Chapter 135
Chapter 135
zaran kin ɗan yi musu mgna da murya a sama to cewa sukeyi, wai kayi musu ihu". Ya ƙarishe mgnar yana kallon corridor fitowa falonshi. Murmushi Hibba tayi tare da cewa. "Ga baki ga tsoro". Aunty Juwairiyya ce ta nuna musu wurin zama tare da fara zuba musu abincin. Ita kuwa Shatu murmushi kawai ta ɗan yi, sai taji hawaye na neman cika mata ido. Zamansu hakan ya tuna mata yayunta, ko ina suke? Wani hali suke ciki? Ko ya jikin Ummeynta? Ya Junainah keyi da kewarsu. Ba ya Lado, Babu Ya Gaini, Babu Ya Seyo, babu Ya Giɗi, sannan nima an kawoni nan an cusani cikin wani irin bahagon gida mai wuyar ganewa". A hankali tasa tafin hannunta tana share hawayenta cikin hikima. Ɗan juyowa tayi ta kalli. Umaymah dake cemata. "Shatu, ga Jalal da Jamil tagwaye ne, sune ƙannen Sheykh Jabeer da suke binshi yanada wasu ƙannen Affan baya ƙasar. Sai Imran ɗan amaryar Hajia Mama mom. sai kuma yayunsu mata, kin san su ai ko? Rumaisa da Rumana". A hankali ta gyaɗa kai alamar eh. Ita kuwa Umaymah su Jalal ta kalla tare da cewa. "Ga Auntyn ku, matar Hammanku". Jamil ne ya ɗan yi dariya tare da cewa. "Allah ya ɗaiyiba". Murmushi sukayi tare da cewa. "Amin Amin." Nan dai sukaci sukasha kana suka dawo falon. Kamar jiya haka yauma suka wuni. Umaymah da Ummi na yawan yi mata dukkan bayanin komai na Side ɗinta. Washe gari ranar. Al'hamis, da yamma taja Hibba suka koma falonta. Cikin yin ƙasa da murya tace. "Yauwa Hibba sammin wayarki. Wallahi na nemi tawa har na gaji ban ganiba tun a Side ɗin Gimbiya Aminatu". Da sauri Hibba tace. "Dama kinada wayane? Kuma ya ɓata baki faɗawa Umaymah". Da sauri ta jawo hannun Hibba tare da cewa. "Ina zakije?." "Zanje in gayawa Umaymah mana". Ta bata amsa tana cire code ɗin wayarta-ta tare da miƙa matashi, da sauri tace. "A a ki bari ke dai bani aron taki bari in kira Bappa na". Ajiye mata wayar tayi bisa cinyarta kana ta wuce ta fita. Ita kuwa Shatu, da ido ta rakata, jin tana ta rabkawa Umaymah Kira tun kafin ta fita. Ajiyan zuciya ta sauƙe tare dasa hannun ta ɗauki wayar. Jujjuya wayar tayi tare da miƙewa ta nufi bedroom ɗinta. Number Bappa ta saka, kana kirashi. tare da kara wayar a kunne mugu ɗaya ana biyu, aka amsa kiran. Wani irin murmushi tayi jin muryar Junainah tana cewa. "Bappa! Bappa ga wayarka ana kiranka". Da sauri tace. "Ƙanwaliya". Cikin wani irin mamaki da jin daɗin Junainah tace. "Laaaaah Adda Shatu, kece? Ina kike? Adda Rafi'a tazo jiya wai tana neman wayarki baya shiga, Bappa yace mata ai anyi miki aure, taita kuka tace to ya batun karatunki, Bappa ma ya nemi number ki baya shiga. Ina kika ajiye wayar ne to Adda Shatu". Cikin sanyi tace. "Wayar ta ɓata ne Junainah". Cikin tura baki tace. "To mijinki ya saya miki mana". Ido ta lumshe tare da cewa. "Ina Ummey na? Ya jikinta?". Cikin sauri tace. "Ummey tana na Kitchen, yanzu jikinta da sauƙi tana mgna kaɗan-kaɗan, ko ɗazuma itace tace. "Bappa ya kira mata ke!." Cikin tsananin jin daɗi tace. "Alhamdulillah, kai mata wayar". Da sauri ya juya ta nufi kitchen tana cewa. "Ummey! Ummey ga Adda Shatuna". Da sauri Ummey ta fito, ta amshi wayar. Cikin murya mai cike da sanyi tace. "Aysha na!". "Wasu zafafan hawayene, suka zubo mata, Cikin rawan murya tace. "Na'am Ummey na! Ya jikinki?". Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa. "Jiki da sauƙi, Shatu yaushe zaki zo?". Bappa da yanzu ya iso daga rakiyar da yayiwa Rafi'a ne, yayi murmushi tare da cewa. "Bani wayar nan". A hankali cikin girmamawa ta miƙa mishi wayar. Shi kuwa amsa yayi tare da karawa a kunne. jin muryar bappa yanayi mata sallama ne yasata jin sabbin hawaye masu masifar ɗumi, sabida tausayinshi. Duk da tsufanshi mugayen ƙabilar ɓachama basu barshiba, sun kashe mishi babban ɗan shi. Kana sun tafi da uku, sun barshi cikin zulumin suna raye ne ko sun mutu? A ina suke? Me akayi musu? Me sukeyi? Sannan itama data rage anyi mata wani irin bahagon auren da yafi kama da na mulkin mallaka. Muryarsace ta katse mata mgnar zuci da takeyi da cewa. "Shatu kina Lfy ko?". Murya na rawa tace. "Lfy lau Bappa, amman bana jin daɗin gidan, ina kewarku, ya jikin Ummey na? Ya lbrinsu su Ya Gaini an samu wani lbrin ko har yanzu shiru? Ya Ba'ana bai muku komai bako? Ya tafi ne ko yana nan?". Murmushi yayi tare da cewa. "To Shatu wacce tamɓaya ɗaya zan amsa miki'. Tana kuka tace. "Duka". Cikin hikima da jinƙai irin na iyaye yace. "To sai kinyi shiru kin dena kuka". Da sauri tasa hannu ta share hawayenta tare da cewa. "Na bari". Taku biyu yayi zuwa uku kana yace mata. "Ba'ana bai mana komaiba! Ya gudu ya bar ƙasar ma baki ɗaya! Jikin Ummey ki da sauƙi sosai! Su ya Giɗi munata addu'a in Sha Allah, in Allah ya yarda zasu baiyana garemu da izinin ubangiji. Kafuran nan kuma mun rigada mun karya ƙarfi su yanzu bazasu sake samun damar cutar da muba, in Sha Allah munfi ƙarfi su." Sai kuma ya ɗan tsagaita jin, tana murmushi mai ɗan sauti alamun jin daɗi, a hankali yaci gaba da cewa. "Rafi'a tazo, nayi mata bayanin komai, kuma in ta dawo zata zo, in an barta zata shigo". Da sauri tace. "Zan gayawa Ummi ta sanarwa sarkin ƙofa in tazo a barta ta shigo". Cikin danne ainihin tarin ƙunar watsewar gidanshi yace. "Yauwa to haka zakiyi. Sannan in sunƙi yarda kada ki damu. Umarnine gareki, kibi dukkan umarnin mijinki, kiyi mishi biyayya a cikin dukkan lamuranshi nasan bazai saki mugun abuba, kada ki saɓawa umarninshi. Kada kiyi komai saida amincewarsa. Ki kasance mai kula da lamuran rayuwarsa kada ki bar wani abun cutarwa tare dashi. Yanzu shine gatanki. Shine madadin Giɗi, Ganin, Seyo, Lado, ƙannenshi mata ki kallesu tamkar Junainah, mahaifiyarshi ki kalleta kamar Ummeynki, yan uwan mahaifiyarshi ki kallesu kamar yadda kike kallon innarku, yanzu sune ƴan uwanki. Domin naki basa kusa Ki zama GARKUWAR sa". Shiru yayi jin kuka na son kubce mishi. Ita kuwa tuni hawaye na kwaranya daga cikin manyan idanunta. Cikin sanyi yace. "Gobe zamu tafi, lardinmu, zamu koma can na wani lokaci". Wani irin tsananin razana da tsoro ta zaro ido tare da cewa. "Bappa zaku tafi Kardi kuma!? Ni ku barni a nan ba kowa nawa!?". Cikin sanyi yace. "Zamu dawo Shatu. Donke zamu dawo. Dole muje, in sanarwa iyayen innarku abinda ya faru da ita da yaranta. In kuma gayawa yan uwana halin da nake ciki a kan ɓatan yayunki, bayan salla zamu dawo. Can zamuyi azumi. Bakiga yanzu a nan ko tinkiya ba'a bar manaba". Cikin gamsuwa da zancen Bappa ta ɗan danne shessheƙan kuka tare da cewa. "Allah ya kaiku lfy ya dawo daku lfy. Amman Bappa ku barmin Junainah mana, a kawo min ita mana in samu iƴar uwa kusa dani". Cikin tausasamata zuciya yace. "Kada ki damu, su nan bazasu barki da maraiciba. Sai mun dawo zan kawo miki Junainah da kaina". Kit kiran ya ƙatse sabida kuɗin sun ƙare.
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185