Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 19

Chapter 19

Garkuwa Book 1 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kuma zazzafan kunun nono da yaji nono da zuma. Sunaci suna ira ga hasken farin wata daya fito yayi ral ya haska ko ina na gidan. Cikin jin daɗi, Giɗi yace. "Shatu hutun mai tsawone ko gajere?". Kunun nonon data kurɓa ta haɗiye kafin tace. "Eh to Yaya Giɗi hutun sati uku ne muka samu". Seyo ne ya amshi zancen da cewa. "A hutun da ɗan yawa". Shi kuwa Giɗi dariyar mugunta yayi tare da cewa. "Ai kuwa naji daɗi wlh sai kinyi kiwo kema kiji hazar da muke ji". Bappa ne ya amshi zancen da cewa. "Giɗi mugunta ba kyaufa, Wato kai wuya kakeso tasha". dariyar ƙeta ya kumayi tare da cewa. "Ai naga duk anfi kashe mata kuɗi kuma muke wahalar kiwo, makarantar da takeyi kawai duk shekara kusan million 1 takeci muko sai wuyar tsiya da muke ci". Gaini ne yace. "To ai kuma ita bata da shanu ko ɗaya kaikuma garke biyu kakeda naka na kanka haka kuma muma". Ladone ya ɗanyi murmushi bayan ya haɗiye lomar da yasa a baki yace. "Ato gaya mishi kam". Ummey ce ta ɗan kalli Shatu tare da cewa. "Kici abinci ki dena shan ruwan kunu ba rike miki ciki zaiyiba". Da sauri Junainah tace.. "A a Ummey ai Inna tana tasa an yanka zabbi zata gasa mana Adda karkici tuwo". Dariya sukayi baki ɗayansu dan duk kowa yasan Junainah tsakaninta da. Nama akwai ƙauna. Haka dai sukaci gaba da hira da dariya, Hatta makiyayan gidan nasu wanda ba yan gidan bane saida suka shigo akayi ta hira da dariya dasu. Suna cikin hirar ne yaro yayi sallama cewa Ba'ana yana kiran Aysha, cikin sauri Aysha ta konta tare da lumshe idonta, ganin hakane yasa Ummey cewa yaron. "Ayyah kaje kace mishi yayi hakuri AYSHA har tayi bacci, in ba matsala yaje sai gobe, in kuma da matsala a tada ita". To yaron yace ya juya ya tafi. Fitarshi bada daɗewa ba ya dawo, Yace,. "Yace a barta tayi baccinta gobe da safe zaizo". To sukace kana yaron ya fita ya tafi. Sukuwa sukaci gaba da hira. Gashin zabbi mai kyau Inna tayi musu gashin da yaji haɗi, nan ta ware na maza ta basu kana ta ware nata da Ummey sannan ta bawa Aysha da Junainah, nan fa sukaci gaba da ci, suna hirarsu ta zumunci wanda ko yaushe haka suke duk daren kuma anan Bappa ke karantar dasu. Bayan duk sun fara miƙewa da dare ya fara nisa, a hankali Bappa yace. "Aysha kinyi baccine?". Cikin sauri ta miƙe zaune daga konciyar da tayi kanta na bisa cinyar Ummey, a hankali tace. "A a Bappa idona biyu". Tashi zaune yayi tare da fuskantar ta, ganin haka yasa ta rarrafa a hankali ta iso gabanshi, cikin kulawa yace. "Ya karatun naki?". Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa. "Alhamdulillah Bappa karatu na tafiya yadda ya kamata". Kanshi ya jinjina tare da cewa. "Baki da matsalar komai dai ko?". Da sauri tace. "Babu matsalar komai Bappa na". "Masha ALLAH haka nake son ji, Allah ya miki al'barka dake da sauran ƴan uwanki baki ɗaya. Allah ya miki zaɓi da miji na gari". A hankali suka amsa da Amin Amin gaba ɗayansu. Daga nan kuma yayi ta mata nasihar ta kama kanta, Jin sanyi ya fara yawane yasa sukayi saida safe kowa ya nufi makoncinsa. Yayinda a can cikin garima masu hira a dandali duk sun watse. Al'walan konciya bacci sukayi kana suka shiga, ɗakin Ummey da yake mai girma da faɗi an laileyeshi da siminti da leda carpet, kana ga jere da gadajenta biyu masu kyau, Ita da Junainah suna kan babban gadon ita kuwa Ummey tana kan ƙaramin gadon. Hira sukaci gaba da yi irin hira ta tsakanin uwa da ƴarta, cikin sanyi tace. "Aysha, kinji Hashimu ɗan Arɗo ya rasu ko?". Da sauri cikin razana AYSHA ta tashi zaune tare da cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun Ummey banjiba yaushe ya rasu meya sameshi?". Ta jero tambayoyin a tare kana ga hawaye na kwaranya cikin sanyi Ummey tace. "Kwanan ya rasu, yankan rago akayi mishi sai tsintar gawanshi akayi a burtali ana zaton Ɓachamawa ne suka kasheshi". Cikin shessheƙan kuka tace. "Allah sarki Ya Hashimu Allah ya jiƙanka da rahama yasa ka huta, Allah ya saka maka duk wanda ya kasheka Allah ya toni asirinshi." Sai kuma ta konta tana kuka sosai saida tayi kamar 3 minute tana kuka kafin tace. "Yanzu shike nan Ummey duk wanda zai soni ƙarshensa yankan rago?". Cikin yin ƙasa da murya Ummey tace. "Ba dukaba in sha Allah akwai wanda zai soki ya kuma rayu dake bisa lfy". A hankali tace. "Ummey wa zai soni a irin yadda kullum ya Ba'ana yake kara zama masafi mugu, wa zai tsira da tarkonshi?". Da sauri Ummey tace. "Wanda yake mai ƙare rayuwarsa a amɓaton Allah da kekyawar zuciya." Kai kawai ta kife tana mai kukan rasuwar Yaya Hashimun ta, a haka dai sukayi ta hira har bacci ya sacesu. A can cikin masarautar Joɗa kuwa. Bayan anyi sallan ishane, Sheykh ya fito cikin shirinsa na tafiya, riga da wondon yaɗin wagambarine a jikinsa sai bakar alkyebbarsa dayasa kana sai hiraminshi fari da kuma bakin tarden dake saman kanshi. Sai takalman sarautar da ya saka, suma farare kalar hiraminshi. Jamil ne ke biye dashi a baya yana riƙe da ƴar madai-daiciyar jakar Hamman nasu, kana hannunshi ɗaya na riƙe da jakar System ɗinshi, shi kuwa Sheykh woyoyinsh ya zura a al'jihunshi. Tare suka fito, a mashigar ƙofarshi nan sukayi kiciɓis da Jalal, da Jakadiyarsu, cikin muryar da bata cika fara'aba Jalal yace. "Please Hamma Jabeer, dan Allah karka daɗe". Kafaɗanshi ya dafa tare da cewa. "In sha Allah bazan daɗeba Jalaluddin, ka kula da kanka da Yah Jafar". Kanshi ya gyaɗa alamar to, Jakadiya kuwa, ido ta zuma musu tana jin so da ƙaunar yaran kamar itace ta haifesu a cikinta. Cikin girmamawa Sheykh yace. "Ummi bari inje in sallami Yaya Jafar". To tace kana ta juya ta nufi sashin, Hajia Fatima, tsakar gidan Maigirma Habibullah. Su kuwa suna shiga a falo suka samu Yayan nasu da iyalanshi, a hankali Sheykh ya ƙaraso gaban ɗan uwan nashi, cikin sanyi yace. "Ya Jafar zan tafi Leddi julɓe Sitti ta nemi muje gidansu, can ƙasar saudia, Abba ne da kanshi yace inje badon hakaba babu inda zanje in barka a haka, zanje ƙasa mai tsarki tushen mahaifiyarmu da kakarmu da take jininsu, in sha Allah zan nemi al'farman a buɗe min ka'aba zan shiga har ciki inyi maka addu'o'in samun lfy, kuma bazan daɗe ba zan dawo kajiko Ya Jafar?". Bai kulashiba kana kuma bai bar karatun da yakeyiba, sai dai hawaye daya fara zubdawa a jere-a jere. Jamil kam juyawa yayi ya fita da jakar ɗan uwan nashi dan yasan zaiyi kuka. Ita kuwa Juwairiyya cikin sanyi tace. "Babu komai Sheykh Allah ya kaiku lfy ya dawo daku lfy in sha Allah zanyi ta kula dashi yadda ya kamata". Jalal kuwa tattauna laɓɓa shi kawai yake tamkar zai hudasu, tabbas sunada ciwo a cikin zuƙatansu musamman Sheykh da yasan shike ɗaukan damuwarsu kab harda ta mahaifiyarsu". Shi kuwa Sheykh hannu yasa yana sharewa Yayan nashi hawayen, a hankali suka juyo suka kalli ƙofar ɗakin Hajia Mama ce,

Table of Contents

Chapters

185 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182
  183. 183 Chapter 183
  184. 184 Chapter 184
  185. 185 Chapter 185
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});