Chapter 61
Chapter 61
fadan irin wannan magannanun, koh kunya baki ji bah, toh maza maza koh wa ya watse kafun na bata muku rai. Kwan kwasa kofan gidan, doct khadija tayi, tashi daya daga cikin body guard din yayi, yanufi wajan gate din Tareda bude kofan, ganin doct khadija ne, ya sashi yin sauri ya bude kofan. Shiga ciki doct khadija tayi, Ta Kalli koh ina na harabar gidan, sa'anan ta girgiza kanta tace, shekara da shekaru kenen, rabon da na dora kafana akan wannan gidan, wacce tayi sanadiyan barina gida nan, itace takuma yin sanadiyan dawowa ta, yau bah gobe bah, kowa zai San abunda kika shuka Karima. Chan cikin gidan ta nufa Tareda Kwankwasa kofan parlour, Aunty amarya tace Grandma kamar naji Hana Kwankwasa kofa, barana je na bude kofan. Bude kofan Aunty Amarya tayi, taga bakuwar fuska, gaisheta Aunty amarya tayi, doct khadija ta amsa , sannan doct khadija tace, Karima na nan kuwa?, Aunty amarya tace Eh Tana nan, shigo Shigowa ciki doct khadija tayi, kamar ance Mom ta juya , Juyowa Mom tayi ,lokaci daya suka hada ido da doct khadija. Gaban Mom ne yayi mumunan faduwa! , yayinda zuciyar ta ya fara Duka uku uku, Murmushi doct khadija tayi tace, kina mamaki ne, Kinga ban mutu bah koh, bakici galaba akaina bah, Cikin fusata, Dad yace meya dawo dake gidan nan, bayan bakin ciki da kuncin da kika sanya mu aciki, wato Kara dawowa kikayi domin ki kara, saka mu a wani kuncin kamar yadda kikayi shekarun baya da ya wuce. Maza zo ki futa, Bamua bukatar, ma Yaudariya, maciya amana, Grandma tace Muhammad barta tukunan, ni zanyi maganin ta Ke khadija, kalle ni nan, Kallon ta doct khadija tayi, Grandma tace kalle ni da kyau, baka nake bah fara nake bah, wato Kara dawowa kike, domin kikara haddasa wani fituna koh, toh ta Allah ba taki bah, baki isa kin kara yiwa wannan ahalin komai bah, Dan aka maza ki fuce, kafun na dauko tabarya, hawaye nee suka Fara saukowa daga kuncin doct khadija tace, bazan ga lafin ku bah, laifin wacce ta hada mu daku, zan gani, nazo gidanan ne badan komai, bah sai Dan na tona asirin abunda Baku sani bah, na tsawon shekara da shekaru, inason ku bani Dama, Dan Allah zan fada muku gaskiyar abunda ya faru, Kallon Dad doct khadija tayi tace, tabbas abunda Amriya ta fada muku gaskiya ne, babu karya, first wife dinka , wato Fatima Tana raye bata mutu bah, Kuma tana kulle ne acikin wannan gidan na tsawon shekaru, batareda ansani bah, Amriya ce kawai ta iya gano, inda Matarka take. Kallon ta Dad yayi, yace Dama wanda ya ruga ya rasu yana dawowa ne, wato zuwa kikayi domin ki cusa mun bakin ciki a zuciyata koh, leave now, banason jin komai dazai futo daga bakin ki. Doct khadija tace, zan tafi, amma bazan bar gidanan Ba Tareda na tona asirin wannan shedaniyar bah. COMMENT & SHARE PLS ALAKALAMIN AISHA M.B(BABY ISHA) BISSMILLAHI RAHAMANI RAHEEM. ALJANAR RUWA CE PAGE 46 ?47 WRITTEN & DIRECTED BY AISHA M.B (BABY ISHA) ----------------------------------------- Murmushin k'eta Mom tasaki sa'anan tace, Yanzu khadija wane laifi na aikata da kike son wargaza gidana, mene na aikata miki? Wane abu na tsare miki a rayuwar ki . Meyasa kike son ganin baya na ta karfi da yaji, Grandma tace, Karima ki rabudani ita, so take ta lalata miki aure, toh ta Allah na Tata bah, maza zoki futa kafun na sakar miki karnukan gidanan, suyi hawan gaba da ke. Wani kukan bakin ciki ne ya ziyarci Doctor Khadija, doct khadija tace, ku yarda dani wannan matar shedaniya. Mom tace DAD Kabeer Dan Allah ka roke ta, ta bar mana gida, saboda wannan matar munafuka ce. kece dai babbar munafuka!" sukaji kalisat tafada! ,ta cigaba da fadin kwarai kuwa, kece munafukar, Tsinka mata mari doct khadija tayi tace, Duk abunda zai faru, karki kuskure kikara ce mata munafuka, saboda a haifa ta haifi sama dake. Kuma itadin a matsayin mahaifiyar ki take. Allah ya kiyaye, Allah ya mun katangar karfe da wannan shedaniyar algunguma, mara imani. Wannan matar bata cancan ci akirata da Kalman uwa bah, domin kuwa yin akan kuskure ne. Dad yace, ke Kalisat," kinsan abunda kike fada kuwa, kina da hankali, bakisan cewar, Tana a matsayin mahaifiyar ki bane, ya karashe maganar ranshi a matukar bace kalisat tace, Dad am sorry to say", gaskiya, ita ba'a matsayin mahaiyata take bah, saboda mahaifiyata ta fita daraja da kima, kuma ita wannan azzaluma ce, mara zuciyar tausayi. Magannanun tane suka sauka akan dodon kunuwan Khalid dakuma su Kabir dake sauk'owa daga upstairs, bata hankara bah taji sauk'an mari akan kuncinta, Dafe kuncinta kalisat tayi, Idan ran Khalid ya Kai dubu toh ya baci, yace kalisat, kina cikin hayyacin ki kuwa, wacce ta raine mu, ta kula damu tamkar yaran ta, ta nuna mana soyayya kamar yadda itama Mami iya karkarin abunda zata iya kenen, shine yau kike kallon tsabagen Idanuwanta kina fada mata magana son ranki, kamar itadin sa'ar kice. Kalisat tace wallahi matar nan, bata son mu Illah son cutar da mu da take kokarin yi, Amriya ce kawai take dakatar da ita, amma na tunan ta gama da yahya kabeer ya kashe kowa na wannan family. Fashewa Mom tayi da kuka!, tace, Yau a gaban idona ake min karya cewar ina kokarin cutar da ahalin nan, meyasa zanyi muku aka, kalisat. Duda irin alkhairy da nayi muku amma da irin wannan abun zaku saka min dashi Dama ance Dan adam butulu ne, Hatake ta Fara tarin karya, tana zubda hawaye Hakuri su Kabir da Dad suka Shiga bata, cikin fusata Kabir ya nufi inda kalisat ke tsaye, Ba tareda bata lokaci bah ya fuzgo ta, sa'anan ya shake mata wuya yace, ke mahaifiyata sa'ar ki ce, wallahi Kuma idan wani abu yasami mahaifiyata saikin dandana kudarki, Murmushi kalisat tayi tace, mahaiyar ka, ko mahaifiya yar basaja, ta dolantar daku, tasaka ku cikin duhu, babu abunda idanuwan ku ke gani sai duhu, Amriya tayi kokarin fidda ku cikin aske, amma kuka ki ku fahimce tah. Da wacce kake Kira mahaiyar na sonka baza tayi kokarin cutar da rayuwar ka bah, idan akane meyasa ta kashe Ummi. Da sauri Kabir ya sake ta, ya dago da idanuwansa wanda suka kad'a sukayi ja. yace, what nonsense are you talking about. Kalisat tace am not saying nonsense, amma ni nasan tabbas Mom itace ta kashe Ummi, kuma sa'anan ta batar da Salma. Gabadaya suka hada Baki wajan fadin what! Dad yace toh menene hujjar ki na fadin akan, gayamin Wacece hujja. Nice hujja . Sukaji an fada, juyawar su keda wuya suka ga, Salma duk ta bi ta rame, tayi baki. Da sauri su nadira sukaje suka rungume ta, fashewa Salma tayi da matsanan cin kuka mai taba zuciya. Nadira tace, Salma Wacece tayi miki aka, ina kikaje cikin wadanan kwana kin, ba Tareda kin dawo bah, Salma tace babu inda naje, asali mah Mom ita ta bayar dani, ba Tareda kowa ya sani bah, kuma tabbas itace makashiya, wacce ta raba Ummi da rayuwar ta, saboda son kanta da son abun duniya. Dafa kanshi Kabir yayi Wanda yake mugun saramai, Kallon Mom wacce tayi zuru
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89