Chapter 125
Chapter 125
wakilai, shi a zatonsa ma shine mahaifin Jabeer cikin sanyi yace. "Kai kuma kaine matsayin mahaifi a gareta ku zame mata dangin ta data rasa, naso ace da mata a masu ɗaukanta, dan in danƙa amanarta a hannun macce yar uwarta. Amman ba komai, na baku amanarta dan Allah kada a cutar da ita, domin nima ta kasance amanace a uwurina, domin ƴaƴan mu da muka haifama amanace Allah ya bamu kuma abun kiyayewa, bare kuma ɗiya irin Shatu ɗiyace da take da nasabobi masu yawa a gareni". Cikin gamsuwa Lamiɗo yasa hannunshi ya amshi hannunta daketa karkarwa, tuni niƙab ɗin fuskarta ya jiƙe jilak da ruwan hawaye. Cikin Dattaku Lamiɗo yace. "In sha Allah zan kula da dukkan lamuranta tamkar yadda nake kula dashi Jabeer, kuma kada ka damu akwai masu meye mata gurbin uwa ƙanwa yaya dama duk danginta a cikin masarauta Joɗo, baƙoma baya kukan maraici bare kuma, matar sashin jinina". Cikin sanyi da wasu hawaye Bappa yace. "To Ngd matuƙa". Arɗo Bani ne ya dafashi tare da cewa. "Ka sanya mata al'barka a cikin aurenta ba zubda hawaye ba." Sosai Haroon ya zuba mata ido. Shi kuwa Sheykh Jabeer da mamaki yake kallon Bappa dake zubda hawaye. A hankali su Bappa suka ɗan ja da baya. Shi kuwa Lamiɗo ya juya ya nufi motar riƙe da hannunta. Haroon ne yayi saurin buɗe musu marfin motar, suka nufoshi gadan-gadan. Jalal kuwa ido ya zubawa yatsun hannunta da Lamiɗo ke riƙe dashi. Shi kuwa Jabeer idonshi ya rufe da ƙarfi. Sai kuma ya buɗesu, dai-dai lokacin Lamiɗo ya kawota bakin ƙofar motar tare da cewa. "Mamana kiyi bismillah ki shiga da ƙafar dama". Cikin shessheƙan kuka ta gyaɗa kai tare da yin bisimilla kana ta ɗan sunkuyo, sai kuma kukan ya kubce mata. Shi kuwa Jabeer da sauri ya buɗe marfin motar ta gefen hagunshi. Kamar gilmawar walƙiya ya fita cikin motar. Dai-dai lokacin da Shatu tasa ƙafarta ciki. da sauri yasa hannunshi ya buɗe motar Jadda tare da shigewa ciki yaja marfin ya rufe sabida ji yayi zuciyarshi zatayi bindiga, wani irin dogon ajiyan zuciya ya sauƙe mai ƙarfi. Ita kuwa Shatu, a hankali ta shiga ta zauna, don batama lura da shi bane tabbas dai taga mutun ya fita cikin motar. Tana shiga Haroon ya maida marfin ya rufe Shida Lamiɗo suka koma sit ɗin bayan wannan sabida su a zatonsu Jabeer na ciki. Ganin Lamiɗo ya shigane yasa duk kowa ya shiga motarshi. Hakama Jadda ya shiga ya zauna hankalinshi na woje. Sai da akaja motocin suka fara tafiya ne, ya juyo da sauri jin Jabeer na jan wani ja'irin tsaki mai tare da ajiyan zuciya. Cikin mamaki Jadda yace. "Haaahh kai kuma Meya kawoka nan? Yaushe ka shigo min mota!?". Bai kula Jadda ba, asalima yi yayi tamkar bai jishiba. Haroon kuwa cikin dariya ya ɗan bugi sit ɗin da yake zaton yana wurin cikin juya harcen Larabci yace. "Masha ALLAH, gasar Shaɗi tayi mana rana mun rabaka da gwauranci". Murmushi Lamiɗo yayi tare da kallon Haroon yace. "Saura kai". Murmushi yayi tare da cewa. "Ni ai nan kusa za'ayi". Jin shirune, yasa Haroon yayi shiru, Azotonshi ya ƙin mgna da shariyar ne suka zowa Jabeer bare, yasan yanzu a cike yake. Su Jalal kuwa kab da al'hini suke tafeyi. Jadda kuwa yayi iya mgnarshi yayi shiru ganin bai kulashi ba. A haka suka isa cikin Masarauta Joɗo. Suna isa kuwa Jabeer ya fito ya nufi Side ɗinsa, fitowarsa cikin motar Jadda ne yayi matuƙar bawa Haroon da Lamiɗo mamaki. Haroon kuwa bayanshi yabi da sauri. Suna shiga Side ɗinsa kuwa suka samu babu kowa. Suna gama tsayuwa Sallama ya nufi Side ɗin Gimbiya Aminatu bisa umarni Lamiɗo. Yana shiga a babban Falon ya samu. Umaymah, Ummi, Aunty Juwairiyya, Hibba, Adda Rumana wacce take yayarsu Jabeer yar farin Abba kenan, sai mai bin mata Rumaisa. Kana sai Gimbiya Aminatu dake tsakiyarsu, sai hadimanta. Koda ya sanar musu, sun iso. Kusan duk a tare suka miƙe sai Gimbiya Aminatu ce bata tashiba da hadimanta. Su kuwa da sauri suka nufi woje, Umaymah ce gaba sai Aunty Juwairiyya dake biye da ita a baya riƙe da wani tire wanda samanshi ke ɗauke da al'kyabbar irin tasu ta matan masarauta da kuma wasu sauran tarkace. Suna fitowa motar na isowa har bakin wurin. Da sauri suka nufi jikin motar. Ita kuwa Zuwa yanzu ta tsagaita da kukanta, sabida ababen da take gani a cikin masarautar ya shallake tunanin mai tunani, gaba ɗaya jikinta tsuma yakeyi, sabida idonta na gane mata ababe na ban tsoro. Cikin ranta take mgnar zuci. "Innalillahi wa innailaihi rajiun, wannan wanne irin gidane? Me yake faruwa da mutanen masarautar? Sunko san gskyar junansu?". Da sauri ta rumtse idanunta sabida wasu irin hayaƙi da take gani yana tashi tako ina na gidan yayiwa gidan rumfa gaba ɗayansa. A da sauri ta buɗe idonta jin an kamo tafin hannunta, Umaymah kuwa cikin tsantsar jin daɗin da farin ciki maras misaltuwa tace. "Marhababiki ya binti". Wani irin azabebben tsinkewar zuciya da firgici da razanine ya daki zuciyar Shatu a lokaci ɗaya. Da sauri ta ƙara ware idanunta, dan son kallon matar da take jawota tare da cewa. "Kiyi bismillah ki fito da ƙafar dama, ki riƙe hannuna da kyau ɗiyata, ki kalleni nan nice jagorarki ki taka ƙafarki a inda zakiga na taka tawa". Ido ta zuba mata, tare da fitowa a hankali. Tana fitowa bakin ƙofar Umaymah tasa hannu ta amshi al'kyabbar da Aunty Juwairiyya take miƙa mata. Kangeta tayi kana tasa mata al'kyabbar, sannan ta gyara mata rufuwarshi da kyau ta rufa mata hularshi. Yadda sam mutun bazai samu damar ganinta ba. Ga niƙab ga kuma hular al'kyabbar da lu'ulu'u danke reto a fuskarta. Da sauri Aunty Juwairiyya ta matso tare da cewa. "Marhabin yar uwarta, Alhamdulillah yau kam na samu yar uwa". Adda Rumana ce ta matso kusa da ita tare da yin mgna da fillanci tace. "Sannu da zuwa Masarautar Joɗa ƙanwata". Adda Rumaisa kuwa murmushi yaketayi tare da matsowa, haka suka sata a tsakiya. Jakadiyarsu kuwa sai bin takun ƙafar Shatu takeyin da ido. A haka suka zagayeta, kana hadimai suka mara musu baya. A haka suka isa babban falon Gimbiya Aminatu. Suna isa Umaymah ta kaita har gabanta ta ajiyeta, Cikin tsantsar jin daɗi tace. "Alhamdulillah Gimbiya yau dai ga sabuwar Gimbiya dan yanzu itace amarya ba keba". Cikin dariyar jin daɗi Gimbiya Aminatu tasa hannu ta kamo hannun Shatu da Umaymah ke miƙa mata tare da cewa. "Kishiya ban haushi, ta isa ta zama Gimbiya zakisa yanzu in korata woje". Dariya sukayi baki ɗayansu. Yayinda tuni hadimai mata suketa jere ababen maƙulashe a gaban Shatu. Danginsu, Zuma, Madarar shanu, Da ƴaƴan itatuwa masu sanyi. Ita dai Shatu ƙasa tayi da kanta, tana jin fargaba da kuma tsoron wannan bahagon gidan data shigo. Su kuwa nan sukayi ta mata hidima da nuna mata so. Ganin magriba ta ƙara to ne yasa, Umaymah ta jawo hannunta ta kaita wani ɗaki dake nan kusa dana Gimbiya Aminatu. Tare da cewa. "Yauwa ɗiyata kiyi salla. Za'a kawo miki abinci, kada kici komai sai nazo". Cikin sanyi ta gyaɗa mata kai. Ita kuwa Umaymah hannu tasa ta fara zare mata al'kyabbar, koda ta cire
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185