Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 81

Chapter 81

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

wajen ingije Arshaad d’in sannan kafin yayi nasarar tsaidata ta tafi gaban Dad ta tsaya! Tana mai jin wani tuk’uk’in bak’in ciki yana taso mata, babu abunda idan ta tuna yake k’ona mata rai irin yanda taga Daddy yana ziryar zuwa wajen Adama last zuwanshi da yayi har kusan kuka taga yayi daga nan ma yace ‘ba zai iya sake ganinta a haka ba’ Tun daga ranar kuwa idan bai kirata sau d’aya ba tou zai kira sau biyu! Amman ita ko lek’enta ko waya Dad bai tab’a yi yace a bata ba, ita tana chan tana tunanin sa ashe shi yana nan Aisha ta d’auke masa hankali! Kalli fa sarai ya san ta dawo amman ko lek’enta bai yi ba kuma suna cikin gida d’aya, sai yanzu dan rashin kunya da tsaurin ido ya buk’aci ganinta kuma ko alamar tambayarta ya take bai yi ba instead ya hau wani tsattsare ido yana hucin banza.. Waennan takaicin ne suka sanya ta kasa cewa komai kawai ta zube a wajen ta fashe da wani mugun kukan bak’in ciki. Cikin son kawar da lamarin Arshaad yace “Dad, dan Allah ka bar maganar nan, na fad’a maka ba komai fa”. Banza Dad yayi da shi kawai ya juya ya fice! Yaso ace Mammy tayi mishi wani shirmen yau wallahi da sai ya yi mata abunda bata tab’a tsammani ba! Ya san at least zai samu peace of mind at last. Yana fita Mammy ta mik’e! Tunda take a rayuwar ta bata tab’a jin kishi da takaici da tashin hankali da bak’in ciki irin na yau ba! Ta rasa dalili amma ko y’ar kissar da ta saba yiwa y’ay’an nata da Dad d’in ta kasa kuma bata jin zata iya, babu abunda take so kuma take buri irin taga ta b’atawa Dad rai ko ta samu zuciyarta ta d’anyi sanyi. Tayi imani yanzu haka wajen Aisha zai tafi yaje ya ganta yad’an samu nutsuwa hankalinshi ya d’an kwanta alhalin ita kuma gashi ya k’unsa mata bak’in cikin da bata jin zata iya mantawa da shi har abada! Taya zai yi mata haka? Taya zai banzantar da ita har haka saboda Allah kamar wata dabba? ‘Inaaa!! Ba zai yiu ba Wallahi’ Shine abunda ta fad’a ta gyara tsayuwarta tana k’ok’arin yin hanyar waje….. Da sauri Hajiya Binta ta tareta tace “Meye haka ne wai Mammy? Ba a isa a fad’a miki kiji bane? Ina za ki ji yanzun?” Cikin kukan Mammy tace “Kina ganin fa abubuwan da Yahaya yake yi mini Ya gama b’ata min rai ya fice ya tafi wajen uwar gidan shi ya bar ni ni anan zuciyata ta kama da wuta kenan ko me? Ki cikani kawai, wallahi bai isa yayi farin ciki ba, ba inda zai je yau, kullle k’ofar gidan nan zan yi sai dai mu kashe juna ni da shi a cikin gidan nan!” Da sauri Arshaad ya matso kusa da su ya rik’eta, wani tsananin takaicin sa take ji hakan yasa ta juyo da sauri ta kifa masa Mari! Sai kuma ta fashe da kuka, cikin kukan tace “Ai kaima baka kishina Arshaad, a tunanina ko Hudan y’ar gwal ce wallahi ba za ka so auren ta b. Taya za ka had’ani da ita mu zama surukai!? Ko kasan cin mutuncin nan da aka yi min shine abu mafi muni a rayuwata?. Na fad’a na k’ara fad’a yanzu ma zan maimaita maka ‘Wallahi idan ka aureta sai na tsine maka!’.” Arshaad bai san lokacin da ya tsugunna a wajen ba ya fashe da wani mugun kuka. Cikin b’acin rai da kafiya Mammy tace “Kuma ko event d’in yau da suka gaiyyaceka ban yarda ka je ba! In kaje kuma wallahi Allah ya isa ban yafe ba! Zan ga wa zaka zab’a tsakanin ni da ita.” Da sauri ya mik’e yace “Haba Mammy ya kike so inyi ne? Ki tsaya ki saurareni kuma kin k’i.. Dad ne ya nema min aurenta Abba kuma ya bani, idan nayi miki biyayya su kuma bijire musu kike so in yi?” Da sauri cikin katsesu Hajiya Binta tace “Rukayya ban tab’a tunanin baki da hankali ba sai yau wallahi! Ni, na fad’a miki! Mahaifiyarmu, itama ta fad’a miki! Amma ba za ki ji ba? Waye a cikinmu zai fad’a miki abunda zai cutar da ke? Munce kiyi hak’uri ko? Waennan irin y’an iskan aljanu masu shegan taurin kai kika kwaso a cell d’in ne wai?” In banda gunjin kuka babu abunda Mammy take yi. Cikin son su kad’aita iyaka su biyu dan ta samu damar lallashinta da fahimtar da ita Hajiya Binta ta cewa Arshaad “wuce ka tafi ka shirya ku je ku yi event d’in, idan ka dawo sai mu k’arasa” Ai kuwa Mammy na jin haka ta tafi da gudu hanyar k’ofar fita ta tsaya tayi stretching hannunwanta sideways ta kare k’ofar tace “wallahi idan ka fita sai na tsine maka!!” Da sauri Hajiya Binta tazo ta kama hannun tana k’ok’arin janyeta tana cewa “Arshaad zo ka wuce” a ranta tana aiyyanawa ‘Tabbas akwai abu a kan Mammy’ “Zo ka wuce nace kar ka bari tayi maka spoiling day d’inka!” Hajiya Binta ta sake maimaitawa ganin Arshaad d’in ya k’ame a waje d’aya abun tausayi. A hankali ya k’araso ya shiga lallab’ata, Hajiya Binta itama tana yi, amman fur!! Mammy ta yi kane kane a hanyar tana ta faman maimaita kalma d’aya ‘Idan ka fita sai na tsine maka!!’ Basu ji lokacin da akai sliding k’ofar aka shigowa ba sai dai kawai suka ga an juyo da Mammy an wanke ta da mari! Diff!! haka parlourn yayi tsit! Cikin b’acin rai Maman Mammyn tace “Yi maza kaje ga Aaima chan driver ya bata kayan da zaka saka ta kawo. Jeka ka shirya yanzun nan za muzo mu rakaka.” Har ya d’anyi gaba sai kuma ya juyo yace “Tace fa In na fita sai ta tsi..” Cikin katseshi Maman Mammyn tace “Nace ka fita ko! Ta tsine makan in gani.” A hankali yad’an kalli Mammyn yaga ta d’auke kai daga kallonshi, cikin nutsuwa yayi sliding door d’in ya bud’e ya fice, yana mai share ragowar kwallar dake kwance akan fuskarshi. Yana fita ta fashe da kuka, cikin kukan tace “Da wanne kuke so inji ne wai? Ya kuke son inyi? Wallahi ko sunan Yarinyar bana so a kira! Ji nake yi kamar zan mutu, ku duba fa kuga yanda yake kuka shab’e shab’e dan kawai nace ba zai aureta ba! Idan ya aureta kuma ya kuke tunani??” Hugging d’inta Mahaifiyar tata tayi tana d’an bubbuga bayanta… Sai da ta tabbatar tayi shiru tukun cikin sigar lallashi tace “Kiyi hak’uri Rukayya, ke fa da kanki kikace Mijinki yana share ki! Ki duba fa ko wajen ki baya zuwa kuma da kika dawo bai nemeki ba, ko ya yi miki magana bayaga yanzun?” Cikin sheshshekar kuka Mammy ta hau girgiza kai alamun ‘a’a’. Ajiyar zuciya Maman nata ta sauk’e kafin tace “Kinga ko! Wannan ma kad’ai abu ne wanda ya kamata a tsaya a duba da kyau. Yanda kikace Matar nan tasa ta warke, da kuma dalilin da ya sanya yake ta faman jin haushin ki wanda bamu san daliliba yanzu shine abun a tsaya a duba a gyara bawai wannan k’aramin alhakin ba.”

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});