Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 63

Chapter 63

Aljanar ruwa Ce Book 1 Complete Hausa Novel 1,214 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

toh shikenen, inajiran Duk wacce zaki kirawo, ina jira, Da sauri su, Aunty amarya da doct khadija, suka nufi hanyar waje. Tarar da su Sadiq sukayi a yashe cikin jini. Sosai su ke kuka, sun rasa yadda zasu sa rayuwarsu. Cinci barsu sukayi suka nufi part din Su nadira dasu, inda kowacce ta Fara kula da mijin ta. Kwantar da su Dad akayi, yayin da Aunty amarya ta Bawa Dad magani, yasha, bayan hour 3, jikin kowannen su ya lafa, yayinda su sadiq sun farka, kuma doct khadija tayi musu treatment, kowa aikinsu ya tashi, amma banda Kabir da haryanzu baiko Motsa bah. Hankalin su Khalid ne ya kara tashi, Dad yace Meyasa Haryanzu Kabir bai tashi bah, Dan Allah ku ceci rayuwansa, banason wani abu yasami d'ana, doct khadija tace, nayi iya bakin kokarina wajan ganin ya farka, amma babu alamun zai farka, ina tunanin fa ya fada a doguwar suma. Gaban kowannen su ne ya tashi, grandma tace khadija doguwar suma fah kika ce, yanzu menene mafuta. Dafe kanta Aunty amarya tayi, tana mai nazarin mafuta a garesu. Da sauri Aunty amarya da Dag'o, sa'anan tace, akwai mafuta, juyowa gabadayansu sukayi, suka hada baki wajan fadin, menene mafuta? Aunty amarya ta basu amsa da fadin, "Amriya", kwarai kuwa Amriya itace mafuta, zata iya, da taimakon ta, da taimakon Allah, zata iya cetan shi. Doct khadija tace da kyar Amriya ta yarda, tazo, saboda ta fadamin cewar bazata kara tako kafarta cikin wannan gidan bah, kuma yanzu bah karamin tsana tayi wa Kabir bah, da kyar mu iya shawo kanta tayi. Tazo, Khalid yace insha Allah zamu yi iya bakin kokarin mu, wajan ganin ta zo. balla kofa sukaji anyi. """"""""""""''''''''''''''''''''''"""""""""""""""""" Rasss gaban Amriya ya fadi ! , zuciyar ta, yafara Dukan uku uku, dafa ta doct Amina tayi tace, y'ata Amriya meyafaru? Amriya tace, Ammi", jikina yana bani cewar, ahalin dana baro suna cikin halin tsaka mai wuya, tundazu gabana yake ta faduwa, yusuf yace toh kije ki gani mana, ko kuma muje, Sai a lokacin Amriya ta tuna da irin cin mutuncin da suka mata. Amsa ta bawa yusuf da fadin, bazanje bah, na fasa, na ruga dana daukar wa kaina alkawarin bazan sake sanya kafafuwa na a wannan ahalin bah, dan aka, su nemar wa kansu mafuta, batareda taimakona bah. COMMENT & SHARE PLS. ALKALAMIN AISHA M.B Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JYYV16dbYaX1dykLX7EE91 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*?? (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ?asaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sau?i_.?? ALJANAR RUWA CE ??♀?? PAGE 4??7????4??8?? WRITTEN & DIRECTED?? BY AISHA M.B (BABY ISHA) ??? ---------------------------------------- cikin rashin fahimtar maganar Amriya Doct Amina tace, taimako Kuma! Wane taimako kike musu? Ganin aka yasa Amriya Saurin chanza magana da fadin, Aa Ammi kawai dai nafada ne cewar bazan Kara taimakon su bah, amma wasa nake babu wani abu. Rike hannunwan ta Ammi tayi tace Amriya kenen, yanzu kenen baki yarda dani bah, kinai tsoro ne? na ruga dana fada miki cewa ki dauke mu tamkar ahalin ki, ki daukeni tamkar mahaifiyar ki, ki fadamin gaskiya, Dan jimmm Amriya tayi, sa'anan tace ina tsoron bayyana muku wacece ni ne saboda, dalilin akan ne yasa wancan ahalin suka koreni, Kuma ina tsoron kada kuskure daya faru ya Kara maimai ta kansa. Kallon ta bban yusuf yayi, yana mai fadin, Aa y'ata babu abunda zai faru, ki shafa wa zuciyar ki ruwan sanyi, bazamu taba butul talki bah kinji, Gyaran murya Amriya tayi sa'anan tace, a gaskiya nidin bah mutum bace kamar yadda kukayi tsanmmani, nidin ALJANAR RUWA CE, Amma Dan Allah kuyi hakuri ban fada muku asalin wacece ni bah kafun na Fara zama daku a matsayin bakuwa, ni yanzu mah zan tafi, Kallon Ammi Amriya tayi tace, gaskiya Duk wacce ta sameki a matsayin uwa, toh tabbas bah karamar yar sa'a bace, rayuwata bah karamin kyau zaiyi bah, Ni yanzu zan tashi na tafi zanje na cigaba da lallaba rayuwata. Jin kalaman ta, yasa Jikin kowanne sune yayi sanyi, shafar fuskar ta Ammi tayi tace, Aa Amriya kada kidamu muna tare dake Duk rintsi Duk wuya, baza mu taba rabuwa dake bah, Sanin cewar ke bah mutum bace akan bazai sanya mu gujeki bah, koh kadan baki yi kalan wa enda suke cutarwa bah, Kuma nidin zan kulada ke tamkar yadda mahaifiya zata kuka da yarta . Ki sani mu dake gabadaya ahalin ne yanzu, kada ki kara bambamta kanki damu kinji, nima na rasa y'ata mafi soyuwa a gareni kamar dai yadda kema kika rasa mahaifiyar ki, dan aka yanzu kinzama y'ata tabbas kedin yar sa'a ce, na tabbata da mahaifiyar ki tana nan zata yi farin cikin ganin wannan d'iya tata wacce take tattare da sa'a da Kuma alkhairy, na tabbata a koda yaushe zata kasance tana Alfa'ari dake. Murmushi Amriya tayi sa'anan tace nagode sosai Ammi, hakika kedin mahaifiya ce ta kwarai, bazan taba mantawa da irin alkhairy da kika aikata a gareni bah, rungume ta Ammi tayi Tana Mai fadin Allah yayi miki albarka y'ata. Tura baki gaba Yusuf yayi Tareda cewar, wato yanzu Ammi kinsamu Auta, ni kuma za'a manta dani koh, murmushi Ammi tayi tace Yusuf kenen sarkin k'ishi toh kaima tawo na sama albarka, Tashi yayi ya nufi inda su Amriya ke Zaune, yana isa ya zauna a kusada Ammi yace, toh nima asaka min albarka, Tom shikenen yusuf Allah yayi maka albarka, Allah ya baka Mace ta gari wacce zata haifa min jikoki, Yusuf yace, Aba Ammi jikoki kuma tun yanzu, Abba yace, toh yusuf idan bakayi aure ka haifan mana jikoki bah, me kake so kayi, wai yaushe zaka futo da mata nee, Yusuf yace kada kadamu Abba nan bada dadewa bah insha Allah, Amriya tace Kardai ka dauko mana mumuna irin wannan budurwar taka dana gani. Kallon sa sukayi baki daya, Ammi tace Dama kanada wacce kakeso baka taba Sanar mana bah, Sosa k'eya yusuf yayi Tareda fadin, Hmmm Ammi fah karya Amirya takeyi, babu wata budurwar danake da. Amriya tace Bawani karyar da nayi, ai ranar nan na ganta, yusuf yace a ina kika ganta din? a awajan nan.. ganin Amriya na shirin tona masa asiri yasa yayi Saurin daukan pillow zai buge ta dashi, Amriya na ganin aka tayi Saurin mikewa tareda nufa hanyar daki da gudu, Ammi tace Kardai ka cutar min da d'iya, dan bazan kyale ka bah, Yusuf yace Kinaji fah Ammi wlh karya take min Abba yace mum yarda karya take amma kada ka Bari wannan watan ya Kare baka kawo mana suruka bah kaji na fada maka, Yusuf yace aba Abba wata daya fah, ina laifin shekara, yanzu ni ina zanje na samo budurwa na nawa maka cikin wata nan, Abba yace Oho duk inda Kaga yayi maka ka samo , mudai burin mu ka kawo ta mugan ta, inba aka bah da kaina zan aurar dakai. Shagwaba fuska yusuf yayi, yana mai fadin Ammi kinajin mijinki koh wai ni zai aurar, kenen auran dole za'a min. Ammi tace kwarai kuwa auren dole za muyi maka, danna ga idan bah auren dolen muka makaba, toh bazaka futo mana da suruka bah. Yusuf yace Tom shikenen zan futo da mata,

Table of Contents

Chapters

89 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});