Chapter 172
Chapter 172
Affan dasu Yusuf sunzo, shine Affan yace inzo in tasheka". A hankali ya buɗe idonshi, Yanayin yadda take ɗan marin gefen fuskarshi da hannunta wanda ke ɗaure da agogo. A hankali ya ɗago hannunshi ya ɗan kan hannunta ya kamoshi ya riƙe, cikin tsoro ta fara kiciniyar kwace hannunta, Sai kuma tayi zuru, jin ya ja hannun da ɗan ƙarfi ya kawoshi dai-dai saitin fuskarshi. Idonshi ya zubawa yatsun hannunta da kullum in ya gansu da jan lalle yake tuna mishi baya. Da sauri tace. "Wash Allah na". Jin ya murɗa hannun ya juyo da fuskar agogon inda zai gani. Ƙarfe biyu da miti arba'in da ɗaya. Du-du baccin 40 minutes yayi tazo ta tasheshi. "Harda zuba min maruka". Ya faɗa a ransa. Ita kuwa kan tattausan suman ta ajiye sinsiyar hannunta. tana jin kanta na sara Especially in ta kalli saitin ƙasan gadonshi." A hankali ya sake hannunta kana ya yunƙura ya juya rigingine, ya fuskanci sama, ita kuma tana zaune tana kallon ƙasa hakanne yasa suna fuskantar juna, cikin wani irin yanayi ya zuba mata ido na wasu sakanni. Shigarta tayi masifar mishi kyau. Kodan tasa kalan kayan da yafi sone. Cikin muryar bacci yace. "Shine harda dukana? Meyasa ne ku mutanen garincan kuke son dukan mutun da kallon jikinsa?". Cikin tura baki tace. "Cinyana, nagaji kanka nauyi". Bai janye idonshi a kantaba ya yunƙura ya tashi zaune tare da juyowa ya fuskanceta. tanƙwashe sawunshi yayi tare da cewa. "Me zaki kalla a jikina? Woto Kin zama kamar ɓarauniya ko? Me kike son gani? Wani abu kike sone?". Cikin tura baki tace. "Nifa tada kai a bacci kawai nayi". Hannunshi yasa ya riƙo hannunta, yatsunta ya zubawa ido, cikin wata murya mai sanyi yace. "Masha Allah, kinyi kyau." Wani irin sanyi taji kalmar tashi tasa mata a ranta, ido ta ɗan ɗago ta kalleshi. Shima ita yake kallo, ido ya lumshe jin sautin zazzaƙar muryarta a hankali tace. "Nagode". Tonƙoshe kansa yayi bisa kafaɗa kana hankali ya sake hannun nata. Fuskarta ya kalla tare da taɓe baki yace. "Waya koya miki irin sa lalle Mammeyyyyy nah!? Dan tafi ko wacce mace iya lalle". Cikin sanyi da nazartar yadda ya kira sunan Mammeyyyyy da yadda lokacin ɗaya idonshi suka fara sheƙin tsastsafo da zafafan hawayen da ba zubowa zasuyiba. Cikin son gano meke cikin zuciyarsa tace. "Ummeyy nah ce ta koya min tun ina ƙaramar". Yatsunta ya jujjuya kana ya miƙe tsaye. A hankali ya juya ya nufi bathroom sabida baya son ta hango wutar ƙunar dake ransa. Ita kuma binshi da ido tayi, tare da langoɓar da kanta tana kallon sharabansa da gargasa yayi musu ƙawanya. A haka ta shiga wani nazarin tana mai maimaita sunan da taji ya kira da cikekken so shaƙuwa ƙauna tausayi rauni shogoba *Mammeyyyyy.* Ta maimaita sunan a fili. Shi kuwa Sheykh Jabeer al'wala yayi kana ya fito. Yayi mamakin ganinta a zaune bata fita ba. Hararanta yayi ganin yadda taketa kallonshi. Jallabiyar shi ya zura, kana yasa al'kyabbar, tare da sa Hiraminshi. Sannan ya fesa turare. Duk inda yayi tana binshi da ido. Wayarshi da yafi yawan riƙewa ya ɗauka ya zura a al'jihunsa. Sannan ya nufi bakin ƙofa inda takalminshi suke yana cewa. "Wannan kallon maitan fa". Da sauri ta janye idonta. Cikin daƙilewa yace. "Kada ki cinyeni da ido fa. Bana son kallo, ko kina bina bashine?." a hankali ta miƙe tare da lumshe ido ta biyu bayanshi. Tana gyara mayafinta tare da cewa. "Ni ban kalleka ba". "Uhummm." yace a taƙaice. Kusan a tare suka fito. Yana gaba tana bayanshi, Suka fito tsakiyar falonshi. Tsayawa ya ɗanyi ya gyara masaƙalin Al'kyabbar tashi. Shiyasa ya zama a jere suke tafiya tana gefen damanshi. A haka suka fito cikin corridor'n. Suka doshi Falon cikin kwarjini da dacewa da juna sai ƙamshi da sheƙi zallan kyau sukeyi. Da Sallama a bakinshi suka kutsa kai cikin falon. Wani irin dariyar jin daɗi Affan da suke can Dinning area yayi, suna cin abinci da Ummi ta matsa suci. Wani irin murmushi Yusuf da Aryan ma sukayi tare da miƙewa suka nufi inda uban gidan nasu ke tsaye da kekyawar tauraruwarshi mai haskawa. Affan kuwa wayarshi ya zaro yana kekkebta musu hoto tare da cewa. "Ga amarya, ga ango, suna carabki da zallan kyau da ƙamshi". Murmushi sukayi dukansu, ita kuwa Shatu tana tsaye gefenshi. A haka su Affan suka iso. Suna Isa Affan ya ruggumeshi shima Sheykh ruggumeshi yayi tare da make ƙeyarsa. Da sauri ya janye kanshi tare da cewa. "Wayyo Allah na yanzu Hamma Jabeer na girma harda yaran nawama ban wuce dukaba". Murmushi yayi tare da, Ruggume Yusuf da Aryan Allah ya sani yana masifar son yaran nan har gobe bashi da ɗalibai sama dasu yana sonsu so na musamman, duk sanda ya gansu yakan tuna ƙuruciyarsu tun suna yan shekara goma sha biyar-biyar yake tare dasu shi ya horas dasu. Yana tura irin tarin ƙalubale da suka fuskanta a gasar Polo da kuma irin nasarorin da suka samu Especially Yusuf nashi yana tuna yadda yaran suke sheƙiyanci in sun haɗu, yana jinsu tamkar su Jamil. Cikin murmushin ya shafa kansu tare da cewa. "Sannunku da zuwa". Cikin jin daɗi sukace to. Bisa kujera ya zauna su kuma suka zauna a ƙasa a gabanshi kan carpet. Ita kuwa Shatu a hankali ta juya ta nufi kitchen ganin Ummi ta nufi can. Hibba kuwa na gefensu tana gayawa su Jalal ga Ya Affan fa. Da gefen idonshi ya bita da kallo. Har ta ɓacewa ganinsa, Allah ya sani yana son abu blue baya iya cire idonshi kan abu mai kalar shiyasa yake jin baya gajiya da ganinta, da zai samu kada tayi nesa dashi, dan tayi mishi kyau sosai farar fatarta ta fito fes kamar balarabiya ji yake tamkar ya bita duk inda tayi. Cikin murmushin ya kalli Aryan yace. "Aryan Ina su Yusuf ƙaramin". "Alhamdulillah suna lfy Malam". Kai ya jinjina tare da cewa. "Masha Allah". Sai ya kuma kalli Yusuf yace. "Ina mai sunana baka zomin da shiba". Murmushi Yusuf yayi tare da cewa. "Malam baka tambayi Aryan ƙaramin ba da yakeso ya zama kamarka sai ka tambayi mai sunanka". Dariya sukayi kana yace. "Ayyah my Aryan, sun kusa tafiya ai in sha Allah Jami'atul Madina zaiyi karatunshi". Da sauri suka juyo suka kalli Jalal da Jamil da suka shigo da sauri. Ruggume Affan sukayi suna cewa. "Oyoyo ya Affan". Hannu ya basu suka tafa kamar sa'ao',insa ne su. Cikin dariya yace. "Tun ɗazu nake kiranku bakwa ɗagawa. Nace waɗannan ana can cikin hayani ". Murmushi Jamil yayi tare da miƙawa Yusuf hannu wanda ke cewa. "Oh wato Affan kawai kuka gani mu ko oho ko". Cikin ɗan sakin fuska Jalal yace. "Afwan Hamma Yusuf ya Aunty Zahra da Mama". "Suna lfy. Sun gaidaku". yace tare da bashi hannun. Kana suka gaisa da Aryan. Sannan suka miƙe sukace bari suje wurin Aunty Mami. Cikin dariya Affan yace. "Eh kujema kuzo da ita taga matar babban yaya". Da sauri Jamil yace. "A a ka kawota da kanka dai". Ya ƙarshe mgnar suna fita. Su kuwa cikin yin ƙasa da kai Yusuf yace. "Uhum dama Malam zamu ɗan shiga wasan daba ne in batsala". Murmushi mai faɗin Sheykh yayi tare da cewa.
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185