Chapter 73
Chapter 73
dariya tace, bansani bah, bani ya Kama ta ku tsaga ku kalla bah, yanzu Kuje ku nemi inda Sabreena yarki take tukunan, Da sauri gabadayansu suka mike, yayin da su khalid suka samu suka daddaure Mom. Daga bisani suka fuce daga dak'in. Daukar Motoci sukayi, yayin da sukayi bribing din body guards din da su barsu su futa, ganin kudade yasa, yan kungiyan asirin bude musu kofa suka fuce daga gidan, Bayan fucewar su, Mom ta kunce kanta, sannan ta Kalli zoben Amriya da tayi nasaran zare shi daga hannun Kabir ta saki murmushi, daukar wayar ta tayi, ta kira Zainab, cikin kankanin lokaci zainab ta Iso gidan, yayin da Mom tayi mata rada a kunne, ni koh nace idan tayi tsami aji, daga bisani naga ta tattara gabadaya yan kungiyan, suka fuce daga gidan. Direct gidan Ammi suka nufa baki daya, yayin da masu gadi suka bude musu kofa, suka Shiga ciki, Futowa gabadaya sukayi daga cikin motocin, suka nufi cikin gidan. Shiga parlour sukayi, cikin rashin sa'a kuwa su kaga Amriya bata gidan, ta karda Salma ta gani akan table, dauka tayi Tareda mikawa Mami, karba Mami tayi sannan ta Fara karanta wa kamar aka. Assalamu alaiki Ammi, na rubuta wannan Sakon ne badan komai bah, saidan na gode miki akan abubuwa na alhery da kika aikata min, hakika kedin uwa ce ta gari, bansan da wane kalma zanyi amfani wajan gode miki bah, naso ace na sami irin ki amatsayin mahafiya, amma abunda Allah ya kaddara, babu wani Dan Adam da ya isa ya chanza shi, Dan aka ina godiya a gareku baki daya, ni zan tafi, zanje na cigaba da lallaba rayuwa ta, zanje na hafi danda ke cikina, a wani gurin daban, idan kuma lokacin mutuwa na yayi na mutu domin kuwa ina da tabbacin cewa tunda babu wannan zoben mutuwa zanyi, zanyi kewar ku baki daya, Dan Allah ki fadawa ahalin su Mom cewa ina matukar sonsu sosai, bazan taba mantawa da hallaci da kulawa da suka nuna min bah, ni na tafi kenen, bazaku Kara ganina bah ar abada, na koma duniya ta, duda sanin cewa ni ALJANAR RUWA CE, akan baisa kun gujeni bah, tabbas ku mutanen kirki ne, Kuma kiyi wa diyar ki Adua na sauka lafiya. nazo duniyar ku, na dandani dadin ta da Kuma rashin dadin ta, nasan yadda kuke mu'amala da mutane dakuma dabbobi, tabbas zanyi kewar ku sosai da Kuma duniyar ku, ina son ki Mika gaisuwa ta ga ahalin kalb, kice ina matukar sonsu, ban taba jin koda sau daya soyayya su ta zama kiyayya a zuciya ta bah. Ina fatan zaki karanta wannan sakon. Na barku lafiya. Zama gabadyaansu sukayi, yayin da gabadaya suka nemi kuka suka rasa. Rike kanshi Kabir yayi, yana ji kamar ya mari kanshi. Kallon Ammi yayi yace, kenen dama, Amriya tana da cikin dana bansani bah. Share hawayenta Ammi tayi tace, kwarai kuwa Tana da juna biyu, Kuma danka ne. ??♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀? Comment & share pls??? ALKALAMIN ?? AISHA M.B ??? (Baby isha) Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JYYV16dbYaX1dykLX7EE91 ?BISSMILLAHI RAHAMANI RAHIM? ALJANAR RUWA CE ??♀??? PAGE 5??1????5??2?? WRITTEN & DIRECTED ?? BY A'ISHA M.B?? ----------------------------------------- Amma wai shin meyasa baka son Amriya?, shin bata kai a sota bane?, meyasa a Koda yau she kana cikin kuntata mata, Kabir ya bata amsa da fadin, Ammi bawai sonta ne bana yi bah, kawai dan inada wata a raina ne shiyasa, Nadirah tace Amma yahya ita ce dai wacce kake so, wacce ta cece ka acikin teku, tabbas itace, Kuma wannan zoben na tane, bana kowa bah, so da dama tayi ?o?arin sanar dakai amma tsam baka fahimta, kuma yanzu saura wasu watanni ka?an kafin ta mutu,indai har bata samu wannan zoben bah, toh tabbas mutuwa zata yi. Zama kabir yayi, yana jin zuciyar sa na masa kuna da radadi, dafa zuciyar shi yayi,yana mai fadin, ba zata mutu ts barni bah, insha Allahu babu abunda zai faru da ita, na aikata kuskure, tabbas na aikata babban kuskure, dole na nemo tah, domin ce to rayuwar ?i, nima na yarda dana bada rayuwa ta,indai zan ceci taki rayuwar. Yana kaiwa nan ya fice daga parlour, su Sadiq na ganin akan,yasa suka bi bayan sa da sauri, shiga mota sukayi gaba-daya, yayin da "Kabeer ya tada mota, suka fice daga gidan. Saida su Kabeer, suka kewaye garin Abuja ba?i daya, amma basu ga Amriya bah. Kallon Kabir Sadiq yayi, yana mai fadin, Kabeer me zai hana muje gidan radio mu sanar da batan tah, Khalid ya ce, kwarai kuwa Kabir, maganar Sadiq gaskiya ce, ya kama ta muje gidan radio ka sanar da batar ta, tunda dai itadin matar kace. Shikenen Kabeer ya fada, tare da fadin muje gidan radion, bah bata lokaci suka nufi hanyar gidan radio. Cikin kankanin lokaci suka isa wajan, fitowa suka yi baki ?aya yayin da suka shiga wajan Gaisawa da mutane wajan suka yi, inda Kabir ke sanar musu cewa, wani muhimmin abune ya kawo su, Kuma suna bu?atar su sanar da mutane. Tashi ?an jaridan yayi, tare da bawa Kabir kujera ya zauna, zama Kabir ya yi, tare da ri?e speaker ya fara magana kamar aka. Assalamu alaikum jama'a wannan garin, barkan ku da wannan lokacin, fatan kowa na cikin koshin lafiya, sunana Kabir Muhammad yunusa, kamar yadda mutane suka sani, nine mai Company fishes production na Abuja, nazo wannan gidan radio ne badan komai bah,sai ?an na sanar da wata muhimmiyar magana, hana cigiyar wata budurwa wacce a kalla zata kai shekaru ashirin da haihuwa, kuma duk wanda yayi ?o?arin gano inda take yana da kyautar million ?aya, za'a buga hotunan ta yanzu kuma inason a ya?a, zan hajiye number na, duk wanda ya ganta sai ya kirani, 07045421451, wannan shine number na. Ina fatan za'a ganta. Kabeer na hajiye speaker,wata kira ta shigo wayar sa, cikin rawar jiki Kabir ya yi saurin ?aukan wayar, ?aga wa yayi, tare da fadin Hello!, daga ?ayan ?angare naji ance, shin ina magana da Kabir", Kabir ya bashi amsa da cewar, eh nine, waye akan layi? daga ?ayan ?angare akace sunana Sani, tambaya ce a ba?i na akan yasa na kira ka, bawai naga budurwar bah. Kabir yace, ina jin ka fada min, Sani yace, shin budurwar da kake nema itadin wacece a wajan kah?, mene ne ha?in ka da ita?, Murmushi Kabir yayi, yace zan fa?a muku wacece ita, kashe wayan yayi, ya saita ba?in sa dai-dai wajan speaker yace, itadin matata ce kuma kan wata, Kuma tabbas itadin rayuwa tace, idan har bangan ta bah, bana tunanin zan iya cigaba da kasan cewa a raye. Share hawaye da ke ?o?arin zubo masa yayi, yace tabbas nasan da cewa kina jina, na ro?eki, ki dawo rayuwa ta, ba zan taba iya rayuwa in babu ke. Kin yi min komai a rayuwa, inason nima na saka miki da abinda kika aikata a gareni, Amriya ki sani cewa ba iya sonki ka?ai nake bah, zan iya bada rayuwa ta, saboda ke da kuma ?ana na cikin ki, mahaifyar ki tana bukatar ki a kusa da ita, ki taimaka ki dawo, zamu nuna miki kulawa wacce ba?i ta?a tsammani bah. Ina fatan zaki dawo gare mu.. Yana kaiwa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89