Chapter 76
Chapter 76
Allah yayi mishi, duk da anso a maidashi majanuni, sai Allah yayi mishi muwafaƙa da littafinsa maisarki, yazama sihirin yayi mishi tasiri tako ina, amman banda gefen addininshi. Wasu irin hawa masu ƙunu yaji suna tsatstsafo mishi, cikin jijiyoyin kekyawan idanunshi, sabida ganin yadda Ya Jafar ɗinshi ke karatu yana, kuka ya za'ayi ya sama mushi farin ciki a rayuwarsa ta ina, zai san me ke cin zuciyar ɗan uwan nashi. Jin yadda ransa ke ƙuna da tafasa ne, yasashi. Komawa ya jingina bayanshi da jikin kujer, kamar yadda Jafar yake mahaddacin haka shima settin kab tana kanshi, Ido ya lumshe tare da yin bisimilla kana ya fara karu inda ya ɗauko daga forkon suratul. Noor ya farayin ƙasa. Saida sukayi awa ɗaya cur kana, Suka fara Azkar, wanda sai da sukayi 23 minutes suna, jero addu'o'in cikin harshen dake nuni da cikekkiyar jimla ta larabci da lugga. Koda suka shafa, sai ya ɗan kalli ɗan uwanshi dake riƙe da hannunshi gam. Ya lura Ya Jafar na tsoron kada ya kuma tafiya ya barshine, yasan duk sanda yayi doguwar tafiya ya dawo, haka yake liƙe mishi. Hannunshi yasa, ya share mishi hawayenshi kana, ya miƙa tare da jawo hannunshi, yasani yanzu lokacin yin baccinsa ne, Side ɗinsu, ya nufa dashi, ta wata ƴar siririyar hanyar dake tsakanin sashukansu. A babban falon suka samu Juwairiyya. Tana ganinsu, ta miƙe da sauri, fuska ɗauke da murmushi kana ido na tsatsafo da hawaye tace. "Barka da dawowa, Sheykh, Alhamdulillah zamu samu nitsuwar Ya Jafar". Kanshi ya sunkuyar sabida bai son ganin hawayenta, Hannunshi ɗaya yasa yana shafa, kam Mimi data ruggumeshi ta ƙafafunshi, cikin murmushi ta nitsuwa yace. "Mimina anyi sallako?". Cikin sauri ta gyaɗa kanta alamar eh, Shi kuwa kanta ya kuma shafawa tare da cewa. "Kinyiwa Ya Jafar ɗina Addu'o'in Allah ya bashi lfy ko?". Kanta ta kuma gyaɗawa tare da cewa. "Eh nayi mishi". A fakaice ya ɗan kalli Juwairiyya dake rugume da yarsu karamar, cikin sanyi yace. "Kukan bashi da wani amfani, muyi ta mishi addu'a, in sha Allah dukkan tsanani yana tare da sauƙi. Ina roƙon Ubangijina mahaliccina a cikin dukkan Ayyukana, daya aramin rai da lfy, kada ya ɗauki raina ko na ɗaya daga, cikinmu, har sai ya nuna mana lfyar ya Jafar, ya faɗa mana abinda ya maidashi haka a dare ɗaya, nasani shine ɗaya rak yasan meya faru, a dare mai duhu da muni na rayuwarmu". Cikin sanyi tasa tafin hannunta ta share hawayenta. Shi kuwa Sheykh, wucewa yayi da Ya Jafar ɗin har cikin ɗakinshi, bisa gado ya zaunar dashi, kana yacewa Juwairiyya dake biye dasu a baya. "Yasha mgninshi ne?". Miƙo mishi gorar ruwa da magungunan tayi tare da cewa. "Yaƙi sha, dan daren jiya kwana yayi, baiyi bacciba, Jalal nan abin tausayi, ko nanda can bai isa ya fitaba, sai ya bishi, Kullum sai Jalal yayi kuka". Wasu tafasassun hawaye ne suka cika masa ido, A duniya shi baya son yaga ko yaji na miji na kuka, domin shi ya sani, duk abinda kaga yasa na miji kuka to abun ya tsananta musamman maza irin Jalal yasan ba ƙaramin raunine zaisa Jalal zubda hawayeba. Shiyasa, shi kukan mace bai taɓa damunshi ba a zuciyarshi, domin mutane sunce in kaga mace na kuka to kayi dariya kafin ka tambayi meya sata kukan. In kuma kaga namiji na kuka to kaima ka fara kukan kafin ka tambayeshi meya sashi kuka. Shiyasa shi kukan mace, bai shiga ranshi, sabida yanaga mata sun iya kukan munafurci da kukan gulma dana ha'inci da yaudara, shiyasa in yaga mace na kuka haushinta yakeji a ransa. Maganin ya bashi sannan ya kontar dashi kafin ya wuce, ya koma sashinsa. Yana shiga, falon, ya samu, Haroon ma zaune, shida Jakadiyarsu, tana ganinshi ta faɗaɗa fara'arta cikin kula da so mai zurfi tace. "Farin gani, Garkuwa, Sheykh, Limamin Masallacin Moddibo Joɗa Jikan sarki mai hatimin sarauta." Gefen Haroon ya zauna tare da rumtse idonshi cikin nitsuwarshi yace. "Ummi ki bari mana, babu wani sarkifa sai Allah, Ummi nace ki dena min irin waɗannan zantukan masu sa kan ɗan adam girma". Murmushi mai cike da tarin so, sabida ita dai jinshi take tamkar ɗan da raina a cikinta ta kuma haifeshi, Koda yake hakan baya rasa nasaba, da cewar itace jakadiya gareshi tun randa aka haishi bacci kawai ke haɗashi da Mamanshi. Sai dai takanzo inda suke su sashi a tsakiya sunai mishi wasa da kallo mai cike daso." Ganin tayi kasake tana kallonshi ne ya sashi ɗan gyara zama, cikin girmamawa yace. "Ina kwana Ummi, ya su Jalal?". Murmushi ta kumayi tare da cewa. "Lfy lau Alhamdulillah, Jalal ya zama mazaunin gida, tunda ka tafi sabida, duk inda yaje , Jafar zai bishi, sai dai kuma abokanshi masu shigar banza har gida suke biyoshi, wani sa'in kwana kiɗe-kiɗe da rawa sukeyi a sashinsu, suna shan sigari. Wasu lokutan dole, Jamil yake gudowa ya bar musu can yazo wurina yake kwana, ko ya shigo nan wurinka". Kanshi ya ɗan maida baya, a hankali yace. "Ummi Jamil da mata?". Kai ta ɗan kauda kana a hankali tace. "Tafiyar bata sauya zaniba, kwanaki uku da suka wuce wata tazo daga, Kano wai ita ƙawarshi ce, kwananta biyu, a sashin Juwairiyya, da Abbanku ya samu lbrine ya korata". Cikin sanyi yace. "Ummi waya gayawa Abba?". Kai ta jujjuya tare da cewa. "Allahu alamu, yadai ji har yace zai kori Jamil ya bar mishi gidanshi, to da yake Jafar yana wojen ne, sai ya riƙe hannun Jamil yayi ta kuka, hakane yasa ya barshi, Mamanku kuwa kuka tayi- tayi". Wani irin zazzafan numfashi ya fesar kana, ya juyo ya kalli Haroon a hankali ya kuma kalli, Jakadiyarsu, cikin sanyi yace. "Basaji Ummi suna samin tunani a raina, ga wannan kuma shima ƙato dashi, sai ya ruggumi waya yayi ta chatting ko waya Da waccar yar mitsitsiyar yarinya Jannart ɗin. Da asuba nayi ta tadashi yafi sau uku baya tashi, sabida bai bacci da wuriba, gashi ko cikekken jam'i bai samuba". Ido Haroon ya lumshe tare da cewa. "Jiya dai ba chatting ko waya da Jannart bane, ya hanani baccin da yasani makara, Ummi ƙarshen darefa muka iso sabida ya sani dole sai mun taho nan." Murmushi Ummi tayi kana tace. "To Haroona ka kiyaye batun tsaida salla kan lokacin ta, kaji ko?." Hararan Sheykh yayi tare da cewa. "To Ummi". Ita kuwa Jakadiyarsu cikin muryar kula tace. "Haroona yaushene bikin naku kam?". Kanshi ya ɗan shafa kana yace. "Uhum Ummi saura watanni bakwai in Allah ya yarda, Ni dai zanyi aure in bar babban tuzurun". Bai kulashiba saima tashi yayi ya nufi bedroom. Ita kuwa Jakadiyarsu cikin yin ƙasa da murya tace. "Yauwa ya dai-dai ta da Jazrah ko?". Baki ya ɗan turo tare da cewa. "Uhum Ummi gudowafa yayi, kuma wlh in ba dagewa kukayiba, wannan bauɗeɗɗen ɗan naku, ustazu bazaiyi aureba, mutun duk yadda akayi dashi sai ya kauce". Kai ta ɗan juya ta kalli ƙofar ɗakin daya shigan, cikin yin ƙasa da murya tace. "Uhum ga zahiri ko mgnar aure akayi sai ya bar wurin." Haka sukayi ta hira da yake akwai sabo tsakaninta dashi. A sashin Hajia Mama kuwa, ita da kanta da kuma, Batul suka shiga kitchin sai kuma yardaddun hadimanta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185