Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 86

Chapter 86

Aljanar ruwa Ce Book 1 Complete Hausa Novel 1,214 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Amriya tayi tace,menene Sabeen, ka kira ni Amriya ba Sabeen bah, ni banaso. toh shikenen gimbiya duk yadda kika ce aka za'a yi. Yanzu dai na dawo, ɗaga mata gira ɗaya yayi yace," yau dai za'a bani hakki na koh?. Shiiii, tayi mai alama da hannun ta da yayi shiru. Kallon sa tayi tace,"aba Kalb, kana gani fa Hydar baiyi bacci bah kuma nasan yaji abinda kace". Dariya Kabir yayi yace," my wife kenen, toh shi din babba ne da za'a ce ya fahimci abinda nace, shagwabe fuska Amriya tayi tace," Toh nidai nace A'a koh". Kallon ta Kabir yayi, yaga ta masa kyau sosai, janyo ta jikin sa yayi ta fada kan cinyar sa, yayin da kamshin turaren ta ya bugi hancin sa, lumshe idanuwa yayi, yayin da yake ji kamar kada ya sake ta. Kallon ta yayi yace," wai me su Ammi ke baki ne aka naga kinyi wani kiɓa kinyi kyau, ga wani fari da fresh da kika kara?, Murmushi Amriya tayi sannan ta kawar da kanta gefe tace," sirri ne". Murmushi yayi shikenen tunda ba zaki fada min bah, amma kinsan mene ne?, shafa sumar kansa Amriya tayi tace A'a saika fada, Kabir yace wallahi ina matukar sonki sosai, i want to stay with you for the rest of my life. Murmushi Amriya tayi tace," nima ina sonka sosai, ta fada tare da rungume shi. Rungume ta shima yayi, sannan ya sumbaci goshin ta. Ɗago kai Amriya tayi tace,"kasan me na tuna, A'a Kabir ya fada. Amriya tace," na tuna lokacin da kake yawan musguna mun, kana ce min mai sufar Aljanu. Ka tuna idan ka shigo ɗaki idan ina ciki sai kace, ke maza zoki futa dan bazan iya hada gado dake bah. Dariya Kabir yayi, sannan yace," Lokacin yarinta ke damuna, ban san gaskiya bane ai, a lokacin rayuwa nake cikin duhu. Yauwa na tambaye ki mana?, Shin har yanzu ke Aljanar ruwa ce, koh kuwa kin zama mutun kamar kowa. @@@@@@@@@@@@@@@@@@@@@@@@ COMMENTS & SHARE PLS ALKALAMIN A'ISHA M.B (Zinariyar Jajirtattu) https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*?? (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ?asaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sau?i_.?? BISSMILLAHI RAHMAN I RAHIM ALJANAR RUWA CE PAGE 57 TO 58 WRITTEN & DIRECTED BY A'ISHA M.B (Zinariyar Jajirtattu) --------------------------------------. Kallon shi Amriya tayi tace, "eh mana ni yanzu mutum ce kamar kowa, dan aka kar ka sake cikin Aljanar ruwa". Murmushi Kabir yayi sannan yace," tayaya zan yarda da akan eh". Ya fada tare da ɗaga mata hira ɗaya. Pillow dake kusa da ita Amriya ta dauka, tare da nufan sa dashi, ganin akan yasa Kabir saurin mike wa tareda ficewa daga ɗakin. Bin bayan sa Amriya tayi, yayin da suka fara zagaye palour, daga karshe tayi nasaran jefa masa pillow din a gadon bayan sa. Faɗuwa Kabir yayi kan three seater dake parlour ɗin, yayin da Amriya ta hau kansa, tare da ɗaukar pillow ta fara buga masa tana dariya. Waiyyoo baya na princess kiyi hakuri mana, zaki ɓallamin gadon baya, nayi alkawari bazan sake bah Dariya Amriya ta kwashe dashi!, tana mai faɗin," zaka kuma kirana Aljanar ruwa eh?, nace zaka kuma kirana Aljanar ruwa". Amsa Kabir ya bata da faɗin, "wane ni da zan kara kiran ki da Aljanar ruwa, da gaske nake ba zan kuma bah. Tashi Amriya tayi daga kan sa, yayin da ta mike tsaye ta saki murmushi. Tashi shima Kabir yayi zaune, sannan yabi Amriya da kallo ya dafa gadon bayan sa yace,"washh! baya na, gashinan zaki ɓallani tun ba'a kai koh ina bah, idan kika ɓallani yanzu taya zamu kara samun wani ɗan". Taɓe fuska Amriya tayi cikin zolaya tace," kai yanzu sai kace bah namiji bah". Murmushi Kabir yayi, sannan yasa hannu ya chafko ta, ba shiri ta fada jikin sa, yayin da numfashin kowanne su yana gogan na juna, kallon_kallo suka shiga yi a tsakanin su, murmushi Kabir yayi, sannan ya hura mata iskar bakin shi a fuskar ta. Lumshe idanuwan ta Amriya tayi, yayin da ta fara shiga wani irin yanayi na daban. Ba zato taji leben sa akan nata, sannan ya fara tsotsar leɓen ta cikin wani salo na daban. Da sauri Amriya ta cire bakin ta daga nasa, ganin yana shirin fita gayyaci sh, sannan ta mike tsaye take ƙoƙarin barin parlour, ganin akan da Kabir yayi, yasa shi janyo ta jikin sa. Ƙoƙarin kwace kanta take yi, amma ina akan ya cutura, ganin ya rungume ta kamm a jikin sa yayin da yake ta shakar kamshin turaren dake tashi a jikin ta, yasa ta faɗin," ka sake ni Kalb, karka maid ni ciki man". Ɗago ta yayi daga jikin sa, tare da zuba mata idanuwan sa masu ɗaukar hankali, yace ,"Amriya kunsan wani abu?, girgiza masa kai Amriya tayi tace,"Aa. Kabir yace, "wallahi ina matukar kaunar ki sosai, kiyi min alkawari ba zaki taba, tafiya ki barni ba, murmushi Amriya tayi, sannan ta shafa sajen kansa wanda suka kwanta suka yi luff tace," nayi maka alkawari bazan taba rabuwa dakai bah har sai numfashi na, na karshe a duniya. Murmushin jin dadi Kabir yayi! yace," Ni kuma insha Allahu zan yi ƙoƙarin wajan ganin cewa na baki hakkin ki a matsayin ki na matata uwar ƴaƴana, zan tarairaya ki tamkar kwai, zan kula da dake tamkar zinariya, zan tsaya tsayin daka domin ganin na kare ki kuma na biya miki bukatunki. Zan nuna miki soyayya tsantsa kawai batare da kiyayya bah. Na miki alkawari bazan kara bari wannan fuskar taki ta kara zubar da hawaye bah. Indai ina raye babu wani bakin ciki dazan bari ya kusanci inda kike, saidai idan bana wannan duniyar kaɗai wani abu zai same ki, amma indai ina nan toh fuskar ki bazata taba gushewa da murmushi da farin ciki bah. Murmushin farin ciki Amriya tayi, yayin da take jin kanta tamkar sarauniya, ringume shi tayi sannan tace," nima ina matuƙar son ka sosai Kalb, insha Allahu zanyi ƙoƙarin wajan ganin ban tauye maka hakkin ka bah na matsayin ka miji kuma uban ƴaƴa na". Alhamdulillah Kabir ya furta, sannan yace, yanzu muje kuyi sallah, sannan muyi wa Allah godiya koh. Girgiza masa kai Amriya tayi tace tom, tashi Kabir yayi sannan ya mika mata bayan sa yace, "maza hau na goya ki". Dariya Amriya tayi tace, " kana nufin goya ni zaka yi, aba dai sai kace wata yarinya". Kabir yace, " toh nidai a wajena ke komai ce dan aka maza hau mu tafi ɗakin . Murmushi Amriya tayi tace, "kamar bakai ne wannan Kabir ɗin ba mai shegen zafin rai da kuma zuciya". shagwabe fuska Kabir yayi yace, "nace miki kidai na tuna min abinda ya faru baya koh". Shi kenen kalb na daina cewar Amriya". Kabir yace, " yauwa koke fah, yanzu maza ki hau yau zamu yi abun. Kunya ce ta kama Amriya, daga bisani kuma ta ɗane bayan sa. Ɗaukar ta yayi a bayan sa sannan ya nufi ɗaki da ita.... Washe gari da sassafe, Amriya ta shiga kitchen domin samar musu da abin karyawa, ganin aka yasa Kabir hana ta, sannan yace shi zaiyi musu abincin Breakfast. Babu abinda Amriya bata ce mai bah, dan ya bar ta tayi Breakfast,

Table of Contents

Chapters

89 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});