallah ko ka sakeni babu inda zanje sai dai in kai ka fita ka bar mana gidan nan ni da y’ay’ana!” Cikin katseta yace “Rukayya kar ki yi underestimating d’ina! Dan wallahi zan yi miki abunda ko me sunana aka kira sai kin ji kin tsani wanda ya kira sunan! Baki san a ya’ya nake ganin ki ba a halin yanzu, kar ki kaini bango! Wallahi ba dan darajar Aaiima da Arshaad ba da tuni na dad’e da sauya miki rayuwa.. Bana son dogon magana dan bana jin iya zama mai tsawo a inuwa d’aya da ke! Ki fad’amin abunda nake son ji in fita.” Ya fad’i haka cikin kakkausar muryar da take baiyyana tsanannin b’acin ran da yake ciki. Haj Binta ce tace “Kayi hak’uri dan Allah, Mammy ke kuma ba a haka! Ki bari wannan matsalarku ce daga baya za ku yi settling ke da shi Yanzu ki fad’i abunda yake son ji tunda ya nuna yana da buk’atar hakan” Cikin tsananin b’acin rai Mammy tace “Ba zan fad’a ba! Wallahi ba zan fad’a ba” Sannan ta juya gareshi tace “In kana buk’atar ji Yahaya ka zo ka shak’eni sai in fad’i maka ta k’arfin tsiya!! Da kake wani maganar sauya mini rayuwa, na nawa kuma? Bayan azabtar da mu d’in da ku kayi me ye kuma kuke tunanin za ku yi kuma wanda yafi wannan??. Ba dai rashin sanin ya kamata ka d’aurawa kanka ba, rana d’aya? To wallahi dede nake da k’ugunka! Maganace nace ba zan fad’a ba In kuma ka matsu to kazo ka shak’eni In fad’eta.” Cikin tsannnin fushi ya tunkarota kamar wanda zai rufe ta da duka! Dasauri Arshaad wanda shigowar shi kenan yanzun ya shiga gaban Mammy ya tsaya Hajiya Binta kuma taci gaba ta k’ok’arin hana Dad d’in k’arasawa inda Mammyn take! Dukkannin k’arfin da Allah yayi mata tayi amfani dashi

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});