Chapter 87
Chapter 87
amma ina bai yarda bah, ganin babu sarki sai Allah, yass Amriya ta ja gefe ta zauna tana kallon shi. dora musu Breakfast kabir yayi, bread & egg, sai kuma ya haɗa musu coslow daban tare da shayi mai kauri. Bayan ya gama haɗa Breakfast ɗin, sannan ya nufi dining da abincin, tare da serving ɗin su. Ganin plate na mutun ɗaya ne akan dining, yasa Amriya faɗin, " ina nawa? , Kabir ya bata amsa da faɗin, "gashi nan zamu ci tare". Girgiza kai Amriya tayi tace, " nidai A'a nawa nake so daban, murmushi Kabir yayi yace," toh zaki karba". tashi Amriya tayi daga kan kujerar da take kai, ta nufi gurin Kabir. Riƙe ta Kabir yayi sannan ya zaunar da ita akan ciyar sa tace, " ni zan baki a baki, kema kuma ki bani a baki okay . Murmushi Amriya ta saki sannan tace, " shikenen tom, ɗaukar chokali Kabir yayi da folk sannan ya chaki Bread din ya fara bata a baƙi, aka suka cigaba da ciyar da kansu har suka koshi. Bayan sun gama Amriya ta koma ɗaki sannan, ta bawa Hydar cerelak, bayan ta gama bashi abinci, sannan ta kaishi toilet sannan Kabir ya fara masa wanka, shikuws Hydar babu abin da yake yi sai wasa, farga lullube a fuskar sa. Bayan sun gama wanka, Amriya ta shafa masa mai tare da saka masa kaya, ta lallaba shi yayi barci. Kallon Amriya Kabir yayi yace, "kyakkyawar matata, yanzu saura mu ko, muje muyi wanka". Amriya tace, " toh kaje ka fara yin wankar mana". A'a bazan je ba, ki tawo mu tafi tare muyi wanka, rufe fuskar ta Amriya tayi cike da jin kunya tace, "ni bazan iya bah, kawai kaje kayi naka, nima sai nayi nawa" . Ba zato yaji ya ɗauke ta chakk, sannan ya nufi toilet da ita, shure _shure ta fara yi da kafar ta amma ina ta kasa ceton kanta. Saka ta yayi cikin baff na wankan sannan shima daga bisani ya fada ciki. Ni ko nace su madam Amriya saikun futo.... Fitowa suka yi cikin shigar su ta alfarma, sanye Amriya take da atamfa milk colour yaji stones da design, kayan ba karamin karbar ta yayi bah. Hannun ta kuma Hydar ne wanda yaji ke sanye da jeans da t-shirt,wanda suka masa kyau sosai. Kallon su Kabir yayi, wow my beautiful family, kinyi kyau sosai fah, kunsha kamshi. Murmushi Amriya tayi, sannan ta bude gaban mota ta shiga tace dashi, " ka shigo Mu tafi, nasan Ammi tana chan tana ta jiran mu". Shiga ciki Kabir yayi, sannan ya tada mota, suka bar harabar gidan, tun da suka fara tafiya babu abinda Kabir keyi sai satar kallon Amriya ganin tayi masa kyau sosai bah kaɗan ba. Aka ya ci gaba da satar kallon su babu kakkautawa. Ba zato suka haɗa ido da Amriya ta cikin madubi, ɗaga masa gira ɗaya Amriya tayi, tace Kalb yadai naga kana ta kallo na, hajiyan zuciya! Kabir yayi, sannan yace, "wai me yasa aka yi ki da kyau a kane, gaskiya ke makura ce a kyau, babu abin da kika rasa, gashi kin haifo min ɗa kyakyawa irin mu, gaskiya ni ɗan sa'a ne, Samun mace kamar ki yana da wuya". Murmushi Amriya tayi yayin da farin ciki ya lullube fuskar ta tace, "ina mai godiya a gare ka Kalb, kuma ina fatan mu dauwama a tare na ar abada". Riƙe hannun ta yayi gamm, tare da rungume shi a jikin sa har suka isa gidan Ammi. Isowar su gidan Ammi keda wuya, suka tarar da babu kowa a gidan, shiga ciki suka yi sallama rike a baki su, ganin ba'a amsa bah, yasa Kabir faɗin", kidai basua nan ne, toh amma ai sun san cewa zamu zo , bai kama ta ace zamu zo kuma mu tarar basua nan". Kallon koh ina na parlour Amriya tayi, sannan tace," ni kamar ina ɗan jin motsi kaɗan_kaɗan". Kabir yace,"kinga mudai na batawa kanmu lokaci, ki tawo mu tafi, tun da Ammi bata damu da ganin ɗanta bah, tsawon shekara guda kenen rabon da na haɗa idanuwa da ita, amma ba'a ba'a yi farin ciki da farfaɗo wa ta ba". Aba kalb!, ya zaka ce ba'a damu da kai ba, bayan kasan yadda Ammi take sonka fiye da nima da nake yarta, kuma..... Bata kaiga karasa wa ba, taga an haska parlourn da design da haske mai ɗaukar ido da hankali. Daga bayan su suka ji an ce, surprise!, welcome back son. Juya wa Kabir yayi, hatake ya haɗa ido dasu Ammi dasu Mami, sai kuma su Grandma dasu Doct habib gaba-daya kowannen su fuskokin su lullube yake da farin ciki da annashuwa. Murmushi Kabir yayi sannan yace,"wow! duk wannan bazatar sabo da nine akayi?, Ammi ta bashi amsa da cewa,"kwarai kuwa duk saboda kaine". Zuwa Kabir yayi inda Ammi take, sannan ya tsuguna tare da gaida ta, Albarka Ammi ta shiga sama sa. Daga bisani kuma, aka yanka cake wanda yake wajan tensteps. Sosai aka yi shagali, aka sha firar yaushe rabo, bayan kowa yaci yasha, Ammi ta kalli Amriya tace,"daughter kina lafiya dai koh?, fatan dai kina kula wa da mijin ki da kyau". Murmushi Amriya tayi tace," kwarai kuwa Ammi, baki ga daga jiya zuwa yau ba har yayi kiɓa, yayi fresh, sai kamshi yake buga wa, yau breakfast ma shi yayi mana". Taɓe fuska Kabir yayi sannan yace, " Ni banso sharri fah, Ni zan dora mace girki lallai, da saidai na karo mata kishiya". Dariya gaba daya suka kwashe dashi! gwanin burge wa, yayin da Nadira tace. Yahya a dai faɗi gaskiya fah, koda yake a bar kaza cikin gashin ta kada a fige ". Kabir yace toh a fige mana, ita kanta tasan bazan mata girki bah. Kallon sa Khalid yayi yace,"dade a dane da kake asalin Kabir dinka shine zamu yarda, amma yanzu koh me zaka ce ba zamu yarda bah. Sadiq yace, "Amriya ko dai kin bashi magani ne naga ya luma a kogin soyayyar ƙi". Kabir ya bashi amsa da faɗin, "A'a ka manta bita zai_zai ta bani na sha ". Ganin abin nasu ba zai kare ba yasa Ammi tace, "yanzu dai ba wannan bah, ina da good news da nake so na sanar muku, Amriya dai ƴata ce kamar yadda kuka sani, dan aka yanzu na samar mata da makarantar medicine, insha Allahu idsn ta gama, hospital ɗin ta yana nan a hajiye, mallakin ta". Masha Allah, gaba daya suka furta tare da fadin, gaskiya abin yayi sosai muma yanzu munada likita a gida cewar grandma. Saida suka kara ci suka sha, sannan su Kabir suka tashi, sannan yace musu zasu tafi akwai wani guri dasasu je. Ba yadda Ammi ta iya, aka ta rabu dasu suka tafi. Futar su keda wuya, shima doct Habib ya fuce daga gidan..... Tuka motar yake yi batare da jinkirtawa ba. Kallon sa Amriya tayi, sannan ta mintsini hannun sa, dan ƙaramin kara Kabir ya saki!, sannan yace, "Maman Hydar kodena da zafi fah". Ya fada tare da haɗe rai. Taɓe baki Amriya tayi tace, ɗazu naji kace zaka yi min kishiya koh, toh yau nisa kaine. Murmushi Kabir yayi, sannan yace, "aba Aljanar ruwa ta,
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89