Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 12

Chapter 12

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

bata yin kalar bugun da take yi a yanzu…. A hankali ta runtse idanunta ta sake yin k’asa da kanta jin takunshi a daf bayanta!Sannan bugun zuciya da k’amshin da yake shak’a na k’ara yawa…. Kamar yadda Arshaad yayi shima hakan ya gaida su Dad waenda suke ata gefe kad’an kusan hanyar shigowa sai dai shi bai k’arasa inda suke ba, hasalima zagayowa yayi ya zo kan kujerar da Gwaggo Asabe take ya zauna.. Kasancewar Gwaggo Asabe a 3 seater take zaune Hudan kuma a 1, sai ya zamana kamar suna facing juna shi da Hudan! A hankali ya d’ago idanuwanshi ya sauk’e su a kanta, da tayi k’asa da kai wanda ita kanta ta kasa tantance dalilinta na yin hakan Magana Gwaggo Asabe take yi mishi amman kamar ma baya jin ta, ganin hakan yasa ta d’an tab’a shi kad’an.. Lumshe idanunsa kawai yayi kafin ya bud’e su ya sauk’e a kan Gwaggo Asabe, d’an murmushi kad’an yayi mata kafin yace “barka da gida”. Cike da tausayawa Gwaggo Asaben take kallonshi, ko ba a fad’a mata ba ta san tun d’azu da ya fito daga d’akin Mommy yake cikin tashin hankali!! Dan gashi idanuwanshi sunyi jaaa sosai bakinshi yayi pink shima hatta kan hancinshi yayi jaaa Amman kuma ko ba a fad’a mata ba ta san ba kuka yayi ba wanda wani lokacin har addua take yi Allah ya bawa hawaye ikon fitowa daga idanun Aslam ko ya samu ya rage rad’ad’in da zuciyarshi take ciki. Hannunta ta d’aura akan lallausan gashin kanshi ta d’an shafa… Hakan ya sanya shi sake maida hankalinshi a kanta! Tana shirin yin magana Dad ya fara yiwa Aslam bayanin abunda ya tarasu anan bayan ya zagayo ya zauna, Abba ma ya zauna. Ajiyar zuciya Aslam ya sauk’e bayan ya gama sauraron Dad wanda ya k’arashe maganar shi da cewa “Zamu fara yanzu saboda mu samu mu gama akan lokaci kafin a gama Parking su Abba su tafi” A hankali ya juya ya kalli Abba kafin yace “Abba ka bari I’ll speak with Granpa, dan Allah don’t leave.” Murmushi Abba yayi ya mik’e daga kan kujerar da ya zauna ya k’araso inda yake kafin ya dafa kanshi tukun yace “Karka damu Aslam, ai bamu da nisa anytime kakeso zaka iya visiting, ni kaina i need some time with my daughter, wanda in muna nan na san Granpa ba zai barni ba, and ya dinga k’untata mata kenan, ni kuma from this time forward inaso In bata cikakken kulawa da happiness d’in da ban bata ba a baya, so we need some space from him, Daddy kuma he wants to leave ne saboda yaci ace Granpa ya fara rage abubuwan da yake yi. In bamu tashi mun tsaya munyi mishi haka ba, al amarin family d’innan ba zai tab’a daidaituwa ba! I hope u understand” Yayi maganan yana shafa kanshi, a hankali Aslam ya sauk’e ajiyar zuciya a karo na ba adadi sannan ya d’auke idanuwanshi daga kan Abba wanda tunda ya fara magana ya kafe shi dasu, a hankali yace “shikenan” sannan ya mik’e ya wuce zuwa inda ya fito yana cewa “zan fara daga Fatiha zuwa Nisa’i ayat 147! Someone should continue from were i stop.” Yana gama fad’in haka ya shige ya jawo k’ofar shi ya zuge. Dad ne yace “Abba ko zaku tafi tare, kasan yadda kuka saba da shi, and ga incidence d’in daya faru d’azu kar abun yai mishi yawa” “Ba zai yarda ba but let me try” Inji Abba, ya mik’e yana k’ok’arin shiga side d’in Aslam d’in. Dad ne yace mishi ya tsaya tukunna… Sai da suka tsara yadda za suyi, su mazan za suyi arba’in d’in sama, Huda kuma da Gwaggo Asabe za suyi ashirin d’in k’asa, kowa ya d’auka izu goma goma… Tukunna Abba ya nufi side d’in Aslam. Kamar yadda yace d’in kuwa sam Aslam k’in yarda yayi ya bishi hakan yasa ya hak’ura, ya zauna a d’akin yana d’an kwantar mishi da hankali, daga nan suka hau karatu a tare suka kammala nasu, dede ana kiran sallar azahar… A chan parlour ma Huda da Gwoggwo Asabe kusan tare suka kammala, Dad ne ma da Arshaad suka d’anyi delay don suna hawa sama Mommy taci gaba da kuka da kyar suka lallab’ata tukunna suka samu suka yi nasu. Sunyi addua sosai, kafin su samu ruwan zamzam aka tofa mata aka bata tasha aka shafa mata…. K’arfe hud’u dai dai komai ya kammala, duk sun shirya kaya kuma an gama jidesu, sai y’an tsirrai da za suna kwasa a hankali a hankali, waenda ba wani important bane!. Abba Dad da Daddy ne suka nufi wajen Granpa don yi mishi sallama.. Har sun kama hanya Daddy ya juyo ya cewa Arshaad “yaje ya samu Auwal yace masa ya kawo wannan Yarinyar nan sannan ya tabbatar komai d’inshi ya zama ready dan suna fitowa za a tafi” Da to ya amsa har ya juya ya nufi k’ofa ya jiyo wadda ta biyo shi da d’an sauri tana ki ranshi a hankali ya juyo yana kallonta Sai da ta k’araso ta d’anyi k’asa da kanta tana wasa da y’an yatsun ta tukun tace “Ina wuni.. Dan Allah ka ara mini wayarka zan kira Mama”. B’ata rai yayi kafin yace “Nima ba zan kulaki yanzu ba” Yana d’an turo baki kamar wani k’aramin Yaro. Dariya ma ya bata dan haka ta d’ab yi y’ar dariya mai k’aramin sauti kafin tace “To kayi hak’uri naga su Abba ne shiyasa kuma ka d’an yi nisa ne, da kana kusa da sai mu gaisa” Murmushi kawai yayi ya mik’a mata wayar sannan yace “bara yaje ya duba Auwal kar suyi ta jiranshi…” Huda ba k’aramin tashin hankali ta shiga ba dajin Mama na asibiti an sake admitting d’inta har yanzu, Sakina sai k’ok’arin kwantar mata da hankali take amman taki hak’ura, barema da taji wai an mata har eco, gashi ance Maman tana bacci ba zai yiu suyi waya ba!! Kwata kwata sai ta gaza kwantar da hankalinta, dan haka kawai tabi Ummu da ‘to’ bayan tace mata tayi hak’uri ta d’an Kara jira Amman tasa a ranta yanzu zata samu ya Arshaad ya kaita emergency d’in… Tana cikin wannan tunanin bayan sun gama wayar, wayar Arshaad ta hau k’ara! Kiranshi akeyi akai akai, gashi ya fita. Ganin an jera mishi sama da 20 misscalls ne ya sanya ta yanke shawarar kai mishi wayar. A bakin gate d’in gidan ta tambayi mai gadin ko “Ina Arshaad d’in yayi?” Opposite gidan da yake kallo wanda take ya nuna mata, dan haka ta nufi gidan....... Tun lokacin da Auwal ya dawo daga wajen Mom ake kai ruwa rana da Jalila har yau da suke shirin barin gidan! Dan tace “wallahi ba zata je wajen wata Gwaggo Asabe ba, kuma ba zata koma gidansu ba! Ta gano wayo yake so yayi mata ya yakiceta, ai tunda babanshi yace baya sonta ta san in dai ta yarda suka bar gidan babu ita tou shikenan magana ta k’are” Bikin ma cewa tayi “ta fasa zuwa” gashi ta amshe kud’i, tace “sai anje sabon gida an nuna mata d’akinta ta zuba kayanta tayi settling tukunna maybe taje” Tace kuma “In ya tilasta mata a yau sai ta tona

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});