Chapter 18
Chapter 18
tabbas Ba'ana kekyawane. A duniya kab Shatu ce tasan sirrinshi ciki da woje, sai daifa bata san yana sataba, amman duk wani abu na asiri da yadda za'a karya asirin da kuma yadda yake juyewa duk ta sani. To hakanne yasa sam bata fatan ya zama miji a gareta bare uban ƴaƴanta, sai dai babu yadda ta iya. Domin ya mata babbar rana a rayuwarta ya mata taimakon da yasa aka ɗaukar mishi al'ƙawarin aurenta. Gashi kuma duk wanda yace yana sonta karshenshi mutuwa, kuma yana gaya mata cewa duk wanda yace zai rabashi da ita zai kasheshi Wannan yasa kullum addu'ar shirya take mishi da fatan Allah ya rabata dashi lfy innshi ba mai shiryuwa bane. Tafiya sukeyi cikin nitsuwa a hankali, murmushi yaketayi cikin so da ƙaunarta yace. "Mata ya akayi na ganki da ƙaramar jaka?". Kai ta ɗan gyaɗa mishi tana kallon kekyawar fuskarshi, cikin murmushi yace. "Kece kika ajiyeni a kasar Kautal a Rugar Bani, kina ƙare karatunki zamuyi aurenmu in ɗaukeki mubar ƙasar, kawai dolece tasa na hakura da batun aurenmu kiyi karatu, dan naga kina son karatun kuma nasan zaki karantar mana da yaranmu, kuma ina son ki zama babbar lawyer mai zaman kanta, sai ki zama lawyer na koda watan-wata rana, rana zata ɓacin min". Murmushi tayi tare da cewa. "Kamar yaune zan kare karatun, Ya Ba'ana". Kanshi ya rausayar tare da gyara riƙon igiyar jakar da yayi, kana yace. "Allah ya nuna min wannan lokacin, in sha Allah sadakin aurenki Garken shanu ɗari zan bada". Cikin mmki ta zaro ido tare da cewa. "Kai Ya Ba'ana garke ɗari bama shanu ɗariba, ya bana ina zaka samu wannan shanun kaida garken naku ko shanu hamsin bai cikaba". Murmushi yayi tare da cewa. "Allah zai kawosu kafin lokacin auren namu". A hankali tace. "Allah ya kawosu". Amin Amin yace tare da ɗan juyowa ya kalleta, murmushi yayi mata, kana ya miƙo mata jakar tata cikin so yace. "Mun iso bakin Gari ki shiga. Ni zan koma baya dama rakoki nazo nayi kar shaiɗanun bakin kogi su cutarmin dake". Kai ta ɗan jinjina tare da cewa. "Ya Ba'ana lokacin sallah ya kusa fa ai gwara ka shigo sai kayi salla ka koma". Bakinshi ya ɗan tabe tare da cewa. "No bar sallan nan sai bayan mako biyu ina ƙara dafa jikinane kuma in nayi al'walan duk aikin zai karye". Dafa kanta tayi da sauri tare da cewa. "Wa'iyazubillah Wayyo Allah na Ya Ba'ana ka gane mana wannan abin da kakeyi shirka ne,". Kanshi ya jujjuya tare da cewa. "Shiga cikin gari zanzo musha hira da daren". To kawai tace mishi ta juya ta nufi cikin garin. Tana shiga ta kama hanyar gidansu, tana gab da shiga gidane ta haɗu da ɗan makotansu Iro cikin girmamawa tace. "Ina wuni Ya iro". Fuska cike da fara'a yace, "A a lale marhabin da ƙanwarmu yar al'barka anyi hutukenan?". Kai ta gyaɗa mishi sannu da hanya ya mata sannan ta wuce ya wuce. A gindin bishiyar mangoro dake kofar gidansu gab da zaure ta hango Bappanta yana zaune bisa dakalin dake wurin yana al'wala, da sauri ta nufi in da yake fuska cike da jin daɗi. Shima Bappa da sauri ya miƙe yana murmushi yake cewa. "Maraba lale da ƴar al'barka." Da sauri ta iso inda yake tana murmushi mai nuna tsantsar jin daɗinta tace. "Oyoyo Bappa na, Alhamdulillah na sameka lfy, ya Ummey na da Innata?". Dariya yayi tare da matsota yace. "Duk muna lfy". da sauri suka juyo ta cikin gida jin muryar yayunta suna cewa. "Oh wato mu kam bakiyi kewarmu bama ko?". Da sauri tayi gabansu cikin jin daɗi tace. "Oyoyo ƴan uwana Ya Gaini, nayi kewarku mana, musamman Ya Giɗi sarkin son girma". Murmushi sukayi dukansu, Seyo ne ya kalleta tare da cewa. "Wallahi yanzuma mgnarki mukeyi da Ummey, har Junainah na cewa wai ai duk munfi sonki". Dariyar jin daɗi tayi tare da cewa. "Ayyah ƴar ƙanwaliya tawa mai kishidani". Murmushi sukayi baki ɗaya kana Lado ya kalleta tare da cewa. "Shiga gida mu zamu wuce masallaci ne". To tace kana ta nufi cikin gida tana cewa. "Yauwa yaya Giɗi dan Allah a kawomin rake". Kai ya gyaɗa mata kana suka wuce ita tayi cikin gida. Tana shiga da fara'ar jin daɗi da ɗan karfi ta buɗe murya tare da cewa. "Assalamu alaikum, gani na dawo, ina Inna ina Ummey, Junainah ina kike?". Ai kusan a tare suka fito gaba ɗayansu, wani irin tsalle Junainah ta buga tare da rugawa ta nufi kan yayar tata cikin ihu da ɗaga sauti take cewa. "Oyoyo Addana oyoyo". Da sauri Ummey ta harateta tare da cewa. "Ke Junainah magriba cefa, kike irin wannan ihu ke sam baki da nitsuwa". Ita dai batama jitaba. Da gudu ta faɗa jikin Aysha, itama Aysha wurgar da jakarta tayi ta ruggume yar uwarta. Inna da Ummey kam ido suka zuba musu, suna masu jin daɗi irin soyayya da shaƙuwar dake tsakanin yaran nasu. Dariya sukayi baki ɗayansu, cikin jin daɗi inna tace. "To yanzu dai lokacin salla yayi ku shigo kuyi salla tukun sai ayita murna dan yau dai kam nasan kwanan zaune za'ayi". Murmushi Shatu tayi tare da karasowa gabansu cikin ladabi ba biyayya tace. "Inna ina wuni". Fuska a sake tace. "Lfy lau Alhamdulillah ya karatu". "Alhamdulillah karatu dai mun samu ɗan hutu." "Masha ALLAH yayi kyau". cewar Ummey hannun Ummeyn ta kamo tare da cewa. "Ummey ina wuni". Murmushi tayi tare da shafa kekyawar fuskarta tace. "Lfy lau Shatu muje muyi salla ko?". Kanta ta ɗan sosa tare da cewa. "Ummey ni nayi sallana a mota". Dariya Ummey tayi domin ta gano cewa Shatu na fashin salla, Ita kuwa Junainah baki ta tura tare da cewa. "To ba gashi ba, ba yanzu muka gama musuba ya Giɗi ba nace mishi nafi Addana son salla, tunda ni kullum sai nayi ita kuma wata rana sai tace a a ita tayi a makka ko kuma tace wai ai tayi kuma babu wanda zai ganta tanayin sallan". Ummey ce ta. Buge bakinta tare da cewa. "To Aku uwar mgna maza wuce kiyi salla, babu wanda ke son jawabin ki". Tura baki tayi kana ta wuce cikin ɗakin nasu, tana cewa. "Ai dama nasan kunfi sonta". Ita kuwa Ummey harara ta watsawa Shatu tare da cewa. "Ke kuma kada dai ki rinƙa kiyaye bakin wannan magananniyar". Murmushi tayi ta bita kana ta ɗauki buta ta shiga bayan gida dan gyara jikinta, sannan ta dawo. Tana shiga ta samu Junainah ta idar da sallan, Gefenta ta zauna, tare da jawo jakarta, sweet ɗinta data seyo mata, ta kwaso ta fitar mata. Ai kuwa tuni fushi ya ƙare, tazo ta raɓa jikin yayartata. Ummey kuwa da Inna saida sukayi sallan isha, kafin suka, fito tsakar gida dan tuni hadarin nan ya watse sai iska mai sanyi daketa kaɗawa. Bappa da su Ya Ladoma saida aka idar da sallan isha kafin suka dawo gida. Gaba ɗayansu a tsakiyar gidan suka zauna bisa manyan taburmaii guda biyu mazan na kan ɗaya matan na kan ɗaya. Abinci sukeci mai rai da lfy, tuwon faran ɗanyar shinkafa, da miyar ɗanyar kuɓewa data sha man shanu da tantakwashi, sai kifin banda sabi kifi na araha a wurinsu. Sai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185