Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 85

Chapter 85

Aljanar ruwa Ce Book 1 Complete Hausa Novel 1,208 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

tayi fresh. Wani mugun kishi ne ya turnuke Kabir, cikin bacci rai ya nufi inda Yusuf yake, tare da karbar Hydar a hannun sa sannan yace," waya baka izinin taba yaro na, kada ka kara dora wannan karamin hannun naka akan ɗana. Mai da kallon sa yayi kan Amriya yace," Amriya da gaske ne kinyi wani Auren. Cikin radhin fshimta ta kalli su Dad, girgiza mata kai suka yi data ce eh. Murmushi Amriya tayi tace kwarai kuma, baka ga alama ba. Aure muka yi, tunda yanzu ka dawo saika saka mana albarka. Dad yace toh yanzu dai kaji, Amriya yanzu bah mallakin ka bace. Dan aka ka cire rai akan ta, Grandma tace yauwa kawa ta lubabatu tanada wata yarinya Saratu a kauye, naga zaku dace sosai, kuma gata bazawara, kaga dama ance zaurawa sunfi iya kula da miji, koh ya ka gani?. Bazai yuba, Wallahi bazan yarda bah, saikun kaini wajan limamin da ya daura auren nan, wallahi wannan bah adalci bane. Indai har da gaske anyi auren nan, toh wallahi saidai na dauwama a gauro, dan babu abinda zanyi da yar ƙauye kazamai. Kallon Amriya yayi yace, "Amriya dan Allah kiji tausayi na, ki fada min gaskiya". Kallon_kallo suka shiga yi a tsakanin su, hatare suka kwashe da dariya, sannan suka hada baki wajan fadin April fool. Kallon su Kabir yayi ya girgiza kai, sannan yace dama wasa kuke da hankali na koh. Janyo Salma Yusuf yayi yace,"toh nidai kaga matata uwar dakina, yanzu aka ma juna biyu gare ta. Hatake kunya ta kama Kabir, yaji kamar ya nutse kasa saboda kunya. Murmushi Amriya tayi, sannan ta nufi inda yake tare da rungume shi hawaye ya fara bin kan kunci ta. ganin aka yasa su Dad dasu Grandma suka bar musu parlour, yayin da shima Doct Habib yayi tafiyar sa... da sauri Kabir ya share mata hawayen ta sannan yace, "kuull kar na sake ganin kin zubda hawaye kinji. Girgiza masa kai Amriya tayi tace, nayi matukar kewar ka sosai Kabir, jin sunan nasa yayi wani iri a bakin ta, kallon ta yayi yace, menene wani Kabir, kice min Kalb kamar yadda kika saba a da. Murmushi gaba daya suka yi, kallon su Adeef Kabir yayi yace, me kuma kuke yi a gida?, baku koma makaranta bah?, Dariya Adeef da Ammar suka yi sannan suka ce, tsohon zance kenan, tun yaushe muka gama har mun samu ma aiki. What!, kuna nufin kun gama makaranta?, da yardar Ubangiji ma kuwa cewar Abdul. Gaskiya nee, toh su waɗanan fah, Kabir ya fada yana kallon su Mansy, oh wai su maryam kake nufi, ai matayen mu kenen. What!, wait a minute, kuna nufin ku ukun nan aure kukayi kuma a cikin shekara daya, Sosa keya Abdul yayi tace kwarai kuwa Aure muka yi, muma yanzu mun shiga saga ciki, sai ma kaga ranar auren mu, shagali iya shagali, anyi rawa na futa fitina, saima kaga photunan da mu kayi na buga wa a jarida. gaskiya babban Yahya kayi missing abubuwa da dama wallahi. Kabir yace toh taya kuka hadu dasu, Maryam din, danni dai nasan yan duniya ne, ana yahya ya kake cewa mata yanmu yan duniya , mun hadu dasu ne fah a nan Nigeria, kuma gashi sun chanza halayen su , sun koma ga Allah, dan Allah adens tono abinda ya ruga ya wuce. Shikenen Kabir ya fada, Adeef yace nidai Maryam itace matata, Ammar yace ni kuma zulaihat ce matata, Abdul ya janyo Kalisat yace toh Ni ma ga my wife nan. Murmushi Kabir yayi yace,"masha Allah, Allah ya kara hada kan zukatan mu, gaba-daya suka amsa da Ameen. Nadira ce tace Yahya kaga ƴarmu, karbar yarinyar Kabir yayi yace, "Masha Allah, ya sunan ta? , Nadira ta bashi Amsa da fadin sunan ta Safiya, wow nice name, gashi kuwa tayi kama da ke sosai har dogon bakin Baban ta. Turo baki Sadiq yayi yace,"kaji dashi". Miko Ɗan ta ita ma Fatima tayi tace,"ga shima ɗan gogon namu, ta fada tana kallon Khalid, harara Khalid ya galla mata, sannan yace zaki yi bayani ne idan muka shiga ɗaki. Dariya Kabir yayi tare da karbar yaron, sannan ya kalli Khalid yace, toh meza kayi wa kanwar yawa idan kunne ɗakin, kardai kana dukan mun kanwa. Khalid yace, " ita tasan abinda nake nufi". Maida kallon sa Kabir yayi yace, ta shi ma mene ne sunan sa?, Fatima ta bashi amsa da cewa sunan sa Zubairu amma hana ce masa Zubair. dariya Kabir kwashe da shi. tare da fadin wanene ya saka masa wannan sunan dan Allah, Fatima tace ba shine bah, nace a saka masa Abdullahi, sai yace min wai tun kafun yayi aure yace indai dansa na fari namiji ne wai Zubairu zai saka masa. Khalid yace,"toh nayi laifi ne, sunan kaka na wato mahaifin Baba na, shiyasa nace duk ɗanda na haifa indai na miji ne, saina saka masa zubairu. Gaskiya ne,gashi kuwa kuna kama harda katon kai naka. Khalid yace oho dai duk katon kaina bankai ka ba, naga ma kafi ni. Mika wa Fatima Zubair Kabir yayi, sannan ya mike tsaye yace, Ni zan je na dawo, inaso naje baki ɗimin mahafiyata. A'a ka bari mu fara cin abinci tukun nan saika je cewar Nadira, aka kuwa aka yi saida suka ci abinci, sannan suka yi sallah tare da yiwa Allah godiya daya kara nuna musu rana mai cike da farin ciki . Bayan sun idar, Kabir ya nufi part din Momsy shiga ɗakin Momsy yayi, ya tarar da ita akan kujera a zaune, zama kusa da ita yayi, tare da dora kansa akan kafadar ta yace," Momsy na, nayi kewar ki sosai, hade rai Momsy tayi tace, "ni banga alama bah","yanzu Amriya ta dawo gare ka ka manta dani koh, ta fada tana murmushi", Murmushi Kabir yayi yace,"kunsan menene Momsy, a duk sanda na ganki bana jin cewa ina tuna wa da ita, amma idan na ganta ke ce ke fadowa a raina". Murmushi Momsy tayi, tare da shafa kansa tace,"Allah yayi wa rayuwar ka Albarka ɗana. Maza kaje yanzu matar ka na bukatar ka, tsawon shekara daya leɓen, baka tare da ita, yanzu ya kamata ka fara nuna mata soyayya, kaji koh. Insha Allahu Momsy zan je, amma kuma kibari na zauna, sabo da kema nayi kewar ki sosai, hira sosai suka sha, abun gwanin burge wa, yayin da suna yi suna dariya. Ganin garin ya fara duhu yasa Kabir faɗin bara naje, nasan Hydar na chan domin kuwa shima yayi missing daddy sa. Mike wa yayi sannan yayi wa Momsy saida safe, daga bisani ya fuce daga ɗakin, zuwa yayi ya tarar gaba daya kowa ya koma part dinsa.Murmushi ya saki, daga bisani ya shiga cikin dakin su. Tarar da Amriya yayi da kan standing mirror a zaune, ta saka kayan barci, yayin da ta daure gashin ta wanda ya' yalalo ga tsantsi ga laushi. Zuwa yayi kusa da ita, sannan ya rungume ta, ta baya, tare da karbar Ribon din hannun ta sannan ya daure mata gashin ta dashi. Ɗaukar ta yayi chakk, sannan ya dire ta akan gado. Kallon sa Amriya tayi tace,"kyakyawan Mijina ya dawo gareni . Murmushi Kabir yayi yace,"my beloved wife Sabeen kenen. Ya mutse fuska

Table of Contents

Chapters

89 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});