Chapter 3
Chapter 3
yake kallon Mama a kan k’afafuwanta, sai kuma ya juya kan Aslam ya rufe shi da fad’a! Da kyar ya lallab’a Mama bayan tace “ba zata koma ta kwanta ba sai Abba ya fita” Shi kuma yace wa Abban “yayi excusing d’insu” Bayan ya fita, aka samu ta tsaya ya maida mata cannularta. Har zai fita yace musu “banda hayaniya!” sannan ya juya ya fita. Yana fita kuwa Abba ya dawo! Dan haka Mama ta sake mik’ewa.. This time around Aslam ne ya k’arasa inda take ya rik’e mayafin da take k’ok’arin yafawa ya fara magana “Mama dan Allah ki tsaya ki sauraremu, bafa ke kad’ai ya kamata ace ranki ya b’aci a lamarin nan ba, shi kanshi Abba yana da ikon yin fushi kawai dai daurewa yake yi dan yaga an zauna lafiya!! Amman na tabbatar ko kotu aka je to kinada laifin b’oye masa y’arsa da kika yi tsawon shekaru ba tare da ya ma san Akwai ta a duniyar ba! So i think its about time da ta kamata ki nutsu! Whatever it is that happen between you and Abba destiny d’inku ne, so don’t mix it up da issue na laifin ‘b’oye mishi y’a da kika yi’ kiyi putting blame d’in ankanshi, wannan laifin ki ne ba nashi ba! And if kika ci gaba da acting stubborn muma zamu biyo miki ta hanyar da baki tab’a tunani ba!” Da sauri Arshaad yace “haba Aslam wanne irin magana ne kake yi haka?? At least ai she is an elder watch your tongue mana!!!” Tabbas daman ko Arshaad bai fad’a ba Mama ta gane wannan Aslam ne, dan kamanninshi basu chanja ba kwata kwata, kenan Arshaad d’in shima realative d’insu ne maybe ma brother d’inshi ne dan gashi suna kama sosai!! Ta yiu Abba ne ya turo shi ko kuma me kenan hakan yake nufi? idonshi yana kansu all this time amman sai yanzu yaga ya dace ya nuna kanshi ko ya ne abun yake???? Gaba daya kan Mama ya d’aure tamau!!!......... Maganar da Aslam ya fara yi a fusace ne ya dawo da hankalinta wajen “Elders! elders!! elders!!! Shin duk meye ne farkon issue d’in nasu?” Bai jira jin amsar da Arshaad zai bashi ba yace “Biyewa son zuciyan elders d’in da akayi ne ai duk ya jawo haka!! Itanma kuma I’m pretty sure idan aka yi musu laga laga problems d’in da zata kawo ba kad’an baneba! Tun ranar da Granpa ya nunawa Abba video d’in d’aurin aurenta Abba yake fama da ciwon zuciya har yau d’innan!! Kuma all those years bai samu sauk’i a wajen kowa ba! Fama yake yi da rashin lafiyanshi ba wanda ya damu!! Sannan yanzu kuma itama zata b’ullo da nata issue d’in? Da wanne akeso Abban yaji da?” Ya yiwa Arshaad tambayar yana kallonshi.. Bai damu da jin amsa daga gareshiba dan daman ya san ba lalle ya samu ba, ya juya ya kalli Mama sannan yace “Ba zan d’agawa kowa k’afa ba! daga yau, ke ko Ummi, hatta Granpa!! Therefore I’m advising you to drop this attitude and stubbornness da kuma haushin Abba da kike ji, ki tsaya ku dedeta akan issue d’in Huda If not, wallahi kinji na rantse miki da kaina zan kaiki kotu!! Kuma sai inda k’arfina ya k’are!!! Dani za kiyi ba da Abba ba...” “Huda mik’o mini purse d’ina” Shine kawai abinda Mama tace ba tare da ta zare kwayar idanunta a cikin na Aslam wanda tunda ya fara magana suke kallon juna ba!. A hankali Hudan ta zare hannunta daga cikin na Abba sannan ta d’auko jakarta ta zaro y’ar k’aramar purse d’in Maman a ciki ta mik’a mata tace “Gashi” Hannu Mama wadda har yanzu take kallon Aslam ta mik’a ta amsa sannan ta d’auke idanunta daga kanshi ta sauk’e akan purse d’in ta zuge ta! Bayan wayarta ba komai a ciki sai chanjin naira talatin ashirin da biyar biyu. Zip d’in dake a gefe acikin purse d’in ta zuge sannan ta zira y’an yatsunta ta fara lalubawa.. Wasu takardu an ninkesu ninkin k’anana guda biyu ta zaro ba tare da ta rufe ba ta mik’awa Hudan purse d’in.. Ta farkon ta fara bud’ewa ganin ba ita take nema ba yasa ta mik’awa Hudan tace “ta ninke ta mayar mata ciki” Sannan ta fara k’ok’arin bud’e ta biyun… Hawayen da suka zubo mata ta sa hannu ta share bayan ta gama karantawa sannan ta cillawa Aslam a dede setin fuskar shi. Da sauri jin takardar tana shirin sauk’a k’asa yasa hannu ya cafe ta sannan ya d’ago ta ya fara karantawa… Mama bata jira ya k’arasa karantawan ba ta fara magana “Aslam za ka iya kaini kotu! amman ka sani ni ba zan biyeka inyi shariah da kai ba, nasan kun fi k’arfi na ta ko wacce siga, sai dai kuma ni kotun Allah zan kaiku! Nan ce k’arshe kuma shine zai bi mini hakkina! Dan ba zan yarda ku dake ni kuma ku hanani kuka ba!” Tana gama fad’in haka kuka ya kufce mata ba tare da ta shirya ba. Da mamaki Abba wanda ya k’araso ya karb’i takardar ya hau karantawa yake sake maimaitawa…. Shiruuuu, ya d’an yi sai kuma kawai ya ninke takardar ya sa a aljihun gaban rigarshi! Dan tabbas yau za a yita ta k’are a estate d’insu!! Ba zai yiu ace yana rubuta takardun da bai san lokacin da ya rubuta su ba! A daa yana kokwanto yanzu kam ya samu clue. Ajiyar zuciya ya sauk’e sannan ya k’araso gaban Mama yace “Maryam! na rantse da girman Allah ba nine na rubuta wannan takardar ba! Ban san da zamanta ba kuma ban san dalilinta da ranar data iso gareki ba!” Cikin kuka Mama tace “naji Abba baka san da takardar nan ba ita kuma Hudan laifin me tayi maka!? Ko sau d’aya fa baka tab’a lek’ota ba! Cinta shanta suturarta duk baka sansu ba! Idan ni nayi maka laifi ka datse igiyoyin aurenka a kaina ita kuma laifin me tayi maka daka kasa koda lek’o ta ne????” Kamar Abba zai yi kuka da ihu yace “Maryam, zabi aka bani ko in fita harkar ki for ever ko kuma ku k’are rayuwanku a jail ke da family d’inki har abada!!!Daman kuma an riga anyi agreement dani ke kin sani an yi agreement akan ‘duk ranar da wani naki ko ke kukaje inda yake dole akwai consequences !’ Duk da haka ban hak’ura ba Inata k’ok’ari da adduar in samu a gyara abun sai kawai naji d’aurin aurenki bagatatan!! Ya kikeso in yi??” “Nifa duk ba wannan nake son ji ba, tsakani na da kai it’s over! Ko ma menene ya faru ya riga ya wuce! Laifi yanzu da nake magana a kai ba ni ka yiwa ba! Y’ar ka ka yiwa, kuma ko ita ta yafe maka ni ba zan yafe in yarda ba!! Dan haka kawai ka juya ka tafi dan ban san me ka zo yi anan ba!.” Aslam wanda yake ji kamar zuciyarshi zata tarwatse ne yace “Wai sau nawa zai yi miki bayanin ‘bai san kin haihu ba’ Hatta shi kanshi Granpa d’in bai san kin haihu ba!! Kuma da kike ta cewa bai zo inda kike ba, was ita not you da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96