Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 130

Chapter 130

Garkuwa Book 1 Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

san yadda ake soyayya da magance matsalolin ta da tattalinta gudun ta lalaceba". Wani irin dariya mai sauti Haroon yayi tare sara mishi. Da sauri ya juya, da nufin tafiya, sai kuma yaga Umaymah na tsaye a gabanshi. Hannunta tasa ta kamo nashi tare da janshi suka fara tafiya. Cikin sanyi yace. "Oh Umaymah ina zamuje?". Haroon kuwa baki ya taɓe tare da cewa. "Wlh gobe zan koma in sha Allah, komai sai an nunawa mana ƴan ubanci". Dariya Umaymah tayi tare da cewa. "Allah kiyaye hanya". Da sauri yace. "To na fasa tafiya". Suna gab da fitane yace. "Umaymah sakeni karmu fita a haka". Juyowa tayi ta kalleshi tare da cewa. "To taho". To yace mata kana yabi bayanta. Suna tafiya cikin ƴar faffaɗan hanyar da bishiyoyin namijin gwanda yayi musu ƙawanya, shiyasa wurin yayi sanyi. A hankali ya kalleta lokacin da suka iso. Bakin ƙofar Gimbiya Aminatu. tare da cewa. "Umaymah me zanyi a ciki?". Hannunta tasa ta kamo nashi. Kawai ta kutsa kai ciki. Dole ya bita a baya. Yana saka ƙafarsa cikin falon yaji zuciyarshi ta buga, da ƙarfi, lokaci ɗaya ta fara harbawa da sauri-sauri. Cikin sanyi yace. "Umaymah barni a nan". Bata kulashi ba taci gaba da janshi tayi har bakin ƙofar falon Lamiɗo. wani irin rumtse idanunshi yayi yin yadda zuciyarshi ke barazar fashewa. Da sallama a bakinta, suka shiga. Yayinda Lamiɗo da Abbanshi suka amsa mata. Cikin wani irin azabebben bugun da zuciyarshi keyi, yasa ƙafarshi cikin falon. yayinda Umaymah ke riƙe da hannunshi tana mishi jagora har zuwa gaban Lamiɗo da Galadima da Abbanshi da kuma Malaminshi Malam Abubakar. Kana ta tsaya dashi kusa da Aysha tare da rusunawa. Yayinda shi kuma cikin fargabar yadda ƙirjinshi keyi ya rusa a hankali ya zauna bisa tattausan carpet ɗin dake shimfiɗe a wurin. Dib, dab, dib, dab, dib, dab. Haka zuciyarshi keyi. yayinda itama Aysha da bai lura da ita Bama haka zuciyarta keyi, sabida jin an mutun ya zauna kusa da ita. A hankali ya lumshe idonshi, sabida bugawar da zuciyoyinsu keyi a tare yasa, ƙarfin nashi bugun ya ɗan ragu kaɗan. Cikin nitsuwa ya kalli Abbanshi kanshi a sunkuye yace. "Barka da safiya Abba". Cikin kula yace. "Barka dai". Sai ya kuma kalli Malamin nashi cikin kamala yace. "Allah hokke sabbugo, Malam Barka da zuwa ya gida?". Cikin nitsuwa Dattijan yayi murmushi tare da cewa. "Alhamdulillah Sheykh Jabeer ya hidima". Alhamdulillah yace, kana ya kalli Lamiɗo da Galadima. sai kuma ya kauda kanshi. murmushi Galadima yayi tare da cewa. "Mu bazaka gaishemu ba kenan?". Ɗan tsuke fuskarsa yayi tare da cewa. "Gaggawa dai aikin shaiɗan ne". Murmushi Lamiɗo yayi sabida ya fahimci duk abinda zasuyi, sai ya cisu gyara ta kuma fuskar gsky. Galadima ne yace. "To ni bari in gaisheka Ina kwana". Kanshi ya jinina mishi tare da cewa. "Kayiwa kanka tanadin lada ashirin, a madadin kaɗan da zaka samu in ni na ɗaga maka gaisuwar. Lfyta lau Alhamdulillah." Ya ƙarishe mgnar da amsa gaisuwar. Dariya sukayi kana, ya kalli Lamiɗo a daƙile yace. "Ina sauri dan inada aikin yi, menene kasa aka jawoni nan". Ya ƙarishe mgnar a hankali yadda Abbanshi da Malaminshi bazasu jiba. Kana ya ɗan muskuta ya matsa gefe yayi nesa da Aysha sabida wani tsalle da yakeji zuciyarshi nayi, a madadin bugun da takeyi kafin ya zauna kusa da ita. Cikin zuba musu ido. Lamiɗo yayi murmushi sabida sunyi masifar dacewa da juna, shigarsu da ta zamo iri ɗaya tayi matuƙar yi musu kyau. Cikin wasa irin na kaka da jika yace. "Ga amaryar taka baku gaisaba, ku gaisa sai ka kaita kuje ka gabatar da ita". Fuskarshi a haɗe yace. "Hakan addinine ko al'ada?". Da sauri Galadima yace. "Al'adace kuma sai kayi ta". Ta gefen ido ya kalli Galadima tare da cewa. "Da ba Galadima za'a bakaba, da sarkin raya al'adu za'a baka". Shiru yayi jin Abbanshi na cewa. "Allah ya bamu nisan kwana, kaima watan watarana a gabanka yaranka zasuyi min haka Muhammad". Cikin yin ƙasa da kai cikin girmamawa da karrama mgnar mahaifin nashi yace. "Sun isa! Suyi maka haka in barsu". Murmushi Malam Abubakar yayi tare da cewa. "Kamar yadda ka isaba". Shiru yayi gane manufarsu. Jin duk sunyi shiru ne, yasashi ɗago kai ya kallesu. Suma shi suka zubawa ido, da sauri yayi ƙasa da kanshi. Ita kuwa Aysha shiru tayi tamkar ruwa ya cinyeta, tanajin yadda suke musayan kalamai. Sai dai bata fahimtarsu domin, tuno nata ahlin. Gyaran muryan da Abbansa yayine yasashi ɗago kai ya kalleshi. Cikin bada umarni Abba ya nuna mishi Aysha tare da cewa. "Kama hannunta kuje, ka gabatar da ita, ka fara daga sashin ƙannen Lamiɗo, sai na Mamanku, daga nan kuje wurin Gimbiya Saudatu, dama sauran matansu Babanku Nasiru". Bisa dole yace. "To kana ya yunƙa ya miƙa, da sauri Umaymah ta miƙe tazo ta miƙar da Aysha. kana ta kamo hannunta ta miƙa mishi alamun ya riƙe hannunta. Cikin tsuke fuskarsa da kwaɓeta tamkar zai ɗaura hannunshi a ka ya kurma ihu. Ya zuba mata ido. Muryar Abbanshi ce ta katse tsayuwar da yayi kamar an dashi. "Riƙe hannunta ku je". A hankali ya ware tafin hannunshi da Umaymah ta kamo kana lokacin guda yaji zuciyarshi tana tsalle da harbawa, kamar dai tana mararin wani abu. Hannun Aysha Umaymah tasa mishi cikin nashi tare da meda yatsunshi ta rumtsesu. Dam-daradam-dam haka zuciyarshi tayi wani masifeffen bugun mai kama da na aradu kana tafara wani irin tsalle. Ita kuwa Aysha, wani irin tsuma jikinta ya fara lokacin da taji tattausan yatsun hannunshi da fatar tafin hannunshi ya rumtse nata. Hannun wani irin masifeffen tsoro da kunyane suka diro mata, a lokaci guda. Shi kuwa Sheykh wani irin asirtace kuma ɓoyeyyen dogon ajiyan zuciya ya sauƙe mai sanyi, jin gaba ɗaya zuciyarshi ta koma ta nitsu tabar wannan tsinkewar da bugawar da tsalle tayi lib a cikin ƙirjinsa. Jin muryar Jakadiya ne yasa, Sheykh Jabeer, yin ƙarfin halin ɗaga ƙafarshi ta dama. Jin ya ɗan yi gabane yasa itama, ta ɗaga ƙafarta ta hagu, sai hakan ya bada wata dama ta musamman, ya zama suna ɗaga ƙafafuwan su, a tare kana suna taku a jere. Sai dai shi ɗin ya ɗan kereta kaɗan. "Masha Allah. Tabarakallah,". Sune kalaman da Umaymah ke Maimaitawa, lokacin da take biye dasu a baya. Lamiɗo da kanshi da Galadima sunga wani irin dacewa na musamman a tsakin Muhammad Jabeer da Aysha. Abba kuwa murmushi yakeyi mai baiyana jin daɗi. Malam kuwa, Addu'o'in yaketa jero musu na fatan al'khairi da zaman lafiya da nitsuwa da samun zuriya ɗayyiba. A hankali suke taku yayinda kowa zuciyarshi ke bin takun sawunsa, A haka suka fito babban falon Gimbiya Aminatu nan suka samu Ummi. Tana ganinsu ta miƙe da tsauri tayi gabansu, hadimai hudu cikin na Gimbiya Aminatu kuwa, sukayi bayan Umaymah dake bayansu. Shi kuwa Sheykh Jabeer suna fitowa yayi wani irin saurin sake hannunta tare da janye nashi, Sabida shi ji yake tsikar jikinsa na tashi tamkar ya riƙe wutan lantarki ne sabida masifar tsuma da yaki naman jikinsa nayi. Murmushi Umaymah tayi ganin still dai suna tafiya a jere a jere suna wani irin taku mai ƙayatarwa. Suna fitowa, suka samu sallama a bakin mashigar wurin. Nan ya shaida musu,

Table of Contents

Chapters

185 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182
  183. 183 Chapter 183
  184. 184 Chapter 184
  185. 185 Chapter 185
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});