Chapter 75
Chapter 75
banason ka dauko halin baban ka. Tana kaiwa nan ta jingina ajikin bishiyar tare da lumshe idonta........... Shin kai yanzu misali idan ka samu million ?aya, me zaka yi dashi?, dariya na kusa da shi yayi, sannan yace, kaii abubuwa da dama, farko zanje ne na biya kudin makarantun yaran na , sannan na siyi kayan abinci na gida , sauran kudaden da suka yi ragowa kuma, na dora wa kaina jari. Saurin dafa shi abokin nasa yayi yace, sani kaga mai na gani kuwa?, Sani ya bashi amsa da cewa, ni banga komai bah, menene ya faru? Nuna yatsan shi abokin nasa yayi, yayin da Sani yabi ?an yatsan nasa da ido, abunda ya gani ne yayi matu?ar bashi mamaki, dafa abokin sa Sani yayi yace, Wannan bah ita akace hana nema bah, wata ?aya daya wuce, tabbas babu makawa itace, Yanzu zan kira Sir Kabir na sanar masa,kaga mu kuma sai a bamu kyautar million ?aya. ?aukan wayar wacce take keypad yayi, tare da dialling number Kabir. Kabir dake kwance kan gado gaba-daya yayi wani iri, yayi sanyi bah kamar daba, ganin hana kira shi, yasa ya bi wayar da kallo, ganin sunan Sani ne bayyane akan screen din wayar sa, akai yasa shi jan tsaki, sannan ya koma ya kwanta... Wai me yasa mutumin nan baya ?aga wa ne , koh baya kusa da wayar tasa ne. Abokin nasa yace masa, ka kara kiran sa, wallahi million ?aya bah wasa bane. Cigaba da dialling number Kabir Sani yayi, yayin da Kabir koh takan wayar baibi bah, Inda a karshe ya kashe wayar gaba daya ... Kashhh!, wannan mutumin ya kashe wayar, kuma gata a gaban mu,kenen munaji, Muna gani, zamu tafi mubar ta, Sani yace, inada wata shawara, muje mu gwada jarrabawa koh Allah zai sa a dace. Nufan inda Amriya ke kwance suka yi, sallama rike a bakin su. Zumbur Amriya ta mi?e, cikin fargaba da tsoro!, kallon su tayi cikin tsorata tace, su waye ku?, me kuke nema?, shin akwai wani abu na kune a wajan nan?, Kallon ta Sani yayi yace, sannun ?i baiwar Allah, bamu zonan da nufin cutar dake bah, mun zone, domin jin matsalolin ki,menene sanadin da yasa kika kasance acikin wannan dajin?, me yasa ba zaki koma ga yan uwanki bah, Dan jimm Amriya tayi, sa'annan tace, babu komai, labari ne mai dogon zango, kudai kada kudamu dani, babu abunda zai same ni, kawai kuje kawai, a aka kaddara ta ta zomin, kuma a akan zan amshe ta. Sosai tausayi Amriya ya kama sani,da Kuma abokin sa Dini. Kallon ta sani yayi, tare da kallon kayan jikin ta, yaga duk sun yi kura sun yi datti sosai, ga ciki ta a gaba, wanda bazai wuce watanni bah. Cike da tausaya wa sani yace, Allah sarki baiwar Allah menene sunan ki?, kallon sa Amriya tayi, sannan tace sunana "AMRIYA". Toh Amili na, me zai hana kizo ki dunga zama a gida na, har zuwa sanda Allah zai sauke ki lafiya, sabo da naga alamun kina bukatar kulawa sosai, bai ka mata ki zauna hanan ba, kunji ke mace ce, ka mata ai ace ki kasance a inda yake da tsaro, domin ganin kyakkyawa irin ki, kan iyasa shedan ya rujayi zuciyar wani, sannan yazo gare ki da zimmar cutarwa. Haka ne, na gode sosai, bana bukata, banason ace na wahalar daku wajan daukan nauyi na, ku barni hanan kawai, inason ya kasance ni kadai ce, banason na kara shiga cikin jinsin bil adama. ???????????????? COMMENTS & SHARE PLS ?? ALKALAMIN ?? A'ISHA M.B ?? (baby Isha) Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JYYV16dbYaX1dykLX7EE91 ?BISSMILLAHI RAHMANI RAHIM? ALJANAR RUWA CE ??♀???♀?? PAGE 5??2????5??3?? WRITTEN & DIRECTED ?? BY A'ISHA M.B?? (baby Isha) ----------------------------------------- Kamar ya kenen? Jinsin bil adama kuma! Sani ya fada, tareda fadin gaskiya baiwar Allah maganar ki akwai alamar tambaya aciki. Murmushi Amriya tayi, tana mai fadin, shikenen nagode, zaku iya tafiya. Mutafi ina kenen? Mufa babu inda zamuje idan baki biyomu bah, cewar Dini. Ran Amriya ne ya soma baci, ganin babu alamun zazu tafi su barta a wajan, danne fushin ta tayi, sannan tace, kada kudamu dani, ni nasan yadda zan kulada kaina, basai na bukaci taimakon kowa bah, kawai kuje, ni nasan yadda zanji da al'amurana. mudai mince miki babu inda zamu, kafarki kafar mu. Cikin baccin rai Amriya ta daka musu tsawa!, wanda ya sanya jikin kowannen su ya fara bari, ?ura mata ido suka yi, yayin da suka ga kwayar idanuwanta na sauya launi . Ja da baya suka fara yi, inda Amriya ta maida kallon ta kansu tace, ba so kuke ku tunzurani bah, ku tawo toh, banzaye marasa tunani, wallahi idan kuka yi wasa saina kashe ku hatake a wajanan. Ha?a hannayen sa guri guda Sani yayi, sannan yace, dan Allah kiyi hakuri, bamuzo wajan ki da niyar cutar dake bah, ki taimaka ki rabu damu, na miki alkawarin koh keyar mu bazaki kara ganin bah, kinji dan Allah ki taimaka. Tausayin sune ya kama ta, binsu tayi da kallo, sa'annan tace, shikenen ku tafi, na rabu da ku, amma kada ku kuskure Ku fada wa kowa cewa kun ganni, idan kuka kuskure ku ka fada wa koda Kabir ne, toh nan gaba ku za'a aska a jarida cewa kun zama shekakku. Cike da tashin hankali Dini yace, na rantse da gyatuma ta laure, bazamu fa dawa kowa bah. Toh maza maza yanzu ku bace min daga gani. Amriya na kaiwa nan, su Sani sa R, wato suka saka gudu. Amriya na ganin sun tafi yasa ta bar wajan, inda ta cigaba da tafiya. Su Sani basu tsaya bah, saida suka ga sun shiga cikin mutane, ha?i kowanensu ya dinga yi, tare da saukar da hajiyan zuciya. Wayan Sani yaji tana ruri, ?aukan wayar yayi yaga sunan Sir Kabir rubuce akai. bai bari wayar ta katse bah yayi saurin ?aga wa, magana Kabir ke shirin yi, Sani ya riga shi da fadin, sir Kabir ina ka hajiye wayar ka, inata kiran ka. Daga dayan bangare Kabir yace, eh bana kusa da wayar ne, mene ne ya faru? naji kamar kana ta ha?i, badai abunda ya faru koh?, Sani ya bashi amsa da cewa, ai sir Kabir komai ya faru, yanzun nan, naga wannan budurwa da kake cigiya wajan wata ?aya daya wuce. Zumbur Kabir ya mi?e daga kan gado, tare da daukan car key , yanufi hanyar parlour da sauri, ganin Kabir cikin tashin hankali!, yasa su Aunty amarya dasu Grandma suka nufi inda yake. Kabir yace sani fada min inda kake yanzu zanzo, dan Allah kada ka bari ta kufce muku, ina zuwa yanzu, katuramin da address din wajan right away. Fada masa address dinda suke Sani yayi, Kabir yace gani nan zuwa yanzu nan, yana kawai nan ya katse wayar. Da sauri ya fara tafiya, koh kallo gaban sa bayayi saboda kidimewa da yi. Saurin shan gaban sa Sadiq yayi, tare da fadin, ina za kaje aka?, naga kamar hankalin ka a tashe, fada mana mene ne ya faru?, dafa kansa Kabir yayi, yana ms fadin, Sadiq dan Allah ka hajiye wadan nan tambayoyin a gefe, zanje wani guri ne, and is very urgent so please allow me
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89