Chapter 131
Chapter 131
duk sashukan gidajen anje anyi sallama dasu an kuma basu daman shiga. Tafiya kaɗan sukayi daga sashin Gimbiya Aminatu, ta gefen hagunshi, suka ɓullo farfajiyar wani babban part, Jakadiyarsu na gaba suna biye da ita a baya, Umaymah na biye dasu. A hankali suke taku cikin ƙasaita hadimai da fadawa na mara musu baya. Suna shiga ciki, suka samuwa wata dattijuwar tsohuwa mai tarin shekaru. Cikin murmushin da muryar tsufa tace. "Malamai magada annabawa, lallai yau inada babban baƙo da babbar baƙuwa." A hankali suke tafiya har zuwa gabanta, inda take zaune bisa tattausan carpet hadimanta na kewaye da ita. wanda biyu daga cikinsu, suka tashi da sauri suka kawo ababen motsa baki suka jera a gabansu. Shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya kalli tsohuwar da take matar ga Galadima. Cikin kula yace. "Barka da safiya Innano". Cike da kula tace. "Barka dai Malam Muhammad, mun samu ƙaruwa ko". Kanshi ya gyaɗa mata a hankali haka yasa duk basu ganiba sai ita da yake gabanta. "Cikin muryar tsufa tace. "Allah ya sanya al'khairi. Ya baku zaman lafiya. Yasa matarkace iya rai da mutuwa. Ya azurtaku da zuriya ɗayyiba." Da Sauri Umaymah ta amsa da Amin Amin hakama sauran baki ɗayansu. Ita kuwa Shatu, cikin saisaita nitsuwarta ta ɗan kalli tsohuwar tare da cewa. "Ina kwana". Murmushi tayi tare da kai hannunta ta kamo hannun Shatu, tafin hannunta ta buɗe ta zuba musu ido, na yan wasu ɗakiƙu kana tace. "Lafiya lau, ya baƙu ta?". A hankali tace. "Alhamdulillah". Jakadiyarsu ce ta ɗan rusuna tare da cewa. "Mun barki lfy". Kai ta gyaɗa kana tayiwa hadimanta umarni su miƙo kyautar da take gadon masarautarsun ce farin gyale ne mai kyau da taushi. Umaymah ce ta amsa ta miƙa hadiman dake bayanta. Kana suka miƙe suka fita. Daga nan sashin wani sashin na kusa dashi suka shiga. Wanda yake sashin ƙannen Lamiɗo ne. Saida suka gama da sashukan manyan masarautar. Kana suka nufi sashin Hajia Mama. Tuni tasan da zuwansu. haka yasa ta kimtsa ta tsara komai na tarban surkar tata. A matsayinta na uwar ango. Har can cikin bedroom Ummi ta wuce, su kuma suna biye da ita a baya. Suna shiga suka sameta, zaune bisa kilishi, Batool na gefenta, wacce son ganin amaryar ne, ya hanata tafiya. Hadimanta kuma na zagaye da ita. Suna shigowa ta tashi zaune daga kishingiɗar da tayi. Cikin tsananin baiyana farin cikin ta, ta nunawa Jabeer kusa da ita. a hankali suka iso suka zauna gabanta. Umaymah kuwa gefenta ta zauna. Ummi ko na bayansu hadiman kuma suna can falo. Hannunta tasa ta kamo hannun Jabeer. Cikin fara'a tace. "Alhamdulillah Muhammad Jabeer, Allah ya sanya al'khairi ya baku zaman lfy". To shifa suna ɗaure mishi kai, da tarin addu'o'insu na al'khairi, shi dai ba sonta yakeba ba kuma zama da ita zaiba, to me zai wahal dashi da zaice Amin Amin. Umaymah da Jakadiyarsu ne suka amsa da Amin Amin kamar dai yadda sukayi a sauran wuraren. Batool ce ta kalli Shatu cikin isa tace. "Amarya ki ɗago kanki mana kinga gaban uwar mijine kike". Duk da taji mgnar Batool sai tayi kamar batajiba, Abubuwan ci da sha dake gabansu ne, Hajia Mama ta jawo wani ɗan ƙaramin tray da cups biyu ke kanshi. Gyara zama tayi da kyau, tana murmushi ta kalli Shatu dake mgna a hankali. "Ina kwana Mama". Cikin kula tace. "Lfy lau ɗiyata ya baƙun ta". Alhamdulillah tace, tare da tsurawa madara da zumar da Hajia Mama ta zuba musu cikin kofu nan ido. a hankali ta ɗan muskuta kaɗan tayi baya, tare da ƙara yin ƙasa da kanta. ita kuwa Hajia Mama, kofin ta ɗauka ta miƙa mata. Tare da cewa. "Gashi ɗiyata amshi kisha." Cikin sanyi murya can ƙasa ta girgiza kanta tare da cewa. "Alhamdulillah". cikin nuna kulawa da so Hajia Mama ta ƙara miƙo mata kofin tare da cewa. "A a ɗiyata, amshi kisha, wannan al'adace ta masarautar Joɗa, dole in marabceki dashi." Kai ta kuma girgiza alamun ya isheta. da sauri Umaymah ta matso kusa da ita tare da cewa. "A a Shatu amshi kisha kinji ko?". Cike da mamaki ta ɗan kalli Umaymah ta gefen idonta. jin Umaymah na ƙoƙarin matso da kofin kusa da itane yasa tayi mgna cikin ɗan ɗaga murya tace. "Bana shan madarar". wani irin kallo mai cike da damuwa Hajia Mama tayi mata tare da cewa. "Subahanallahi, bakya sha, kuma, amai yake sakine? Ƙa'idane da dole kishi". Ta ƙarishe mgnar cikin damuwa. Ita dai Shatu shiru tayi idonta na bisa kofunan madarar. Ummi ce ta matsota tare da cewa. "Shatu amshi kisha koda kurɓa ɗaya ne". Cikin rawan murya tace. "Bana sha". Jin alamun rawan murya irinta an takura mutum ne, yasa duk sukayi cirko-cirko suna kallon Madarar. Zuwa can Hajja Mama ta sauƙe wani bahagon ajiyan zuciya, kana ta ɗauki ɗaya kofin ta miƙa Jabeer tare da cewa. "To gashi kai kam kasha naka". Zamanshi ya ɗan gyara tare dasa hannun damansa ya amshi kofin. Wani irin zaro ido Shatu tayi. Kallon kofin takeyi tamkar zata maida kwayar idanunta cikin kofin. duk jikinta tsuma yakeyi, wani irin masifeffen bugawa ƙirjinta yakeyi da ƙarfi. Shi kuwa Sheykh Jabeer zaune yake riƙe da kofin, ya fuskanci Hajia Mama da kyau. Ita kuwa Hajia Mama hannunta tasa ta kamo ɗaya hannun Jabeer da baya riƙe da kofin. Kana ta miƙowa Shatu hannun alamun ta miƙo mata hannunta. Ƙara runsunar da kanta tayi tamkar bata gane me take nufiba. Cikin murmushin Hajia Mama tace. "Kawo hannunki ko ɗiyata". A hankali ta ƙara maida hannunta baya, dai-dai lokacin kuma Jabeer ya ɗago kofin ya kai saitin bakinshi da niyar zai sha. cikin hikima ta muskuta ta ƙara matsowa jikinshi da sauri ta ɗago hannunta kamar zata miƙawa Hajia Mama hannun. sai kuma ta ɗan kaikaice, ta buge c...! Ƙaƙa tsara ƙaƙa By *GARKUWAR FULANI* Ta bugi kofin madarar, ba zato ba tsammani, Jabeer yaji kofin ya tsumbce mishi. ya faɗi gefenshi. Tass ya fashe madarar ta kwaranye a ƙasa. Cikin sauri da tsuƙe fuskarshi ya juyo ya kalleta. Itama ɗin shi take kallo. Ido cikin ido sukayi da ita a karo na forko a rayuwarsa duk da yasan sun taɓa haɗuwa. Kallon kwaɗayye mai irin bakin Junainah, tayi mishi. Sai kuma ta janye ƙwayar idanunta cikin nashi da sauri. Sabida wani irin kallon da taga yanayi manata. Umaymah da Ummi kuwa, kallon junansu sukayi, cikin yanayin son gane ya akayi kofin ya faɗi dan basuga sanda ta ta ɗan buge mishi hannunta. Hajia Mama kuwa cikin tashin hankali da kiɗima ta kalli Umaymah tare da cewa. "Akwai matsala, ita batasha, shi nashi ya kwaɓe." Sai kuma ta maida dubanta ga Shatu cikin alamun damuwa tace kawo hannunki na dama." Still maida hannun nata tayi baya, ba tare da tace komaiba. Ummi ce ta ɗanyi ƙasa da murya tare da cewa. "Miƙa mata hannunki ku gaisa". Murya can ƙasa tace. "Yana ciwo". Ta ƙarishe mgnar da jin haushin kanta da ƙaryar da suka satayi. Batool ce ta kalleta sama da ƙasa kana cikin gyatsine tace. "Umaymah ai wannan ba irin matar Sheykh bac." Sai kuma ta haɗiye ragowar mgnar dan ganin wani irin kallon daya watsa mata na alamun. Ki kama kanki da kiran
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185