Chapter 79
Chapter 79
Ta fad’a a k’asan ranta! Bata san dalili ba amman taji zafin yanda yayi mata, taso ta koma sama kawai abunta amman sai ta tsinci kanta da kwad’ayin bin bayanshi, dan haka ta rufe k’ofar ta nufi side d’in Arshaad. Direct main bedroom d’in dake side d’in Auwal ya nufa. Yana shiga ya ganshi yashe a k’asa da jikakkun kaya. Da sauri ya k’arasa wajen ya durk’usa ya hau jijjigashi yana kiran sunanshi…. Dai dai nan Aaima ta shigo, duk da fushin da take yi dashi hakan bai hanata fashewa da kuka ba da ganin halin da yayan nata ke ciki. Da sauri Auwal ya juya gareta yace “Yi maza Aaima d’ebo ruwa a toilet yi sauri plss..” Ya fad’a cikin gigita da kid’ima. Da gudu ta nufi toilet d’in ta d’ebo ruwan ta fito ta na zuwa Auwal ya amsa ya hau yayyafa mishi…. Sai da suka fidda ran ma zai farfad’o tukunna yayi wata wawiyar ajiyar zuciya wadda ta taho mishi tare da tari! Auwal ne ya d’an d’ago shi kad’an yahau bubbuga mishi baya yana jera mishi sannu. Da kyar ya samu tarin ya tsaya ya shiga jejjera ajiyar zuciya.... Sai da Auwal ya kamashi ya kaishi kan gadonshi, tukun ya zaro waya ya fara k’ok’arin kiran family doctor d’insu…. Kamar Arshaad d’in ya san me yake shirin yi, yace nasa “Kar ka kira kowa Auwal, i’m fine. Please.” Kallonshi Auwal d’in yayi kafin shima yace “Dan Allah kar ka gwada yin wannan taurin kan! Ka bari a kirashi ya duba ka kawai.” Cikin d’an fushi Arshaad yace “Auwal zamewa nayi na fad’i na buga kaina! Yanzu kuma na farfad’o… Ka gaya min in akwai abinda Doc zai yimin idan ya zo d’in bayan wanda kukai min.” D’an k’uraa mishi ido Auwal d’in yayi kawai ya tsaya yana kallonshi. A hankali Arshaad d’in ya koma ya jinjina a jikin gadon sannan yace “sorry” Ajiyar zuciya Auwal ya sauk’e kafin yace “Are you sure that’s all?” Jinjina kai kawai Arshaad d’in yayi. Auwal bai wani gamsu da maganan shi ba but yaga kamar he wants to be alone shiyasa yace “Shikenan, Allah ya kare gaba, ka kira su Hudan hankalinsu ya tashi sosai. And dan Allah ka sauya kayan jikin nan naka, sai da safe.” “Ok” shine abunda Arshaad yace sannan ya k’ara da cewa “Thanks a lot” Murmushi yayi kawai yace mishi “Good night” Daganan ya nufi hanyar fita. Kallonshi (Arshaad) itama Aaima tayi tace “Ka kira wayana if you need anything” Jinjina mata kai kawai yayi sannan ya fara k’ok’arin mik’ewa dan chanja kayan jikinshi. Ganin haka yasa Aaiman yi mishi sai da safe itama ta juya tabi bayan Auwal wanda har ya kusan ficewa… Sai da ya kusan isa k’ofar fita ta main parlour tukun ta samu ta cin mishi ta wuce ta isa bakin k’ofar ta sa hannu ta bud’e. Ba tare da ya kalletaba dan shi har ga Allah ta fara k’ular dashi Ya sa kai zai fice. Daurewa tayi tace “Mun gode sai da safe” “Allah ya kaimu” yace daga nan ya fice. Ta jima a parlourn bayan ya fita.. Daga k’arshe ta nufi side d’in Arshaad har bedroom ta lek’a ganin yayi bacci yasa ta fito ta nufi sama ta koma d’aki. Da kyar ta samu bacci ya d’auketa. Shi kuwa Arshaad yanda yaga rana haka ya ga dare! Yana jinta lokacin da ta shigo, baya san ganin kowa shiyasa yayi baccin k’arya, ko Hudan text kawai ya iya tura mata cewar ‘he’s okay’. Kafin safiya ya gama deciding yanda zai yi da abunda zai cewa Mammy amman still yana d’an d’arr! Ga fargaba ga tunani barkatai shiyasa zazzab’i yace salama alaikom........... Zazzab’in da ya rufar masa ne yaasa da kyar ya iya mik’ewa yayi sallah a daddafe! Kafin 7 kuwa zazzab’in yayi masa rufdugu…. Ganin yana shirin mutuwa ya sanya shi kiran family Doctor d’in da baya so, dole! Ya kira fad’amshi yana zazzab’i mai k’arfi. Ba a rufe 30 minutes ba Doctor d’in ya iso.. Allurai yayi mishi bayan ya duddubashi dan ya san Arshaad ya tsani magani, daga nan ya jona mishi drip yayi mishi sallama… Sai wajajen 11 drip d’in ya k’are da kansa ya zare ya danne, bayan some minutes ya mik’e ya fad’a wanka. Yaji dad’in jikinshi ba kad’an ba kuwa. Yana fitowa ya d’an shafa mai da turaruka ya zura wata cream jallabiya mai gajeran hannu… A hankali ya k’arasa bakin gadon ya d’au wayarshi ya fara kiran Hudan dan tun da safe yaga message d’inta. Bata wani dad’e tana ringin ba ta d’auka! Bayan sun gaisa ya tabbatar mata da ‘he’s okay daman kawai dan zazzab’i ne’. Tace mishi “Anjima around 1 ana buk’atar shi za suyi traditional event d’insu na yaren Shuwa kuma dole sai yana wajen! Inda hali ya turo driver kafin nan, yazo ya karb’a mishi kayan tradition d’in da aka tanada domin shi (wanda zai saka a event d’in) Kayan ba su iso ba sai d’azu shiyasa bata bashi da wuri ba.” Da “to” ya amsa ta daga nan suka hau hirarsu dan yaga kamar hankalinta still a d’an tashe yake. Sun jima suna hira dan sun fi 30 minutes kafin suyi sallama. A hankali yayi shiruuu, yana y’an tunane tunane.. Chaaan! Ya turawa driver d’in da zai karb’o mishi kayan nashi message daga nan ya mik’e yayi kalmar shahada ya fita ya nufi sama wajen Mammy. A stairs suka had’u da ita tana k’ok’arin sauk’owa! Kamar bata ganshiba haka tazo ta wuceshi. Hannunta yayi saurin rik’ewa ya juyo a hankali yace “Haba Mammy.. Ki saurareni please mana.” Ya fad’i hakan kamar mai shirim fashewa da kuka. Ba tare da ta kalle shi ba tace “Ka bari idan Allah ya kaimu gobe naga kayi abunda nace sai in saurareka” “Meye abunda kike so yayi miki goben??” Suka ji muryar Dad a bayan su!. Da sauri Arshaad ya juya yana kallonshi gabanshi na tsananta fad’uwa! Ba tare data juyo ko ta damu da Dad d’inba tace “Ai gaka ga shi nan! Kana iya tambayarshi.” Tana gama fad’in haka ta nufi k’asa wajen bakinsa da take expecting dan sune ma suka ce mata sun kusan shigowa ba daban su ba da babu abinda zai sauk’o da ita k’asan! Tana buk’atar time ita kad’ai, dan ita kanta bata san daliliba amman komai ya kunce mata.. Kame kame Arshaad ya fara bayan ta sauk’a… Babu yadda Dad bai yi da shi ba amman yace mishi “ba komai! Kawai sun d’an samu issue ne shi da ita lokacin tana cell shine yake so suyi settling”. Sam Dad bai yarda da shi ba dan kwata kwata babu kamanceceniya a cikin maganar shi da tata!. Fahimtar da Dad yayi Arshaad d’in ba zai gaya mishi komai ba ne yasa kawai yace “to, shikenan ka samu ku shirya d’in kafin ka bar gidan nan.” Yana gama fad’in haka ya wuce shi shima yayi k’asan. Sai a sannan Arshaad ya sauk’e ajiyar zuciya He needs to talk to Mammy! Idan tak’i ta lallashi tabbas zai b’ullo mata ta hanyar da bata zata ba! Akwai abubuwa da dama waenda ya sani amma yayi shiru kuma ta san ya sani but it’s like kamar ta manta, so he has to
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96