Chapter 17
Chapter 17
dawowa dede ba ya sake d’auke ta da wani! Cikin tsananin b’acin rai yace “na fahimci option 1 kika d’auka!” Sannan ya juya ya nufi wardrobe da sassarfa. Da sauri Ummi wadda take ji kamar an yi mata b’arin wuta a kumatunta duka biyu ta k’arasa jikin k’ofar tana bubbugawa tana neman taimako, dan ta lura Abba baya a haiyyacinshi… Babu wanda ya jiyota, dan k’ofofin gidan gaba d’aya sound proof ne, ko bayaga haka ma yanayin girman gidan ba lalle a iya jiyota ba! Bata ankara ba taji ya janyota da dukkan k’arfin shi ya zuga mata belt…wani mahaukacin ihu tayi ta fad’a kan gado ta rarumo blanket da quilt d’in kai ta k’udundunu a ciki. Cikin zafin nama ya fincike bargunan yayi cilli da su sannan ya shak’o ta, kafin yasa dukkanin k’arfin da Allah yayi mishi ya fincikota daga kan gadon ya tsayar, still yana rik’e da wuyanta da ya yiwa muguwar shak’a! Ita ya shak’e amman yadda idonshi yayi jaaa zaka d’auka shi aka shak’e!. Cikin d’acin zuciya yace “na fasa sakinki da kaiki kotu Ummi kashe ki zan yi kowa ya huta!!” Ummi kuwa ganin Abba yana shirin kaita lahira ne ya sanya ta fara dukan hannunshi, tana tarin wahala, da y’ar ragowar muryar data ragemata tayi amfani wajen cewa “Za.z.Zan fa ff fad’a” Tana kallon kwayar idanunsa waenda take hango tsananin tashin hankali a cikinsu. Jifa yayi da ita sannan cikin b’acin rai ya juya mata baya kafin yace “Ina jinki, kuma kar kiyi kuskuren b’ata mini lokaci, dan ba zan baki wani chance d’in a karo na biyu ba.” Ajiyar zuciya kawai take ta faman sauk’ewa mai had’e da tarin wahala… Jin shiru ya sanya shi juyowa yana mata wani irin kallo. Ganin haka yasata fara magana “Ranar bayan mun ji labarin sakin da kayi mata…. Muna zaune da ni da Mom, kawai sai ga Daniel ya zo a rikice….dama duk wani abu idan ya faru ya kan fara fad’a mana kafin Granpa, in na dannewa ne mu danne ko kuma mu sakashi ya juya zancen sai mu bashi kud’i. To kamar kullum haka ranar ma yazo mana da takardar sak’on Maryam, yake cewa ‘k’anwarta ce ta kawo kuma tace dan Allah a baka tana waje tana jira’ Ba komai ne a cikin takardar ba fa ce ‘Baka hak’uri da take yi akan duk laifin da tayi maka har ya kaika ga d’auke k’afa wanda ita bata san laifin ba! Sannan tana buk’atar ka a asibiti zata haihu.’ A lokacin kusan sumewa nayi, dan ni ko had’a shimfid’a baka yi da ni amman ita Maryam gata harda ciki zata haihu! Kuma na tabbatar muddin kaji labarin cikin nan to baza ka tab’a yarda mu koma ba, sannan definitely zaka mayar da ita tunda saki d’aya ne a tsakanin ku. Rasa yadda za muyi mukai. Murnar mu gaba d’aya sai ta koma ciki...... Tun muna Yara Allah ya yiwa Adama baiwar kwafar duk wani zane da rubutu duk kuwa wahalarshi tsaf zata kwafe tayi irinshi exactly.. Ganin yadda duk na rikice ne yasa ta ce mini ‘inje In d’auko littafin ka’ Na fahimci me take shirin yi shiyasa da gudu, na fita naje d’akinka na kuwa ci sa’a baka nan hakan ya bani damar d’auko diary d’inka. Da farko da muka zo, mun tsara ne akan zamu rubuta mata ‘ta jiraka nan da 2 weeks in shaa Allah in ka gama settling da Granpa, zaka je ka sameta’ Kaga kafin nan tunda haihuwa zata yi already ta fita iddarka, ni kuma sai in san yadda zan yi in ja hankalinka mu koma, kuma mun tsara zamu tura wani yaje ya aure Maryam d’in kafin mu dawo tukunna mu saka ka fahimci kana da y’a ba tare da sunan mu ko laifin mu ya fito ba! Amman karanta diary d’inka da muka yi ne ya sake hautsina komai! Domin kuwa Abba kwata kwata baka da plan d’in yin rayuwa da ni, you promised maryam (a diary d’in) cewa nan da 1week zaka je ka maida ita, kuma ko parents d’inta sun yarda ko basu yarda ba zaka d’auketa ku sake barin k’asar! Har sai lokacin da Allah yayi Tou were willing to leave and risk everything for her, a plan na future Dinka kwata kwata babu ni a ciki!! And you wrote it ‘a dalilina ne yasa ka tafi ka bar Nigeria, har iyayenta suka kasa hak’ura, suka biyoka, shi kuma Granpa ya yanke wannan hukunci, so I have to pay the price!’ Although ban san menene price d’inba tunda baka rubutaba, but na fahimci saki ne, tunda yadda kake tsarawa..y’ay’an da zaku haifa da sunayen da zaku saka musu, da irin tarin addu’o’in ka na burin samun babys daga gareta, na fahimci baka da tsarin zama da ni! Kuma hankalina yayi matuk’ar tashi da naga kwad’ayi tare da kalar son da kake yiwa y’ay’an da zaku haifa( kai da ita), shiyasa kawai muka yanke hukuncin rubuta mata takardar da muka aika Daniel ya kaiwa k’anwarta!. A baya tunani na son Maryam kakeyi, amman karanta diary Dinka da nayi tun daga farkon had’uwar ku har k’arshe bayan tafiyar Daniel, shi ya tabbatar min da cewa haukan somta kake yi Dan haka with her in your life, Abba banida chance kwata kwata.” Matsowa tayi kusa dashi ta kama hannunshi kafin tace “Abba put yourself in my shoes, yadda kakeji akan Maryam wallahi nima haka nake ji a kanka! Shiyasa da naji plans d’inka hankalina bai ida kwanciya ba har sai da muka had’u da mammy ta rakamu aka rufe maka baki akan batun mayar da ita d’in da kace zaka yi sannan aka cire ta a ranka gaba d’aya! Sai dai kuma shekara d’aya kawai Allah ya bawa addu’o’i n namu ikon yin tasiri a kanka domin har yau zancenta kakeyi ba dare ba rana kuma na tabbatar ba dan ta yi aureba da tuni tana a gidan nan ni kuma na san karshenta zuciyata bugawa zata yi!”. Cikin kuka tayi k’asa ta durk’usa a gaban shi still tana rik’e da hannuwanshi kafin tace “Duk wani abunda kake buk’atar ji, gashi na fad’a maka, har wanda bai kamata kaji ba duk na fad’a maka Abba Amman inaso ka cire son rai ka duba lamari na, wallahi duk kai ka janyo komai! Komai kuma da nayi, na yishi ne saboda kai, saboda son da nake yi maka da kuma burin inga mun kasance tare har abada!. Dan haka, dan Allah ka dube ni da idon rahama ka yafe min, ni kuma na yi maka alk’awarin ba zan sake wani attempt d’in tab’a rayuwar Maryam ko y’ar ta ba! Tun farko ma da ace baka yi abinda kayi ba, da ba azo nan ba.. Inda ace ka bani time d’inka tun lokacin farkon aurenmu da ba zan yi attempting aika mata da sak’o ba wanda har yayi sanadiyyar da ya sanya ni karanta diary d’inka. A yadda nake sonka inda zaka dinga kula da ni, sannan ka min alk’awarin adalci da zama dani har abada, wallahi Abba da zan rufe idona In danne duk wani kishi, in barka da Maryam Amman yadda ka nuna gaba d’aya baka da plan na rayuwa dani shi......” Hannun shi da ya warce
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96