Chapter 85
Chapter 85
ya maida hankalinshi a direction d’in Ummi, ya ganta zube a k’asa. Dan haka ya mik’e a mugun firgice ransa na k’arasa dagulewa. Abba kuwa ko gezau bai yi ba Yana nan zaune a yanda yake ko motsi ma ba shi da niyyar yi. A gigice Dad ya mik’e cikin sassarfa ya k’arasa inda suke yana cewa “Subahanallah, Abba suma tayi ko me? Duba ta mana, tashi mana, ya kamar baka ga abunda ya faru ba ne?” Ya fad’i hakan yana mai durk’usawa a inda Ummin take. Cikin nuna halin ko In kula ya mik’e tsaye ya karkad’e farar jallabiyar dake jikinshi, kafin yace “At least na sakata tayi mai dalili ai yanzu ba fake ba.” Yana gama fad’in haka ya juya zai hau sama.. Da sauri Dad ya mik’e ya sa hannu ya juyo da shi, bai yi wata wata ba ya d’auke shi da wani mahaukacin mari dan tun lokacin daya durk’usa akan Ummi idanuwanshi suka sauk’a kan takardar saki biyun da Abba yayi mata. Da sauri Auwal wanda ya shigo yanzun ya k’araso inda suke yana cewa “Subahanallah, mai ya faru? Dad wace..?” Maganarsa ce ta katse sakamakon Idanunshi da suka kai kan fuskar Ummi, da sauri ya durk’usa ya hau tattab’ata yana tambayar mai ya same ta?. Cikin b’acin rai Dad yace “Maida ita yanzunnan ko ka fuskanci fushina Yakubu!” Da mamaki Abba yake kallonshi jin yana yin yanda Dad d’in yayi mishi magana da kuma yanda ya kira sunanshi haka! Wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauk’e kafin yace “I can’t Dad, I’m really sorry Wallahi baz..” Wani marin ya kuma sakar mishi kafin yace “Kar ma ka rantse! Dan ko ka rantse sai kayi azumi saboda Ummi sai ta koma d’akinta a yau wallahi! Kaji dai na rantse.” Bai ankara ba yaji hawaye yana zuba ta idanunshi.. Cikin kuka yace “Dad bana son ganin fuskar matar nan, tayi ruining komai nawa saboda selfish reason d’inta! Ba zan b’oye maka ba wallahi Ina having second thoughts akan auren Hudan da Arshaad saboda kwata kwata bana son yin nesa da y’ata because i just knew her, all because of ummi. Ka san irin azabar da Hudan ta sha a hannun Usman kuwa? All because of Ummi. Ka san yadda nake jin Maryam a cikin zuciyata? Amma ba yadda na iya dole haka inaji Ina gani ta auri wani ta rayu da shi for almost 20 years!! All because of ummi Komai fa Yaya ita ce sila! Itace silar ciwon zuciyana! Itace silar bak’in cikina! Itace silar lalacewar soyayya ta! Haba haba dan Allah.. sannan yanzu kace In maida ita? Gaskiya kayi hak’uri Yaya, ban tab’a maka gardama ba amman kam yau zan yi maka!. Wallahi ko sunanta ba na son ji kwata kwata..” Ya k’arashe maganar cikin d’acin zuciya sannan yana gama fad’in hakan ya wuce sama ya barsu shi da Auwal wanda yake ta yayyafa wa Ummin ruwa yana son yaga ta farka. Da kyar Dad ya iya juyowa ya kalli Auwal d’in, sannan yace “Kamata mu kaita asibiti, Allah yasa ba wani babban abun bane ya sameta......” Gandun albasa (2:30 pm) A tsakar gidan Madu, akayi decoration na traditional kaulu! Wajen yayi masifar yin kyau. Taken wak’e wak’en Shuwa Arab ne ke tashi in a very low tone. Su Sudais da wasu Yaran sai y’an tsofaffi tsilla tsilla ne a zazzaune a kan kujerun da aka k’awata tsakar gidan da su. Gaba d’aya y’an mata da manyan matan suna ciki, wasu suna had’a takeaway da souvenirs wasu kuma suna shiryawa dayake mostly family ne sai na jiki sosai suka zo dan Mama ba wani taro tayi ba Ita dama ba wani sanin jama a ma tayi sosai ba, sai y’an unguwa da suke ta zirya tun safe waenda rabinsu duk munafurci ne yake kawosu dan an san yau za a kawo lefe. Umma bata da lafiya tana fama da hawan jini amman tun sassafe suka zo ita da Baaba Laraba da yayarta Hansai, kuma wani abun mamaki tunda tazo d’in tak’i kula Mama dan wani mugun zafinta take ji, sun dai gaisa da Shuwa da Ummu Ita kuma Mama sun gaisa da Hansai da Baabaa Laraba amman Umma kam tama k’i bari su had’u dan tana hango ta zata kauce hanya ko ta fad’a d’aki ta shige band’aki. Da Mama ta fahimci hakan kawai sai ta tattarata ta watsar ta shiga sabgar gabanta dan ita mamaki ma Sadiyar take bata duk tabi da d’aurawa kanta wahala gaba d’aya a takure ma kamar ta ganta ga kuma rashin lafiyar Bp da take ta fama. Sai da Anty Zainab ta zo tukunna ta d’an samu ta ware. Itama Anty Zainab d’in da kyar ta iya daurewa suka gaisa da Maman wadda tayi wani irin fresh! Sannan idan ka kalleta ba zaka tab’a cewa sa’ar su bace ita da Sadiyar Sai dai kace Antys d’inta ne dan ba za ma ka ajjiyesu a matsayin yayunta ba! Musammam ma Sadiya wadda ta zama kamar wata mahaukaciya kwana biyun nan! Tun lokacin da taji labarin maganar auren Huda har yau bata san inda nutsuwarta take ba……… Mama na gama gaisawa da Anty Zainab ta juya ta wuce abunta. Anty Zainab kuma ta nufi wajen Umma! Nan kuwa suka hau hassada da zagin Mama har da suna cewa wai “bazawari take nema shiyasa taci wannan uwar kwalliyar”. Laffaya Maman ta nad’a itada Ummu, kalar laffayar ja sai blue d’in flowers, sun yi kyau sosai dan har d’an light makeup sai da Sakina ta tirsasa su suka tsaya aka yi musu. Itama Sakina laffayar ce a jikinta, amma bata nad’a ta har ka ba, instead sai tayi d’aurin Zahra Buhari da mandil a kan nata shi kuma mayafin layyafar ta nad’a a kafad’ar ta. Amarya kuwa ta sha traditional kaya abunta! Hatta hair style d’inta ma irin nasu aka yi mata, daga sama ta nad’a wata had’add’iyar blue black d’in laffaya, aka yafa mata mandil akai. Tun daga kan sark’ok’in k’afarta har na wuya da y’an kunneta da wanda ta sa a kanta na sisin gold duk na asalin gold ne! Wanda Madu ya bata kyauta jiya da daddare, yace “tun na mahaifiyar mahaifinsa ne! Maryam yaso bawa Allah bai yi ba. Ashe rabon ta ne..” D’akin isu isu ne ita da k’awaye ta, anata d’aukar hotuna amman kallo d’aya za kayi mata ka san hankalinta baya ma gidan gaba d’aya! Tun da gari ya waye take jin fad’uwar gaba, gashi yanzu kuma sai kiran Arshaad take yi baya d’auka….. Shuwa ce ta shigo ita da Baabaa Talatu sanye cikin wata rantsatsiyar milk laffaya sun yi anko su biyu suma abun su ita da Baabaa Talatun. Basu dad’e ba wasu mata suka shigo su biyu, daga nan suka umarci Hudan da ‘ta mike a fita da ita’ Aranta ji take kamar ta tambayesu ‘Ya arshaad ne ya zo? Sai kuma taga rashin kunya da zak’ewarta Kuma ta tuna jiya Sakina tace mata ‘Ta bar nuna mishi ta damu sosai fa, idan ba haka ba tabar ganin wai yana sonta Wallahi wahala zata sha....’. Lumshe idanuwanta tayi ta dedeta nusuwarta sannan ta bawa Sakina wayarta ta mik’e, ta jaa mandil d’inta ta rufe kaf fuskarta, su kuma suka tik’eta sukayi waje. Suma su
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96