Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 30

Chapter 30

Garkuwa Book 1 Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ɗan harari Junainah dake cewa. "Uhum ta worke ai dama kawai hegen tsorone da raki". Dariya sukayi baki ɗayansu. Seyo ne wanda yakeda tarin jinƙai da nitsuwa, ya ɗan afa geɗan daya ɓare a bakinshi tare da cewa. "To Amman Shatu meya samekine lokaci ɗaya kika firgita?". Giɗi ne da shi kuma doya yakeci yace. "Kamar mai cutar al'janufa ta zama". Bappa ne ya ɗan kalleta cikin kulawa yace. "Shatu meya sameki ne?". Murmushi ta ɗanyi tare da kallon Ummey dake cewa. "Uhum tsorone da gajiya fa". Kai ta jujjuya a hankali tace. "Allah ko Ummey ba tsoro bane". Sai ta kuma meda hankalinta kan Bappa cikin sanyinta tace. "Bappa naga abinda ya firgitanine. Shin Bappa dama bakan Gizon cikin curi yake fitowa ne?." Cikin mamaki suka zuba mata ido baki ɗayansu. Bappa ne da kanshi yace. "Ban fahimceki ba Shatu". Bredy dake gefenta ta gutsura kana ta dandola da zuman data sa Junainah ta kawo musu, a baki ta ɗansa ta tauna kana a nitse ta basu labarin abinda ta gani da kuma yadda taji, ta ƙara da cewa. "Bappa dama bakan Gizo a curi suke fitowa ne?". Cikin mamaki da al'hini yace. "Allahu al'alamu. Sai dai koma menene, lallai tabbas akwai abinda ke tunkarar rayuwarmu, fatana mu dage da addu'a koma menene Allah ya kawo mana shi kan al'khairi ya kuma sauƙaƙa manashi, zan kuma bincika in sha Allah. Sannan kada ku gayawa kowa mgnar nan". Ya karishe mgnar da kallon Junainah. Wannan labari ya sasu cikin dogon nazari. haka dai sukaci gaba hira kamar yadda suka saba. A can cikin yola kuwa, yau tunda Ya Jafar yaje sallan juma'a ya dawo baiga Ƙaninshi Sheykh ba, gaba ɗaya ya tashi hankalin ƙanenneshi da iyayenshi. Domin kama hannun Jalal yayi yana kuka, yana jan Jalal zuwa sashin Sheykh koda suka shiga, Jamil kuwa sashin mahaifinsu ya nufa. Ba tare da ya saurari Hadiman ba ya wuce. A babban falon ya samu , Abba Haurawa sama yayi yana shiga kuwa ya sameshi a falo shida jarabebboyar amaryar tasa cingom dinshi. Sai dai tana konce bisa kujera, Shi kuma yana zaune bisa sallayane ya fuskanci al'ƙibla, da ƙur'ani a gabanshi yana karatu cikin suratul Khafi. cikin rauni Jamil ya ƙaraso gabansa. Bai kulashiba har saida ya kai ƙarshen surar kana ya shafa addu'a. Cikin haɗe fuska da alamun faɗa yace. "Jamil lfy kuwa mehakan?". ido na zubda hawaye yace. "Abba Ya Jafa". Rai a hade yace. "To me zan mishi?". Cikin zubda hawaye yace. "Abba tunda aka dawo aka sauƙo sallan jumma'a fa yaketa kuka yana bin Jalal yana kuka alamun a kaishi wurin Hamma Jabeer, yau ko abinci baiciba, Aunty Juwairiyya ma sai kuka takeyi hakama su, Jiddah." Tsaki ya ɗan ja tare da cewa. "To ni zaka gayawa? Kaje ka gayawa Mamanku mana". Wasu sabbin hawayene suka zubowa Jamil a hankali ya juya ya fita". A can sashin Sheykh ya samesu, Juwairiyya da Jalal ɗin da Affan sun tasashi a gaba, Affan yanata kuma, shi kuwa Jalal sai tattaune laɓɓansa yakeyi, da sauri Jamil ya iso cikin sanyi yace. "Affan je ka gayawa Mama". Da sauri Affan ya juya har zai fita kuma ya dawo jin Juwairiyya na cewa. "No Affan kada kaje, ka gaya mata, nasan yanzu tana bacci ne". Shi kuwa Ya Jafar sai ya shiga ɗakin nan ya fito ya shiga wancan ya fito yana kuka kuma. Shigowar Abbane ya sasu su Jalal duka fita. A hankali Abba ya kamo hannunshi suma suka fito, da mamaki a fuskar Jamil ya bisu da ido. Shi kuwa Abba yana riƙe da hannun babban ɗan nashi suka wuce har makoncinsa, Gefen gado ya kontar da dashi, kana a hankali yake shafa kanshi cikin taushi da tausayawa yace. "Jafar kayi haƙuri kayi baccinka kabar kuka, Sheykh yana lfy lau, ya tafi ƙasar Saudia ne shida kakarku Sitti." Shiru yayi yana kallon mahaifin nashi. Shi kuwa Abba, kanshi yake shafawa yana kontar mishi hankali a take yayi baccinsa. Bayan sallan ishane Jamil yaje wurin Kakansun ya sanar mishi halin da ake ciki ya ƙafarsa cewa. "Allah rene, magar gsky kace Hamma Jabeer ya dawo, sabida abin ya Jafar yana tsananta in bayanan". Murmushi kakan nasu yayi tare da cewa. "Uhum ai Allah ya sauƙaƙa abinda zai taso Sheykh ya dawo ba tare da an gama dai-dai-ta abinda ya kaishi ba Dole shi wannan mai saɓulellen mondon Jalaluddin shi zai dena yawon iskanci ya zauna ya kula dashi tunda yafi kallonshi a madadin Sheykh". Cikin takaici Jamil yace. "To ni zan kai Ya Jafar saudia wurin Sheykh ɗin suci gaba da zama a can in sun so, tunda dai kun san Sheykh shine GARKUWAnmu". Cikin kontar da murya kakan nashi ya ɗan tausasashi kana yace in yaje ya turo mishi Jalal. A can Saudia kuma, sosai aketa shirya yadda ɗaurin Auren Sheykh da Jazrah zai kasance, duk da basu sanar mishiba, sabida kashedin da Sarki Jalaluddin da Nuruddeen sukayi musu dan ko yaushe in dai ana shirya batun aurenshi muddin yaji sai yaƙi fir yayi ta kaucewa dole a ƙarshe aure ya fasu, to wannan abunne yasa ba'a sanar mishiba. Sai dai yasan batun zuwan da Jazrah take sashinsu wai nune da ita suke zaɓa mishi in tayi mishi. To shi kuwa bayan gaisuwa ko sannu bai taɓa haɗasu da itaba. Haroon kuwa da Jannart sunata shirye-shiryen dawowa gida Nigeria. A garin Bani kuwa, Yau tun bayan sallan isha'i yaro ya shigo yace, Ya Salmanu yana sallama da Aysha, haka kuwa ta fita taje, Suka zauna a dakalin ƙofar gidan nasu suna hango yadda, Yara keta wasa a dandali domin ranar jumma'a tafi ko wacce rana a garesu wurin shanawa. Ya Gaini ne ya fito riƙe da hannun Junainah, a bakin ƙofar suka wuce Su Shatu Bayan sun gaisane ya wuce riƙe da hannun ƙanwar tasa, Murmushi Salmanu yayi tare da cewa. "Shatu, inaga dai aurenmu dana babban yaya rana ɗaya za'ayi shi". Murmushi itama tayi, tare da cewa. "Tab shifa har an kai kayan aure". Ido ya ɗan lumshe tare da cewa. "To ai in kin bani dama nima gobe-goben nan sai a kawo kayan aurenmu ko?". Da sauri tasa tafin hannunta ta rufe fuskarta, alamun jin kunya. Su Ya Gaini kuwa kai tsaye ƙofar gidan Ahaji Haro sukaje, A bakin ƙofar suka tsaya, sunkuyowa ya ɗanyi a hankali yace. "Yauwa ƙanwaliya maza shiga cikin gidan kicewa Addanki Bintu tazo". Cikin happy tace. To kana ta shiga cikin gidan da sallama. Kamar yadda gidansu yake hakama gidan Ahaji Haro duk suna zaune a tsakiyar gida da yaranshi da matanshi sunata hira, bayan ta gaidasune taje gefen Binto cikin raɗa ta gaya mata saƙon ƴaƴansu. Wani ɗan kekyawan matashi ɗan kimanin shekaru sha takwas mai sunan Junaidu ne ya kalli Junainah cikin tsananin so da ƙaunar yarinyar yayi murmushi tare da taɓa mamanshi cikin raɗa yace. "Inno ga surkarki in Allah ya yarda". dariya suka ɗan yi dan kowa yasan Junaidu yasan son da yakewa Junainah tun tana ƙaramar ta. Ita kuwa Junainah hannun Binto ta riƙo suka fito tare, Junaidu na biye dasu a baya, Koda suka fita, Gaini ne ya kalle Junaidu tare da cewa. "Yauwa Junaidu raka min Junainah gida ko". To yace kana yabi bayanta suna tafe suna

Table of Contents

Chapters

185 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182
  183. 183 Chapter 183
  184. 184 Chapter 184
  185. 185 Chapter 185
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});