Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 49

Chapter 49

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

dan na sanki da taurin kai! Kar kije an kashe case but still kina zarginshi so just ki barshi su zo d’in.” A hankali tace “komai ya wuce, ki cire hijabin please haba mana”!Ta k’arashe maganar kamar zatayi kuka. Sai yanzu Sakina tayi murmushi kafin tace “Shikenan na faasa tafiya amman ki barsu kawai suzo d’in ayi a gama” D’aga mata kai Hudan tayi. A hankali Sakina ta koma ta zauna akan gado, bayan ta cire hijabin. Da kad’an kad’an Hudan ta dinga janta da hira har ta samu ta sake ta daina fushin.. Nan take bata labarin Ya Junaidu, amman the good news is that DNA d’in su Baba bai yi matching da gawarwakin ba Both wanda akayi a Lagos da wanda suka taho da sample d’in nan Kano aka yi. Hawaye Hudan ta share kafin tace Yanzu Ya Junaidu ya b’ata kenan?” A hankali Sakina tace “Mu yita addua kawai Allah ya baiyyana shi” “Ameen” tace. Ba abunyi dan haka daga kallo sai chatting da hira.. Yau su biyu tol suka yi lunch, su Shuraim suna school Abba kuma ya d’an fita wasu ayyuka, Arshaad bai lek’o ba Aslam ma haka. Sai bayan Magrib Arshaad ya kira Sakina yace mata “suna k’asa shi da Jalila, su sauk’o!”. Jalila tunda take bata tab’a jin farin ciki irin wannan ba!……. D’azun tana d’aki Gwaggo Asabe tazo tace mata “taje, inji Arshaad, yana kiran ta.” Kasa b’oye farin cikin ta tayi a gaban Gwaggwo Asaben har da su fesa turare da shafa jambaki, daman already idanunta da kwalli fuskarta kuma da powder! Ita dai Gwaggo Asabe tsayawa tayi tana kallon ikon Allah, Allah yasa dai ba wannan Yarinyar Arshaad zai kwaso musu ba, ita tunda tazo gidan gaisuwa bata tab’a had’asu ba, gashi bata son aiki, hatta d’akin da take ciki sai dai tazo ta kira aje a gyara mata. Doguwar riga y’ar kanti mai kyau ce a jikinta, dan haka ta d’auko d’an k’aramin mayafi tayi d’auri sannan ta d’auko wani ta yafa shima d’an mitsitsi daga nan ta d’au wayarta tazo ta wuce ta fita ta bar Gwaggo Asabe da baki a sake. Nannauyar ajiyar zuciya ta sauk’e, kafin ta lek’a da d’an k’arfi tace mata “yana chaan waje a bakin mota” Don har tayi nisa. “Ok” Kawai Jalila tace tayi gaba abunta. A bakin motarshi ta ganshi a tsaye. Bai yi wani kwalliya ba hasalima Jallabiya ce a jikinshi bak’a amman sai da numfashin Jalila ya kusan d’aukewa dan yayi mugun tafiya da imaninta! A k’asan ranta tace “Ma shaa Allah” Tanajin tsananin tsantsar k’aunarsa tana sake ratsa dukkannin ilahirin jikinta, itafa ko da ace Arshaad zai dinga yi mata dukan tsiya kullum! Muddin zai yarda ya aure ta su zama k’ark’ashin inuwa d’aya, ta na amsa sunan matarshi to wallahi zata iya zama da shi!. Tsabar kallon da take yi mishi har tuntub’e tayi ta kusan fad’uwa wanda hakan ne ya janyo hankalinshi gareta dan shi bai ma san ta fito ba!. Suna had’a ido ya tamke fuskar shi kamar bai tab’a dariya ba. A take taji gabanta ya fad’i amma sai ta dake ta k’arasa inda yake still tanata satan kallonshi…. Sai da ta d’an risssina tukunna tace mishi “Ina wuni” cikin wani kalan yauk’i da kissa. Sake had’e rai yayi, ya bud’e mata murfin motar tukun yace “lafiya, shiga mu je!” A take tsoro ya rufeta, D’an bata san mai ya shirya mata ba Tana shiga, ya rufe ya zagayo ya zauna mazaunin drivern. Sai da taji tashin motar tukun ta bud’e idanunta dan tun lokacin da ya rufe mata motar ta wani lumshe ido tana murmushi saboda ba k’aramin dad’i taji ba. D’an juyowa tayi ta kalleshi fuskar shi yanda kasan wanda bai tab’a dariya ba! A hankali ta zaro wayarta ta turawa Auwal message saboda gaskiya in dai daga ita sai Arshaad ne a waje tou za a iya samun matsala dan tabbas tsaf! Zata Fallasa komai kuma ta san Auwal uban ta zai ci idan tayi hakan. Suna parking a cikin gidan dai dai message d’in Auwal ya shigo wayarta… Sai da su Hudan suka sauk’o tukun ta fahimci inda suka zo dan haka tayi mishi reply ta ajjiye wayar. Tunda ta sauk’o take maka mata harara!! A kujerun tsakiyar parlourn suke dan haka suma suka nufi wajen suka zauna. A hankali suka gaidashi ya amsa Sannan Huda ta kalli Jalilan tace “Ya Jalila ina wuni” Wani uban tsaki Sakina taja ta d’auke kai. “Hmm” Kawai Jalilan tace, wallahi ba don Arshaad yana wajen ba da sai ta tashi ta bugewa Sakina baki, dama a k’ule take dan ita kad’ai ta san tashin hankalin data shiga tun saukowarsu….. Ajiyar zuciya ta sauk’e kafin ta kalli Hudan tace “lafiya” Kawai! Amman a k’asan zuciyarta ji take yi kamar ta mutu dan tsananin bak’in ciki! Wani irin tuk’uk’i ne yake taso mata saboda abunda idanunta suka yanzu nan ne gidan Mahaifin Huda?? Ba abunda yafi d’aga mata hankali daman tuntuni irin labarin da taji Gwaggo Asabe tanayi da wata mai aiki dattijuwa akan ‘Mahaifin nata ya bar gidan saboda Babansa yace ya zab’a ko shi ko ita!!’ Ita a tunaninta bashi da wani kud’i sosai dan tama d’auka gidan haya suka je suka kama suna zaune Ashe shima mugun mai kud’i ne. Ta tabbata Hudan y’ar masu kud’i ce kenan yanzu? Kuma Babanta yana matuk’ar sonta! Muryan Arshaad ce ta katse mata tunani jin yana cewa “Jalila ga Al Qurani, izu sittin.” yayi maganar yana nuna mata kan center table kafin yaci gaba “Idan baki da alwalla kije kiyi kizo yanzu! Zan rantse akan ‘cikin jikinki ba nawa bane ba! Sharri kika yi mini’ kema kuma zaki rantse akan ‘gaskiya kike fad’a (cikin nawa ne). Tsakanin ni da ke duk wanda yayi karya Al Qur’ani ya ci shi!.” Wata zazzafar zufa ce ta keto mata, tana shirin yin magana taji ance “Sannu Ya Sheik! Akaramakallahu.” Suka ji muryarshi yana takowa cikin parlour… Cikin gadara Auwal ya k’araso wajen, kafin one by one ya kalle su! Da kyar ya iya janye idanuwanshi daga kan Sakina! Sannan ya d’anyi murmushi yace “Ai ya kamata ni ma a gaiyyaceni meeting d’in ko?” Ya fad’i hakan yana mai neman kujera ya zauna kafin yace “Ya sheikh!! You were saying??” Banza Arshaad yayi da shi ya tashi ya matsa yana k’ok’arin d’aukar Qur’ani n Hudan tasa hannu ta d’auka a hankali tayi k’asa da kanta ta fara magana “Ya Arshaad dan Allah kayi hak’uri akan abunda nayi maka, na yarda da kai please ba sai ka rantse ba!” Wani farin ciki ne ya lullub’e Arshaad da Sakina a take. A hankali shima, yace “Thanks for trusting me Hudan, but i’ve to do this, please don’t stop me, okay?” Cikin katseshi tace “Nima please kar kayi haka, wallahi i trust you, in kuma kak’i yarda har kayi, to it means stilll baka hak’ura ba kenan da abunda nayi maka.” This time around murmushi yayi, kafin yace “Tou kawo, bani” Yayi maganan yana mik’a mata hannunshi Tana shirin yin magana, suka ji Auwal ya kwashe da dariya, cikin dariyar yace , “Yayi Romeo and Juliet!! Hey, look here” Yayi maganan referring to Hudan, kafin yace “Ki yarda da shi ko kar

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});