Chapter 68
Chapter 68
saboda yusuf bah dan mu bane bah. Zaro ido Amriya tayi tace mee, kina nufin yusuf bah danku bane, toh wacece mahaifiyar sa? Ammi tace wallahi muma bamu sani bah, a bakin hanya muka tsince shi lokacin baya cikin hayyacin shi, baisan ciwon kansa bah, a lokacin muna fama da rashin haihuwa, sai Kuma Allah ya bayyana mana yusuf a matsayin da a garemu. Kuma a halin yanzu dole Mahaifyar sace kawai zata iya bashi jini. ---------------------- Kwan -Kwan -Kwan, su Khalid suka Shiga Kwankwasa kofan gidan, daya daga cikin masu tsaron gidan ne ya Mike tareda nufan hanyar gate din ya bude musu gidan. Kallon su Mai gadin yayi, ganin doct khadija ce yasa yayi Saurin wangale gate din, tareda gaisar da ita, amsawa Doct khadija tayi tace, shin mutanen gidan suna nan kuwa? Mai gadi ya bata amsa da fadin, wallahi gabadayan su, Sun futa, dansu ne bah lafiya, yanzu mah suna Chan babban asibity, Innalillahi wa innahilahi rajihun! Doct khadija tafada, babu dai abunda ya same shi koh, Mai gadi yace babu abunda yafaru, amma yana ga kamar hankalin ki ya tashi, cewar Mai gadi. Doct khadija tace babu komai shikenen, Kallon su Khalid tayi tace, ku tawo mu wuce asibity suna Chan, Tarar napep sukayi, yayin da suka Mai kwatan cen asibityn, direct Asibityn Mai napep ya nufa dasu, ba'a fi mintuna ashirin bah suka isa wajan. Futowa sukayi daga cikin napep din, yayin sadiq ya biyashi kudin sa. Shiga ciki sukayi, inda suka tarar da su Ammi a zazzaune, Amriya na ganin zu Khalid tayi saurin kauda Kanta gefe. Da sauri Doct khadija ta nufi inda Ammi ke Zaune. Ganin Doct khadija, yasa Ammi yinkurin mikewa, zaunar da ita Doct khadija tayi tace Aa kawata basai kin tashi bah, ya jikin nasa yanzu, Ammi tace da sauki, amma nurse tace dole yana bukatar karin jini Kuma Onegetive, in bah aka bah zai iya rasa rayuwar sa . Doct khadija tace jini na Onegetive ne, muje zan bada nawa jinin, Aa khadija you don't need to stress yourself, Doct khadija tace no Amina what are we friends for, na taimake ki, kema ki taimaka min, yusuf shima a matsayin dana yake , kinga bazan ga yana cikin magagin mutuwa Kuma naki taimakon sa. Tashi Doct khadija tayi tareda Shiga cikin room din, tareda Sanar da nurse din cewar zata bada jinin ta, Kwantar da ita akayi sannan aka zuki jinin ta, yayin da nurse din ta bawa Doct khadija Apple ta ci. Saida aka ibi wajan leda guda na jinin Doct khadija, sannan aka sanya wa Yusuf. Yin kurin tashi Doct khadija keyi, Nurse din ta dakatar da ita da fadin, Aa bai kama ta ki tashi bah yanzu, kina bukatar ki kwanta, ku huta, Doct khadija tace na ruga dana kwanta babu damuwa inason zanyi wani abu mai mahimman ci ne, Tana kaiwa nan ta fuce daga dakin. Su Amirya na gani ta suka isa Inda take, Ammi tace har kin bada jinin, Doct khadija ta bata amsa da cewar Eh na bada, godiya sosai Ammi tayi mata, yayinda Doct khadija tace babu godiya a tsakanin mu. Kallon Amriya Doct khadija tayi tace, Amriya muna bukatar taimakon ki, Kabeer yana cikin halin tsaka mai wuya, kuma da taimakon ki da taimakon Allah, zaki iya fidda shi daga wannan halin da ya shiga, Dan Allah Amriya kada kice baza ki je bah. Kallon ta Amriya tayi tace, bazan taba zuwa wannan gidan bah, na ruga na yi alkawarin bazan Kara sanya kafana a gida nan bah, kuma dalilin Kalb, bazai sa na karya alkawari na bah, Khalid yace, Amriya Dan Allah badan Halinsa bah ki taimaka mana, cikin fusata Amriya bazan jee bah, bana sonsa, bana kaunar ganin sa, kuma bazan taba taimaka masa bah, tun wuri kune mi inda dare yayi muku. Idan mah kuna tunani zanje gidan nan wai da sunan taimako, toh ku maida ita tatsuniya, domin kuwa bazan je bah. Sadiq yace amma fah Amriya, kabir zai iya rasa rayuwar da, idan baki taimaka masa bah. Amriya tace toh ni mene nawa, ai nauyi bah akaina yake bah, Allah ne sai bayarwa Kuma shine Mai karbe abarsa, Dan aka idan lokacin sa yayi Kaga saidai muce Allah ya jikan sa. ----------------------------------------- COMMENT & SHARE PLS ??? ALKALAMIN ?? AISHA MUHAMMAD BASHIR ??? (BABY ISHA) ?BISSMILLAHI RAHAMANI RAHIM ? ALJANAR RUWA CE ??♀??? PAGE 4??9????5??0?? WRITTEN & DIRECTED?? BY AISHA M.B?? ----------------------------------- Dan jimm Ammi tayi, tace Maganar ki hakane Amriya, amma da mutane zasu bi ta halin koh in kulan da ake nuna musu, koh irin rashin mutum cin da akayi musu, da babu Wanda zai Kara taimako a duniya, Dan aka baza kiyi wannan taimakon danshi bah, amma kisa a ranki cewar zaki taimake shine Dan Allah. Amriya tace hakane amma kuma na ruga danayi alkawari, kuma banason na kasance mai karya alkawari, domin kuwa karya alkawari ba abu bane mai kyau. Akane Amriya, amma Domin cetan Dan uwa, mu kan iya sadaukar da komai na mu, harda alkawarin mu domin cetan rayuwar sa daga cikin hatsari, nasan da cewar kin tsani kabeer, amma danne zuciyar ki zakiyi, kije ki cece shi, ke kanki zaki yi farin cikin cewar kema kin ceci rai daga mutuwa, kuma zakiyi tsanan da kike zai tafi, kije Insha Allah komai zaiyi sau?i. Amriya tace naji shikenen zanje, amma har abada tsanan da zai cigaba da kasance wa acikin zuciyata, domin kuwa Shida kansa ya dasa min tsanar sa a zuciya tah. Ku taso mutafi cewar Amriya. Murna sosai su Khalid sukayi ganin ta amince zata bisu. Mikewa Amriya tayi , tareda fucewa daga cikin reception din, su Doct khadija na ganin aka ,suka bi bayan ta da sauri, tarar musu napep sadiq yayi, tareda yiwa mai napep din ?watan cen gidan. Hawa napep din sukayi, basu suka isa gida bah, sai wajan la'asar. Futowa sukayi saga cikin napep din, yayin da sadiq ya biya mai napep din hakkin sa. ?arewa gidan kallo Amriya tayi, Tana mai fadin, ban taba jin koda sau ?aya nayi kewar gidan nan bah, Wanda nasan nayi kewar su a gidan nan sune, Aunty amarya, Dad, da Kuma Grandma. Doct khadija tace, Allah sarki Amriya suma yan gidan abunda yasa kika ga sun miki aka, saboda idanunwan su ya rufe ne basusan gaskiya bah, amma kinga yanzu, sun fahimce ki, kuma sun gane gaskiyar lamari , Sadiq yace kwarai kuwa, a lokacin bamusan menene gaskiya bah, amma yanzu mun gane gaskiya Kuma insha Allah zamu kiyaye gaba, Dan Allah ki tawo mu Shiga please, Ku shiga ciki zan biyo ku daga baya cewar Amriya, Khalid yace, kin tabbata zaki biyo mu, Amriya ta Bashi amsa da fadin kwarai kuwa zan biyo ku, Suna jin akan yasa kowannen su Shiga ciki, yayinda suka bar Amriya a wajan. Share hawayen dake shirin zubo mata tayi, Tana mai fadin, ban yi niyan zuwa gidan nan bah, amma zuciya ta baza ta iya juran ganin sa acikin wannan yanayin bah, dole ne na ceci rayuwar sa badan halin sa bah. Bangaren su Doct khadija kuwa, suna Shiga ciki suka tarar dasu, Grandma a zazzaune kowa na tofa albarkacin bakin sa akan Mom, Mamaki ne ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89