Chapter 127
Chapter 127
Jazlaan sama da ita a cikin wannan masarautar, ki kasance mai bin umarnin ta, domin itace idonki cikin wannan masarautar, Jazlaan a matsayin uwa mahaifiya yake kallonta ba baiwar gidansu ba". Cikin nitsuwa Aysha ta gyaɗa kai tare da cewa. "Nagode". Ita kuwa Ummi murmushi tayi tare da bin bayansu. Suna isa bakin ƙofar tayi musu iso bayan ta shiga ta sanar musu da isowarsu. A hankali suka shiga, cikin nitsuwa take bin takun Umaymah. Ita kuwa Umaymah har gaban Sarki Jalaluddin da Sarki Nuruddeen taje da ita, cikin shaƙuwarta dasu, ta ajiyeta a gabansu tare da cewa. "Jadda ga amaryar Sheykh Jabeer a sanya musu al'barka". Murmushi yayi tare da kallon Aysha. Wani nannauyan ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa. "Allah ya sanya al'khairi ya basu zaman lafiya. Allah yasa tazo mana da hasken da zai kore duhun daya meye hasken idanunmu". Amin Amin suka amsa baki ɗayansu. Uncle Abdulkareem ne ya ɗan kalleta cikin sanyi yace. "Allah yayi miki al'barka dake da mijinki ya baku zaman lfy mai ɗorewa". Kanta ta ƙara sunkuyawa, Ita kuwa Umaymah matsota tayi tare da cewa. "Kinga ɗan ɗago kanki ki kallesu. Kinga ga Mahaifina. Ga Sarki Lamiɗo". Sai kuma ta nuna Abba dake zaune cikin murmushi tace. "Ga wannan shine mahaifin Jabeer mamanshi kuwa sai gobe a bisa ƙaidar masarautar keda shi Jakadiyarsu da Sallama zasuyi muki jagora ku zagaya cikin masarautarsu baki ɗayansu a nuna miki ahlinsu to da ɗakin mamanshi za'a fara kaiki". Kinga wannan shine babban Yayanmu sarki mai jiran gado. Ga kuma wa ƙaninmu Abdulmumin." Murmushi Lamiɗo yayi tare da cewa. "A a Khadijah a rana ɗaya kikeso ɗiyar taki tasan komaine? Ai abun da wuya, dole sai a hankali zata gane mu". Murmushi Jakadiyarsu tayi tare da cewa. "Hakane kam. Amman gwara an gabatar mata da manya". Sarki Jalaluddin ne ya gyara zamanshi tare da cewa. "To Khadijah mu yanzu zamu wuce, ke kuma sai yaushe?". Murmushi tayi tare da kallon gefen damanta inda Haroon ke zaune da wani kekkyawa mutun mai matsakaici shikara. Mi kama dashi wanda bisa dukkan alamu babanshi ne. Kauda kanshi yayi daga kallon da Umaymah keyi mishi, cikin ƙasaita alamun shima jinin sarauta ne, yace. "Ni kada ki wani kalleni, bance komaiba". Murmushi dattawan sukayi baki ɗayansu, Haroon ma murmushin yakeyi. Ita kuwa Umaymah kauda zance tayi da cewa. "Yauwa Aysha kinga wannan shine Haroon ɗan uwa kuma aboki amini abokin faɗan Jabeer. Akwai kuma ɗan yayanmu Ibrahim shine shaƙiƙin Jabeer shi yana Cairo, amman kwanan zai dawo ki ganshi." Jadda ne ya kuma tsareta da cewa. "Khadijah yaushe zaki koma?". Cikin sanyi tace. "Jadda in Abban Haroon ya amince zanyi wata ɗaya rak, sabida ganin yadda lamuran zasu tafi. tsakanin yaran, ita kanta Aysha tana buƙatar makusanci tare da ita, sabida baƙonci a irin gidajenmu abune mai wuya ga wanda ba irin gidajen ya taso ba". Murmushi Abban Haroon yayi tare da cewa. "Ba laifi na Amince, Amman bazaki ɗauki azumi a nan bada". Da sauri tace. "Na yarda". Haroon ne ya ɗan juya idonshi alum lissafi kana yace. "Ke nan sati uku zakiyi tunda azumin saura wata ɗaya". Kai ta gyaɗa alamun gamsuwa, Jadda ne ya kalli Jakadiya tare da bata umarnin su tafi ita da Aysha. Gane abinda yake nufine yasa ta kamo hannun Aysha suka fita. Gimbiya Aminatu na biye dasu a baya. Gyaran murya Jadda yayi bayan sun fita, cikin nitsuwa da girma ya kalli Umaymah tare da cewa. "Alhamdulillah Khadijah, aure dai an ɗaura, duk da tarin tsana da ƙin abin da ɗan naki keyi. Haƙiƙa baya son wannan abun da akayi mishi. Naga fushi da tashin hankali mai tarin yawa a ƙwayar idanunshi da fuskarshi. Ina da yaƙini bisa halin Jabeer in ya tsani abu tofa ya tsaneshi kenan har gaban abadan, wannan shine babban tashin hankali na, Sabida yanada lafiya da tsayuwa kan kaifi ɗaya. Ya gayawa kakarshi Sitti babu wani gari na duniya da yakejin ya tsana sama da wannan garin. Yace baya son garin da mutanen garin. Sabida anci mishi zarafi a garin a gaban kafurai an tozarta shiga ta addinin Musulunci". Shiru sukayi baki ɗayansu, tabbas sun san hakane mgnar Jadda. shi kuwa Jadda a hankali yaci gaba da cewa. "Yanzu kubar Yarinyar a ta kwana a nan. Kana a ɗan ɗaga kafa har sai an gyara mata inda zata zauna, kamar ko wacce amarya. Sannan kada kuyi mishi mgnar auren bare ita yarinyar, in anyi haka fushinsa bazai tsanantaba, zaici gaba da al'amuran rayuwarshi, tunda shi mutum ne mai ibada da kuma aiyuka". Murmushi Haroon yayi tare da cewa. "In dai baza'ayi mishi mgnarta ba, to wallahi mancewa zaiyi da ita da babinta ma gaba ɗaya". Lamiɗo ne ya gyara zama tare da cewa. "Ya isa". Murmushi Umaymah tayi sabida ta lura har yau su Lamiɗo basu gama sanin Jabeer da halaiyarsa ba. Shi dai Jadda nan ya jadadda musu cewa, kada suyiwa Sheykh Jabeer mgnar sai an gama gyara komai na sashinta. Ko gaisuwar su bari sai bayan kwana uku a zagaya da ita cikin Masarautar. Nan dai sukayi sallama suka, tafi baki ɗayansu. Suna tafiya, Umaymah ta koma ɗakin da Aysha take, nan ta samu Ummi na zaune da ita. Nan ta zauna ta suka ɗan yi hira ganin alamun gajiya da bacci a tattare da itane yasa, sukayi mata saida safe suka fita suka tafi. Ratsawa sukayi wurin Gimbiya Aminatu suka mata saida safe kana suka fita suka tafi. Cikin tsananin jin daɗi suke tafiya, har suka iso bakin. Mashigar sashinsa, cikin nitsuwa sukaci gaba da tafiya. Shiru ba motsin komai suna gab da isa bakin ƙofar, suka tsaya cikin zaro ido, suka kalli Laminu da Gimbiya Saudatu, cikin haɗe fuska da zafi Umaymah tace. "Aoozubikalimatillahi taaa'ammati minshirin makalaƙa!." Cikin tsantsar tsanarta Gimbiya Saudatu tace. "A kanki hegu masu jajayen kunnuwa". Tana faɗin haka taja hannun Laminu suka fita. Su kuwa Umaymah da sauri sukayi ciki. A falo suka tsaya. Ba kowa a falon haka yasa tayi sauri ta nufi arear'n Side ɗin Jabeer, a falo ta samu Haroon konce bisa kujera. Yana ganinta ya tashi zaune. Cikin gimtse dariyarshi murya a hankali yace. "Yau duk kayan ahlin masarautar Joɗa sai an yagesu baki ɗayansu." Ya ƙarishe mgnar yana nuna mata ƙofar ɗakinshi. A hankali ta kutsa kai cikin ɗakin tare da yin sallama. Can ta hangoshi kan gadon yana konce rigingine, idonshi a lumshe, a hankali takeyin taku tana nufo inda yake. tare da mgnar zuci. "Wato harda sharrin Haroon zayiwa ɗan Umaymah". A hankali ta zauna bisa bedside drower'n. Idonta ta sauƙe bisa goshinsa, cikin mamaki ta juyo ta fuskanceshi da kyau ganin yadda Goshinsa ke....! By *GARKUWAR FULANI* "Kamar tsoffin karnuka". Cikin fusata Gimbiya Saudatu ta miƙe tsaye tare da nufo inda yake. Shi kuwa kanshi ya jinjina tare da cewa. "Kinyiwa kanki Garkuwa da kika tashi daga kan kujerata". A hatsale tace. "Wai kai a zatonka tsoronka nake jine ko meye?". Da sauri ya jujjuya mata kai tare da tsuke fuskarsa alamun baison sautin amon muryanta da take ɗaga mishi, a daƙile yace. "A a, na isa inyi zaton tsorona kikeji. Ke da bakinji tsoron Allah'n daya halicce ki bama, ina zakiji tsoron wani bawa nashi, ai masu tattausan zuciya suke tsoro".
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185