Chapter 116
Chapter 116
kuwa Sheykh Jabeer bayan an salla. Ya fito kamar koda yaushe su Jalal na biye dasu a baya. Haroon kuwa suna tafiya a jere, suna cikin tafiya duk suka tsaya fuska a haɗe Jabeer ya juyo ya kalli gefen hagunshi da yaji an dafa kafaɗarshi, Jadda ne ya ɗan kalleshi kana ya kauda fuskarshi ba tare da yace mushi komaiba. Murmushi Jadda yayi cikin sakin fuska yace. "Ƙarfe tara dai-dai jirginmu zai tashi. Zamu koma da kawunan naku duka". Cikin muryar dake nuna cewa yana cikin tsananin ɓacin rai yace. "Allah kiyaye hanya". Ya ƙarishe mgnar tare da juyawa yaci gaba da tafiyarshi. Shi kuwa Jadda murmushi ya kumayi, fahimtar Sheykh yana tsananin fushi da baƙin cikin abinda sukayi mishi. Lamiɗo ne ya kalli Aminin nashi tare dayi mishi alamun ya barshi. Su tafi. Daga nan suka juya duk suka nufi, sashin Lamiɗo, inda aka gama shirya manya-manyan Foodflaks a tsakiyar falonshi bisa wani tattausan Turkey carpet mai masifar kyau da taushi. Nan suka zauna sukayi Dinner sunayi suna hira, Tare da yaransu. Bayan sun gamane, suka miƙe dan tafiya Airport sabinda lokacin tafiyarsu ya kusa. Kusan a tare suke fito zuwa babban falon dake tsakanin side ɗin Lamiɗo dana Gimbiya Aminatu. Bayan sun zaunane, Sallama yaje ya sanarwa Gimbiya Aminatu cewa Sarki Jalaluddin yana neman Umaymah da Amaryar Sheykh. Jin saƙon Sarki Jalaluddin daga bakin hadimanta da Sallama ya isarwa saƙon ne yasa ta miƙe ta nufi ɗakin da Umaymah take. A cikin ɗakin kuwa, cikin kula Umaymah take gabatarwa Aysha da abin ci dana taɓa ka lashe dana motsa baki. Adda Rumana kuwa kamar tasa mata abinci har bakinta, Itako Aysha kanta a sunkuye, ta zubawa kulolin abincin ido tana ganin ikon Allah dake wanzuwa cikin kayayyakin cimar, da sai dai gidan wane da wanen. Fahimtar kunya ne ya hanata cin komai yasa suka fito falo suka barta, da Umaymah kawai wacce taketa janta a jiki ganin hakane yasa, ta ɗan yarda taci abincin kaɗan. Suna zaune a nanne Gimbiya Aminatu ta shigo ta sanar musu saƙon sarki Jalaluddin nan, Umaymah ta sake saka mata wata al'kyabbar cikin jin daɗi tace. "Aysha ki saki jikinki dani, ki gaya min dukkan abinda kikeso, yanzu kinga wurin kakanunki zan kaiki. Sarki Jalaluddin mahaifina ne, wanda kuma shine mahaifin maman mijinki, ɗaurin auren sukazo shida yayunmu da ƙannenmu maza yanzu zasu koma jiharmu ne. Kinga wannan kuma Gimbiya Aminatu itace ta haifi mahaifin mijinki. Kana Sarki Nuruddeen ɗan Sarki Bubayero jikan sarki Joɗa, shine kakan mijinki. Mu ma mahaifiyarmu na Raye mijinki ne yasa mata suna Sitti, tana jiharmu ita bata samu zuwaba sai daga baya zata zo". Ajiyan zuciya tayi tare da kamo hannunta kana taci gaba da cewa. "Mijinki ɗan babban family ne gaba da bayanshi. A ƙalla zai ɗaukeki shekaru goma cikin masarautar Joɗa data musulmai baki gama sanin adadin dangi da yawan yan uwan mijinki ta gefen mahaifiyarshi da mahaifinshi ba. Yanzu muje su ganki ki gansu." Cikin sanyi tace. "To Aunty". Murmushi Gimbiya Aminatu tayi tare da cewa. "Ba Aunty ku bace, Mijinki Malam Jabeer yafi yarda da ita fiye da kowa a dangin mahaifiyarshi, Umaymah yake kiranta". Kai ta gyaɗa tare da mgnar zuciya. "Ikon Allah". Ita kuwa Umaymah murmushi tayi kana tana hannunta suka fita. A falo suka samu Jakadiyarsu, da sauri Umaymah tace. "Yauwa kinga wannan itace Jakadiyarsu, itace ta rainesu tun suna yara, bayan mahaifiyarsu babu wanda yasan halin Jazlaan sama da ita a cikin wannan masarautar, ki kasance mai bin umarnin ta, domin itace idonki cikin wannan masarautar, Jazlaan a matsayin uwa mahaifiya yake kallonta ba baiwar gidansu ba". Cikin nitsuwa Aysha ta gyaɗa kai tare da cewa. "Nagode". Ita kuwa Ummi murmushi tayi tare da bin bayansu. Suna isa bakin ƙofar tayi musu iso bayan ta shiga ta sanar musu da isowarsu. A hankali suka shiga, cikin nitsuwa take bin takun Umaymah. Ita kuwa Umaymah har gaban Sarki Jalaluddin da Sarki Nuruddeen taje da ita, cikin shaƙuwarta dasu, ta ajiyeta a gabansu tare da cewa. "Jadda ga amaryar Sheykh Jabeer a sanya musu al'barka". Murmushi yayi tare da kallon Aysha. Wani nannauyan ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa. "Allah ya sanya al'khairi ya basu zaman lafiya. Allah yasa tazo mana da hasken da zai kore duhun daya meye hasken idanunmu". Amin Amin suka amsa baki ɗayansu. Uncle Abdulkareem ne ya ɗan kalleta cikin sanyi yace. "Allah yayi miki al'barka dake da mijinki ya baku zaman lfy mai ɗorewa". Kanta ta ƙara sunkuyawa, Ita kuwa Umaymah matsota tayi tare da cewa. "Kinga ɗan ɗago kanki ki kallesu. Kinga ga Mahaifina. Ga Sarki Lamiɗo". Sai kuma ta nuna Abba dake zaune cikin murmushi tace. "Ga wannan shine mahaifin Jabeer mamanshi kuwa sai gobe a bisa ƙaidar masarautar keda shi Jakadiyarsu da Sallama zasuyi muki jagora ku zagaya cikin masarautarsu baki ɗayansu a nuna miki ahlinsu to da ɗakin mamanshi za'a fara kaiki". Kinga wannan shine babban Yayanmu sarki mai jiran gado. Ga kuma wa ƙaninmu Abdulmumin." Murmushi Lamiɗo yayi tare da cewa. "A a Khadijah a rana ɗaya kikeso ɗiyar taki tasan komaine? Ai abun da wuya, dole sai a hankali zata gane mu". Murmushi Jakadiyarsu tayi tare da cewa. "Hakane kam. Amman gwara an gabatar mata da manya". Sarki Jalaluddin ne ya gyara zamanshi tare da cewa. "To Khadijah mu yanzu zamu wuce, ke kuma sai yaushe?". Murmushi tayi tare da kallon gefen damanta inda Haroon ke zaune da wani kekkyawa mutun mai matsakaici shikara. Mi kama dashi wanda bisa dukkan alamu babanshi ne. Kauda kanshi yayi daga kallon da Umaymah keyi mishi, cikin ƙasaita alamun shima jinin sarauta ne, yace. "Ni kada ki wani kalleni, bance komaiba". Murmushi dattawan sukayi baki ɗayansu, Haroon ma murmushin yakeyi. Ita kuwa Umaymah kauda zance tayi da cewa. "Yauwa Aysha kinga wannan shine Haroon ɗan uwa kuma aboki amini abokin faɗan Jabeer. Akwai kuma ɗan yayanmu Ibrahim shine shaƙiƙin Jabeer shi yana Cairo, amman kwanan zai dawo ki ganshi." Jadda ne ya kuma tsareta da cewa. "Khadijah yaushe zaki koma?". Cikin sanyi tace. "Jadda in Abban Haroon ya amince zanyi wata ɗaya rak, sabida ganin yadda lamuran zasu tafi. tsakanin yaran, ita kanta Aysha tana buƙatar makusanci tare da ita, sabida baƙonci a irin gidajenmu abune mai wuya ga wanda ba irin gidajen ya taso ba". Murmushi Abban Haroon yayi tare da cewa. "Ba laifi na Amince, Amman bazaki ɗauki azumi a nan bada". Da sauri tace. "Na yarda". Haroon ne ya ɗan juya idonshi alum lissafi kana yace. "Ke nan sati uku zakiyi tunda azumin saura wata ɗaya". Kai ta gyaɗa alamun gamsuwa, Jadda ne ya kalli Jakadiya tare da bata umarnin su tafi ita da Aysha. Gane abinda yake nufine yasa ta kamo hannun Aysha suka fita. Gimbiya Aminatu na biye dasu a baya. Gyaran murya Jadda yayi bayan sun fita, cikin nitsuwa da girma ya kalli Umaymah tare da cewa. "Alhamdulillah Khadijah, aure dai an ɗaura, duk da tarin tsana da ƙin abin da ɗan naki keyi. Haƙiƙa baya son wannan abun da akayi mishi. Naga fushi da tashin hankali mai tarin yawa a ƙwayar idanunshi da fuskarshi. Ina da yaƙini bisa halin Jabeer in ya tsani abu tofa ya tsaneshi kenan har gaban abadan, wannan shine babban tashin hankali
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185