Chapter 44
Chapter 44
daga wajan kah, nuna saitin zuciyarta amriya tayi tace kasan yadda nakeji kuwa, jinake kamar na kashe kaina, Tana kaiwa nan ta fasheda kuka mai cin rai. Karo na farko a rayuwarsa dayaga amriya tabashi tausayi, rungumeta yayi kam jikin jikinshi yace, kiyi hkr, namiki alkawari bazan sake miki abunda bazaki ji dadi bah kinji. Dago kanta Tayi ta dora akan yatsansa, gabanta ne yayi mumunan faduwa, ganin babu zoben ta a hannunsa, cikin zuciyarta tace waiyyo Allah, zobena baya yatsan sa, yana wajan wa kenen, tunanin ta ne yatafi kan mom, tace tabbas wannan matar bazata bar kowa a Raye bah indai zobena yana wajanta, yakamata ace nakoma kafun ta aiwatar da mugun nufinta akan wannan ahalin , Kallonsa tayi tace Kalb, inaso mukoma gida, kabir yace kinaso mu koma gida karki damu gobe idan ma'aikatan dana tura zasuyi order na kaya suka kai saimutafi, amriya tace Aa Dan Allah yau mu koma, kaji, kabir yayi murmushin yake yayi yace Tom shikenen, Tareda sumbatar goshinta. Saitin tureshi tayi Jikinta yafara karkarwa, hankalin kabir bah karamin tashi yayi ganin halinda amriya tashiga, Ihuu ta kwallah, inda mutanen wajan suka zuba ido suna kallo, Bah abunda bakinta kefadi sai ruwa, dukanta yayi chakk yanufi cikin wajan da itah. Da sauri doct khadija ta juyo sannan tace, meya kawoki nan, murmushin mugunta mom tayi tace, abunda kike tunanin zai kawoni mana. Nazone na karbi memory daga wajanki ,yana ina, doct khadija tace, baya wajena kuma meyasa zan baki, Aba meyasa kika zama Mara imani aka, bazan kara aikata kuskure dana yi Ba abaya, har yau har gobe, saina tuna ranar dakika sani nayi kuskurenda bazan taba mantawa dashi bah. Ke wace iriyar muguwa ce, kin kashe mutane bah iyaka, kin raba da da mahaifyarsa, kin mayarda mutane bayinki, tabbas zakiyi danasanin abunda kikeyi, wlh wlh, wlh, Saikin yi dana sani, a lckn da aka zo zaran ranki, a lckn zaki San irin kuna da azabar da zare rai yake dashi. Hahahaha, mom ta kwashe da dariya Tana mai fadin kijira kinga abunda zai farudake tukun kafun kiyanke abunda zai farudani. Kallon sauran yan qungiyan tayi tace inason yanzunan ku kimin ita fadata, daya daga cikin mutanen yace angama shugaba.. Direct daki kabir yakaita tareda kwantar da ita akan gado, tareda dauko inhaler dinta yabata tashaka , babu bata lck tasamu nutsuwa, ajiyan zuciya yayi yace, na tambayeki, shin kinada aljanu ne koh shafar iska, Girgiza masa kai amriya tayi tace Aa, Toh meyasa, kike yawan faduwa, kamar wata mai aljanu, gsk abunan naki akwai lauje cikin nadi. Murmushi amriya Tayi cikin ranta tace Idan da kasan wahala da gwagwar mayar da nakesha wajan cetan rayuwarka da bazaka CE aka bah, tabbas yakamata, na koma sbd wannan azzalumar matar taruga tasaka wannan zoben , Kabir yace toh shikenen kishirya zamu koma yau, yana kaiwanan yafuce yabar mata guri. Yana futa amriya, ta Rike kanta wanda yake mugun saramata, tashi tayi a daddafe tanufi toilet. Chan cikin daji suka Shiga da doct khadija Inda yan qungiya suka taru , Daddaureta akayi ajikin bishiya Wanda yan qungiyan suke kiranta da bishiyar bishiyar azaba. Zama mom tayi, tace zan Kara tambayanki a Karo na karshe ina memory da bayanan nan suke, Doct khadija tace bansaniba muguwa azzaluma mara imani, mai bushashiyar zuciya, Allah ya wadaran wannan rayuwa taki, tabbas bakiji dadin rayuwa bah,. Kuma bazan Bari ki kara nasara akaina akaro na biyu bah. na rante da Allah saidai ki kasheni, amma bazan fada miki inda yake bah. Ran mom ne yayi kololuwar baci tace wato sbd kinga ban sakar miki azaba bah shiyasa kike baki koh, toh yanzu nan zan gama dake, idan yaso kya basu lbr achan. Daukan wuka mom tayi, tafara tsaga cikin doct khadija, wani irin azzababbiyar kara doct khadija tasaki, Zaki fadamin koh saina gama dake, hawaye ne yafara bin kuncinta inda jini keta malala abakinta da cikinta, tace Bazan fadaba, Kuma wlh, acikin yaranda kika bi kika mayardasu marayu, a lckn da basuji bah basugani bah, daya daga cikin su ita zata kawo karshenki, ki je kirubuta zakice nafada miki. Murmushi mom tayi tace ba yau nafarajin aka daga irinku bah, kindauka zan rabudake nee Dan kinfadamin aka, toh shikenen tunda bazaki futoda memory bah, toh kingaishesu idan kinje. Tana kaiwa nan ta soka mata wukan da karfi Chan cikinta har ya ratsa jikin bishiyar. Faduwa doct khadija tayi muttaciya Daga wukan tayi tace ina bukatar jinin jariri yanzu nan , angama shugaba, Akwaishe mun gawar wannan matar a jefa a cikin teku yadda kiyaye zasuyi abincin dare da namanta, angama shugaba. Hawaye ne yafara zuba a fuskan aunty amarya dake tsaye, cikin ranta tace tabbas matar nan shedaniyace, mara imani, wane sirri nee yake a memory, menene takeson doct khadija tabata, tabbas akwai lauje cikin nadi. Alhj usman ne yace ranki shi Dade, ga yata zainab tanaso ne tashiga qungiyan devilish, Kallonta mom tayi tace, yarka CE, Alhj usman yace Eh yata ce, zainab tace ranki shi Dade nima inaso nazama yar qungiya na sha'ara yadda babu Wanda zaimin na Kyale, Dariya mom ta kwasheda dashi tace karki damu indai zaki iya shan jini toh zaki zama yar qungiya, gobe ki hallarci taro, zaki zamo yar qungiya, kuma sannan dole ki sadaukar da abunda kika fiso, Zainab tace komai zan iya bayarwa indai har zan kasance a wannan qungiyar . Tashi mom tayi tace, yanzu kowa zai iya tafiya, yau karku manta kowa yasha jinin akuya, sbd jikina na bani akwai wani iftilahi dake shirin faruwa kwanan nan . Angama uwar shedanu, Watsewa kowa yayi daga wajan, inda aka dauki gawar doct khadija aka jefata a ruwa kamar yadda mom ta umarta. Shiryawa su kabir sukayi tsaff, inda suka Nufi Airport, Daukan Wayanshi sadiq yayi, yayi dialing number Nadira ringing biyu ta dauka, Tareda yin sallama, , amsawa yayi yace, my wife to be ykk, murmushi nadira tayi tace Lfy lau, kaifa, sadiq yace ina cikin koshin Lfy kamar yadda kike. Alhmd Nadira tafada, tana mai fadin wlh Nayi missing dinku yaushe zaku dawo, sadiq yace yau dinnan da yardar Allah. What, ta tashi a kwance datake tace are you for real, gsk naji dadi sosai, Shine Kuma baka gayamana bah, murmushi sadiq yayi yace, yanzu dai nafada miki kohh,. Tom shikenen Allah yadawo daku Lfy, sadiq ya amsa da ameen . Sadiq yace yanzu jirgi zaitashi, saimun Iso koh, Tom shikenen, ka kulamin da kanka, kabir yace insha Allah, kema ki kulanmun da kanki kinji. Tom Nadira tace, daganan sukayi sallama. Kashe wayan nadira tayi Tareda saukarda nannauyan ajiyan zuciya, Su Ummi dake Zaune suna Kallon ikon Allah Tace ohh wayaga su aunty nadira da soyayya, kamar bah da bah dakika mutuwar son yaya kabir. Yanzu Kuma Gashi, yaya sadiq zaki aura, inda Allah ke ikonsa kenen Murmushi Nadira tayi tace 馃挮馃挮馃挮馃挮馃挮馃挮馃挮馃挮 ----------------------- 馃挮馃挮馃挮馃挮馃挮馃挮馃挮馃挮 COMMENT & SHARE 馃檹馃檹馃檹 ALKALAMIN 馃枈锔忦煐婏笍馃枈锔? BABY ISHA 馃挒馃挒馃挒(AISHA M.B) 2/28/24, 22:09 - AISHA M.B (Baby isha): Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/IhGI6IqdpVVABEzyBe7LGM 馃鈥嶁檧锔忦煣溾€嶁檧锔忦煣溾€嶁檧锔忦煣溾€嶁檧锔忦煣溾€嶁檧锔忦煣溾€嶁檧锔忦煣溾€嶁檧锔忦煣溾€嶁檧锔? 馃寠馃寠馃寠馃寠馃寠馃寠 馃挒馃挒馃挒馃挒 馃尮Bissmillahi rahamani raheem馃尮 ALJANAR RUWA CE BOOK 2 馃鈥嶁檧锔忦煂婐煂? PAGE 3锔忊儯2锔忊儯鈴?3锔忊儯3锔忊儯 WRITTEN & DIRECTED馃枈锔忦煐婏笍馃枈锔? BY BABY ISHA 馃挒馃挒馃挒 ------------------------ Murmushi nadirah tayi tace Allah ya ruga daya kaddara cewa bani zan aureshibah, banice na dasawa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89