Chapter 58
Chapter 58
ki Bari zuciyar ki ta kaiki nesa, kada ki Bari shedan ya rin jaye ki, komai yayi farko zaiyi karshe, ma hakuri mawada ci, idan kikayi hakuri zaki dace. Amriya tace, hakuri na me, hakuri na nawa, wane hakuri ne nan banyi bah a wannan rayuwa, ya wulakan ta ni, yaci min mutunci, zagi ba dare bah rana, yace min kaskantaciya, Duka zagi Ba bu abunda baiyi bah. toh fadamin shin Nayi hakuri koh banyi bah, na tabbata da wata ce bani bah, wallahi saita iya kaishi ga hallaka.. kinga Dan aka yaje na bar masa zoben, Dama rayuwa tah bata da amfani, Kuma cikin kwanan na zan mutu, kamar yadda gumurzu ya fadamin. inaso zanga abunda zan haifa a duniya kafun Allah ya dauki raina. insha Allah babu abunda zai same ki cewar doct khadija, ta cigaba da fadin, kada kidamu, duda cewar Ahalin Muhammad sun tsane nii, saka makon sharrin da Karima ta min, amma akan bazai hana ni na je na bayyana musu gaskiya bah, dole Su san abunda Karima ta shuka. Karima tayi min abubuwa da Dama Mara misaltuwa. ta raba ni da yan uwana, ta rabani da yar uwata mafi soyuwa a gareni, ta kashe min dana, Wanda iya shi Allah ubangiji ya bani, ta sanya na raba da da mahaifiyar sa, ta kuntata wa rayuwa ta. tasa na aikata babban zunubi amma akan baisa ta rabu dani bah, dole ne na dauki mataki akan tah, shiru bazai yi magani bah, saidai abu ya Kara baci. Amriya tace, Dan Allah inason kikaini wajan mahaifiyata, inason zan ganta. Kallon ta doct khadija tayi tace, zan kaiki kamar yadda kika bukata amma yanzu lokacin kaiki baiyi bah, dole sai mun kashe wutar dake ci a gidan Muhammad kafun na kaiki, Amriya tace bazan karya rantsuwa ta bah, nice miki bazan sake dora kafana akan wannan gidan bah. murmushi doct khadija tayi tace, bazan ga laifin ki bah, saboda kina da hujja tayin akan, Kuma akan bazai sa naji bah dadi bah, Amriya tace zan cigaba da zama na a nan dajin har sai lokacin da zan sauka lafiya. Aa Amriya" bai kama ta ki zauna a nan bah, kama ta Ai ace kin samu gida, Wanda za'a dunga kula dake. ki tawo Tareda ni, zan kaiki gidan ka wata doct Amina, na tabbata zata kula dake harda abun cikin ki. Aa doct khadija, ki barni na cigaba da zama a nan shine zai fiye min sauk'i, saboda idan ina cikin jama'a, zan dunga jin zuciya tah na kuna, inaso na zauna ni kadai. Aa Amriya kiyi hakuri, ki tawo dani muje, Banaso na kaiki gida na, saboda har yanzu Karima bata San ina Raye bah, Kuma idan ta gano baza ta bar ni har ke bah, Dan aka ki tawo na kaiki gidan kawa ta Dan Allah. shikenen, zanje amma da sharadi, Doct khadija tace inaji ko menene ki fadamin . Amriya tace, zaki je gidan su Kalb, kamar mahaukaciya, Kuma sannan kice musu, mahaiyar Kalb Tana Raye, what doct khadija tace, Tana mai fadin kinsan ko me zanyi bazasu taba yarda bah, Amriya tace kawai kiyi abunda na fada miki . shikenen, Doct khadija ta fada, Tareda fadin, zanje Kuma zan fada musu. insha Allah gobe goben nan. ki taso muje gidan doct Amina,cewar doct khadija. Amriya tace, Aa ki Bari gobe. Tom shikenen, Allah ya kaimu goben..... Washe gari da sassafe Amriya da doct khadija suka wuce gidan doct Amina. Kwan kwasa gate din gidan sukayi, inda mai gadi ya bude musu Ganin doct khadija ce, yasa mai gadi ya bar su suka Shiga, yayi musu rakiya har wajan corridor din, parlour. Shiga ciki doct khadija tayi bakin ta rike da sallama. Kabir inason muyi wata magana mai mahimman ci da Kai, dago kai Kabir yayi ya dora idanuwansa akan mom yace mom inajin ki. mom ta cigaba da fadin, kasan wannan yarinyar kirkin wato zainab yar gidan Alhj usman, Kabir yace Eh nasan zainab, naga yarinyar Tana da tarbiya, Kuma tana da hankali, mezai hana ka aure ta domin d'aga darajar Ahalin mu. Dan jimmm, Kabir yayi, yace naji dadin wannan Shawarar mom, amma am sorry to say, i can't marry zainab, she's not my type. bata Kai tsarar da zanso tah bah. and mom as for me, inada wacce nake so, Kuma ni ban shirya yin wani aure bah yanzu gaskiya. Mom tace, shikenen Kabir, amma na Tambaye kah, shin tunda kake ka taba tambaya ta wani abu a duniyar nan, ban maka bah. Duk abunda kake bukata shi nake maka amma, shine bazaka iya cika min wannan muradi nawa bah, shikenen bakomai, zaka iya taciya. Dafe kansa kabir yayi yace, mom ki tambaye ni wani abu ko menene zanyi,.amma banda auren zainab. mom tace, auren zainab shine muradina, inason ka aure ta, Dan Allah, ta Fada tana hada hannayen ta guri guda. shikenen mom naji zan aure tah, cikeda farin cikin jin furucinsa, mom tace da gaske kake zaka aure ta. Kabir ya bata amsa da cewar da gaske nake zan aure tah, shikenen kinyi farin ciki koh, ya fada yana Murmushi, mom tace farin ciki mara misaltuwa mah. yanzu inason yau kaje ka ganta a gidan su, kaji, Tom mom naji, farin cikin ki shine farin ciki na, banason na ga bacin ranki kwata kwata, tashi yayi yace, zan tafi saina dawo, mom tace Allah ya dawo dakai lafiya. Kabir ya amsa da Ameen. Kallon su Nadira Kalisat tayi, tace, kuna Ganin abunda aka yiwa Amriya yayi Daidai kuwa, Meyasa za'a yanke mata irin wannan tsatsauwar hukuncin. Nadira tace, Meyasa ba za'a yanke mata bah, kokarin kashe mom fa tayi, Kuma ita ta kashe Ummi, kama ai ace an yanke mata hukuncin kisa. fatima tace kwarai kuwa, amma saboda yahya Kabir yaji tausayin ta yace tayi tafiyar ta, mu mun rike ta da hannu bibbiyu., bamu taba yin kurin kashe ta bah. kalisat tace dukkan ku, bakuda tunani , a ranar da abun ya faru,. naga mom da idanuna ta dauki ruwan dake kan dinning ta watsa wa Amriya. Nadira tace toh Dan Mom ta watsa mata ruwa mene akan yake nufi, kalisat tace mom ta Daidai tah lokacin da Amriya ta keson fadar wata magana. kinga akan yana nufin Mom tana da wani kulla kulla acikin ranta, Kuma akan yana nufin Amriya bah karya ta fada bah, gaskiya ne, Fatima tace Aba Kalisat, Meyasa bakida tunani nee, wannan abunda kike fada, babu hankalin da zai daukeshi, koda kin fada babu Wanda zai yarda saboda, Mom baza ta taba aikata abunda zai cutar da wannan Ahalin bah bare Kuma y'ay'an tah. Kalisat tace hakane, amma saina war ware abunda ya sanya kowa cikin duhu. Nadira tace oho Ke kika sani, kya yi kya gama, amma Duk abunda zaki yi, daga karshe Mom itace da gaskiya Ba Amriya bah. mikewa Kalisat tayi tace, aida yar uwarku ce bazakuBazakuce aka bah, amma kuma ni ina goyon bayanta, zan tsaya mata har sai inda karfina ya Kare, zan nuna mata cewar Tana yar uwa kuma wacce kuma zata tsaya mata tsayin daka, domin futo da gaskiya. Tana kaiwanan tayi fuce warta. ikon Allah doct khadija nake gani aka a gida na, murmushi doct khadija
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89