Chapter 83
Chapter 83
ceta, toh zai lalace, kuma ina tunanin idan na fasa shi Amriya zata koma asalin mutum yadda take tun farko. Amma sai sai idan an kawo wannan zoben tukun an sanya mata. Babu shiri zuka ga Kabir yayi tsalle ya fada a ruwan. Hade hannayen su suka yi, inda suka soma yi masa adua, saida aka dau kusan thirty minutes fito bah, ganin aka yasa gaban kowanen su faduwa, inda Momsy ta zauna ta fara kuka tana mai fadin, "shikenen yanzu na rasa dana, na shiga uku ni Fatima, yanzu kenen Hydar ya zama maraya kenen". Ba zato suka ga gangan jikin sa yayo sama, ganin aka, yasa suka nufi inda yake da sauri, sannan su khalid suka fito dashi daga cikin ruwan. Gaban su ne ya fadi!, ganin ko motsi ba yayi, sannnan kuma gefen guda ya dun ƙule hannun shi, bude hannun Sadiq yayi, sannan taga zoben Amriya. Da sauri Sadiq ya dauki zoben sannan ya mikawa Aunty Amarya, karba Aunty Amarya tayi sannan ta nufi inda Amriya take, Danna masa ciki suka shiga yi, amma koh alamun motsi baiyi bah, ganin aka yasa hankalin su ya kara tashi. Saka wa Amriya zoben Aunty Amarya tayi, sannan ta dauko ƙwan wanda yake fari sall, sa'annan ta samu daidai kan Amriya ta fasa shi, tare da shafa mata shi duk jikin ta. Ganin bata motsa bah, yasa gaban Ammi ta fadi!, sannan tace kardai ƴata ta mutu!?, Aa insha Allahu babu abinda zai faru, ki kwantar da hankalin ki, cewar Aunty Amarya. Motsi suka ji daga cikin ruwa, waigawa suka yi, hatake idanuwan su ya sauka akan Mom, yayin da suka ga, an kwaƙule mata idanuwa sannan an cire mata kunne da hanci, gaba daya gawar ya zama abin tsoro, ihuu!, Zainab ta saka yayin da take kokarin guduwa, ta suɓule ta fada cikin ruwan, yayin da Aljanun ruwan suka janye ta ciki. Rintse idanuwan su gaba daya suka yi, yayin da gawar Mom ya zama abin tsoro, share hawayen ta, Ammi tayi tace,"yanzu duk izza da mugancin da kike takama dashi yana ina?, kalli yadda gawar ki ta zama wulakantanciya, yanzu gashi nan, kin mutu a wulakance, kin mutu ba tareda kin tuba bah, kin mutu ba tare da kin gyara kura kuran ki ba. Yanzu aga wanda ya kashe da wanda aka kashe, aga wa yake da riba ran gobe ƙiyama, tabbas Wanɗa da kika kashe, suke da riba. Dama ance karshen azzalumai bata yin kyau, indai mutum ya dade yana aikata zunubi bai nemi tuba ga Allah bah, toh irin abunda ke faruwa dasu kenen, mutuwa suke a wulakan ce. Ni na yafe miki duniya da lahira, saidai kije ki fuskan ci saka makon abunda kika aikata". Nufan inda gawar Doct Khadija yake, suka yi , tareda cinciɓar gawar suka saka s bayan Mota, Sannan suka cinciɓi Amriya da kuma Kabir suka suka su a mota. Tada mota suka yi, yayin da suka bar harabar dajin baki daya. Direct Asibity suka nufi dasu, yayin da aka shiga bawa su biyun taimakon gaggawa. Gefe guda kuma, suka koma gida, yayin da aka suturta doct Khadija, aka kaita gidan ta na gaskiya, sosai kowa yayi kuka game da mutuwar ta, su Mami da kuma doct Habeeb ma, mutuwar ta bah karamin girgiza su yayi bah, babu abinda kake ji sai koke- koke, saida sukayi mai isarsu, sannan aka dora da karatun Alqur'ani mai girma, aka shiga yi mata adu'oi. Koma wa Hospital din suka yi, yayin da Doct Habib ya zama shine special Doct wanda aka ware zai kula da Kabir da kuma Amriya. Saida likito ci suka dau kusan 3hours basu dawo da numfashin Kabir bah, amma an samu na Amriya ya dawo. Fitowa doct Habib yayi, yana sharfe zufa, ganin sa yasa gaba dayan su suka nufi inda yake, sannan suka ce ya jikin nasu?, Doct Habib ya basu amsa da cewa, "mun daiyi nasaran dawo da numfashin Amriya, amma. For Kabir, am sorry to say, ya fada doguwar suma, kuma a kalla zai kai kusan watanni koh shekara kafun ya far fado". What!, gaba daya suka fada. Baki na rawa Momsy tace kana nufin ɗana ya fada doguwar suma, girgiza mata kai Doct Habib yayi alamin eh. Innnalilahi wa inna hilaihi rajihun, la ila a ila anta suba'a naka inni kuntun mina zalumin. Abinda kowanen su ke nana tawa kenen. Hakuri doct Habib ya shiga basu, sannan yace "zaki iya zuwa ku duba lafiyan Amriya". Shi kenen Ammi ta fada, daga bisani suka shiga cikin ɗakin da Amriya ke ciki. Shiga ciki suka yi, suka tarar ta far fado, abunda ya fara fitowa daga bakin ta shine, ina Kabir?, Kwantar mata da hankali Ammi tayi, sannan tace, "Kabir dinki yana cikin koshin lafiya kinji, yanzu ba lokacin magana bane, ki kwantar ki huta kinji". Aa ni bazan kwantar da hankali na ba, ba tare da na ga Kabir bah, yana ina?, ku kaini inda yake dan Allah. Shikenen Amriya taso mu kaiki, mike wa tayi, hatake jiri ya dibe ta, saurin riƙe ta Aunty Amarya tayi, sannan tace,"kiyi a hankali zaki iya faduwa. Riƙe ta Aunty Amarya tayi sannan ta kaita dakin da Kabir yake. a daddafe Amriya ta karasa inda yake, sannan ta shafa fuskan shi tace, "gani nan na dawo gare ka, babu abinda ya same ni, kuma kaiwa ina fatan Babu abinda ya same ka". Dafa ta Ammi tayi tace, "kiyi hakuri Amriya, bazai iya magana bah, saboda ya fada a doguwar suma, taso mu tafi kada mu ta kura masa, hawaye ne ya fara bin kan kuncin Amriya tace, " kina nufin Mijina ya fada doguwar suma, me yasa bani ce na fada bah shi ya fada. Kiyi hakuri Amriya, ki taso mu futa. Cikin sheshekar kuka Amriya tace, " babu inda zani, zan zauna hanan har lokacin far fado warsa yayi. Da ƙyar suka samu suka shawo kan Amriya ta bisu suka fuce daga ɗakin, koma wa ɗakin da take tayi, sannan Ammi ɗauƙi Hydar ta bawa Amriya tace, "Amriya ɗan ki yana bukatar ki, ki bashi abinci. Karɓar sa Amriya tayi, sannan ta fara shayar dashi. BAYAN SHEKARA DAYA(1) COMMENTS & SHARE PLS 🙏🙏 ALKALAMIN ✍️ (Zinariyar 🪙 Jajirtattu) https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*?? (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ?asaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sau?i_.?? ----------------------------------------- Likitoci ne gaba daya suka fara kai kawo a Cikin Asibity. Yayin da suka fara shiga cikin emergency room, ririke shi gaba daya suka yi, yayin da yake shure _shure, sannan yake ƙoƙarin wafce kansa daga gare su, yayin da yake ta daman kiran sunan Amriya. Ɗaukar waya doct Habib yayi, sannan ya yi dialing number Dad, ringing biyu Dad ya dauka, tare da karawa a kunne shi yace, "hello Habib lafiya naga kiran ka?, doct Habib ya bashi amsa da fadin "Yahya Kabir ya farfaɗo daga doguwar suma". Zumbur Dad ya mike tsaye, sannan yace "kana nufin my son is back to life, ya farfaɗo, gani nan zuwa right away, kada ku bari yaje koh ina". Shikenen toh saika zo, yana kaiwa nan ya kashe wayan. Dad na kashe wayan ya nufi parlour da sauri, yayin da ya tarar da su Khalid
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89