Chapter 1
Chapter 1
So da Buri Free Book 36 Kamar yadda Arshaad ya fad’a, mintuna ashirin d’in bama su cika ba! Ya gama abunda zai yi… Ya sa komai a sai ti sannan ya kira Granpa da landline d’in wajen ya sanar dashi ya gama, komai yayi normal. Daga nan ya nufi hanyar office d’inshi cikin d’an sauri saboda very important magana suke yi shi da Aslam kafin Granpa ya kirashi ya sakashi aikin. Tun kafin ya k’arasa ya hango k’ofar office d’in nashi kamar a bud’e! Yana suwa kuwa ya gasgata hakan sakamokon ganinta da yayi a wangale sosai.. Da mamaki ya kutsa kai ya shige ciki… Tun bai gama shiga ba ya fahimci babu Aslam babu alamar shi a cikin office d’in. A hankali ya sanya hannu ya rufe k’ofar office d’in yana mamakin abubuwa guda biyu ‘Tafiyar da Aslam yayi bayan ya san maganar da suke yi mai mahimmanci ce!’ Da kuma ‘yadda yazo ya samu k’ofar office d’in nashi a wangale’ Could it be Aslam d’in ne ya fita a rikice? Ko kuma dai bayan ya fitan ne wani ya shigo mishi office May be Auwal? No it can’t be!!….. Duk shi kad’ai yake ta sak’e sak’en shi a cikin ranshi. Ganin babu inda waennan tunane tunanen zasu kaishi ne ya sanya kawai ya yanke shawarar ‘gara ya kira Aslam d’in! Ya ji ko lafiya’. Shafa aljihun shi yayi da niyyar d’aukar wayarshi yaji wayam Yasan daman da guda d’aya ya fito d’ayar kuma tana gida bai ma fito da ita ba! To ko dai ya jefar ne a inda ya baro… Har zai juya ya fita dan yaje ya dubo wayar sai ya hangota a kan table d’inshi a ajjiye. Ajiyar zuciya ya sauk’e kafin ya k’arasa yasa hannu ya d’auka da niyyar kiran Aslam.. Sai dai kuma bai kai ga bud’e wayar ba idanunsa suka ci karo da notification Barr dinsa wanda yake nan cike da tarin misscalls d’in Huda! A firgice yad’an zaro ido yana kallon wayar.. Whatever it is da ya sanyata ta jero mishi wanann tarin misscalls haka ya san its very serious and important!! Idanuwansa ne suka sauk’a akan message d’inta…dan haka cikin k’aguwa ya hau karantawa......... Tsayawa yayi cak!!! Kamar wanda aka dannawa pause. Dan ko numfashi kasa ja yayi.. A hankali ya lunmshe idanuwanshi… Da kyar ya samu yace “Ya subahanallah!!” Sannan ya sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya ya bud’e idanuwanshi da har sun kad’a sunyi jaaaa!. Wani abu ne yaji ya toshe mishi mak’oshi! Da kyar ya samu ya had’iye ya ja numfashi ya fesar da mugun k’arfi!. Yana nan tsaye rik’e da wayar a setin fuskarshi har yanzun ya kasa gota ta…. A hankali kamar mai jin tsoro ya shiga Call log ya danna kiran Aslam… Ya kirashi yafi sau biyar amman bai d’auka ba saboda a lokacin ba abunda yake da buri kamar ya gansu a asibiti! Ko ya samu ya daina jin kukan Huda wadda ta kasa yin shiru, sannan a samu a duba Anty Maryam a ga lafiyar ta! Shiyasa in banda gudu ba abunda yake tsulawa kamar shi kad’ai ne a akan titin Tunda ya samu suka yi waya da Abba yace mishi ‘gashi nan zuwa’. A hankali Arshaad ya zare wayar daga kunnenshi ya yi scrolling zuwa sunan Huda ya danna ya kara a kunnenshi… Sai da ta kusan katsewa tukunna ta iya d’auka tace “Hello Ya Arshaad” Kana ji ka san kuka take yi. A hankali ya sauk’e ajiyar zuciya yace “Kina ina?” Cikin kukan tace “Ga Ya Aslam d’innan ya zo, muna hanya zamu kaita akth yanzu. Na gode sosai.” Ta fad’i hakan, ita duk a tunaninta shine ya turo Aslam saboda maybe ko shi d’in yana wani abun important ne. A hankali yace “Umm! Mu had’u a chan.” Daga nan ya yanke kiran. Mukullin motarshi kawai ya d’auka ya fice a office d’in! Yana zuwa ya shiga ya kunnata ya bata wuta ya fice ya nufi asibitin..... A mota Aslam yace “ta jira” Shi ya shiga, ya fito, da nurse guda biyu da gado aka d’aura Maman a kai suka shige ciki. Sai da ya tsaya aka yi komai tukunna ya cewa “Huda tazo taje ta zauna” Sai da ya tabbatar ta zauna sannan a hankali ya d’an durk’usa ya shiga lallashinta! Da kyar ta samu ta d’an yi shiru….Yana matsawa a wajen taci gaba da kukanta a hankali tana share hawaye…. Bayan rashin lafiyar Mama har da abunda Hajiya Shuwa tayi d’azu ya daki zuciyarta ya b’ata mata rai kwarai!! Bata tab’a jin zafin kalar abubuwan da Hajiya Shuwa take yi musu kamar irin na yau ba! A hankali Aslam wanda yake ta faman k’ok’arin ganin bai sake kallon direction d’inta ba Ya d’aura idanuwanshi a kanta yana kallonta… Ji yake kamar ya sake komawa yaje ya lallasheta tayi shiru! Har ga Allah kuka yana d’aga mishi hankali. Nurse d’in data taimaka aka shigo da Maman ce tazo zata wuce ta kusa dashi Har ta d’anyi gaba sai kuma ta dawo tace masa “Kaje ka zauna ka lallashi matar taka mana! Ka barta ita kad’ai chan gefe sai faman kuka take yi. Kaje wajenta mana.” Tana gama fad’in haka ta juya ta wuce a bunta. A hankali ya lumshe idanuwanshi a ranshi yace “Why am i too nice to her, yau?” Wata zuciyar ce tace mishi “Saboda Mamanta bata da lafiya mana.” A hankali ya sauk’e ajiyar zuciya yana mai raya wa a ranshi ‘yadda yayi da yadda ya nuna tsananin damuwarshi! Tabbas kowa ya gani zai yi tunanin ita d’in matarsa ce’ A hankali ya sake lumshe idanuwanshi yace “damn it!” A chan k’asan mak’oshi!. Cikin k’ok’arin son kawar da wani tunanin na daban ya fara k’are mata kallo yana mamakin kamannin ta da Abba! Gata kuma y’ar gidan Anty Maryam! Ko shekaran jiya ma sai da ya ga hoton Anty Maryam wanda suka d’auka ita da shi da Abba da Dad da Mommy lokacin a Saudiyya! Ko da ace ma bashi da hoton ta tabbas fuskar Anty Maryam ba zata tab’a b’ace mishi ba… Sauk’e Ajiyar zuciya yayi, a k’asan ranshi yana zullumin k’arasowar Abba! Tabbas lissafinshi dai dai yake bashi! Bashi da tantama.......... Sai da ya sha d’an k’aramin yak’i! Da security d’in bakin k’ofar shiga emergency d’in tukunna da kyar!! Ya barshi ya shiga. Yana shiga hankalinshi da idanuwanshi suka kai kan Aslam wanda yake a tsaye ya k’urawa Huda wadda take zaune tanata faman kuka, ido! Da sauri ya k’arasa inda yake.. Sam Aslam bai lura da shi ba har sai da ya dafa shi, tukunnan yayi firgigit ya juyo yana kallonshi.. Maimakon yace wani abun kawai sai Arshaad yaga ya k’ura mishi ido kamar wanda yake son hango wani abu, har sai da ya d’an tsargu! Kusan 2 minutes Aslam ya d’auka yana kallon Arshaad Wanda hakan ya sanya duk wani rikicin da yake ciki hauhawa jikinshi kuma yayi sanyi lokaci guda dan bai san me ya sanya Aslam d’in yi mishi irin wannan kallon k’urillar ba!. Kamar daga sama yaji muryarshi yana cewa “Ka tab’a ganin Mahaifiyar Huda??” Da mamaki Arshaad d’in yake kallonsa kafin yace “Ba sau d’aya ba!.” Shiruu, Aslam d’in yayi sai kuma ya runtse idanunsa da k’arfi kafin ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96