Chapter 81
Chapter 81
dan darajar ma'aikin Allah, idan kina kaunar mahafin mu da gaske, toh dan Allah ki bamu zoben nan, dan Allah . Dan Allah ki bamu, we don't have much time, and we need to rescue Amriya's life. Dan jimm Mom tayi, kamar tana tunanin wani abu, lokaci daya kawai suka ga ta zari zoben ta mika wa Ammi", Da Kallon mamaki kowa ke binta dashi, ganin babu musu ta miko zoben, share hawayen ta Ammi tayi tace, kin yarda na karba?, Girgiza mata kai Mom tayi tace, kwarai kuwa na yarda, Amma da sharadi duk abinda na tambaye ku shi zaku bani, Mike wa Ammi tayi tace, munyi miki alƙawarin duk abinda kika ce kina so zamu baki, murmushin mugun ta Mom tayi, tare da fadin, tom shikenen ku karbi zoben ku tafi. Karbar zoben Ammi tayi daga hannun Mom, ta kalli Doct Khadija tace, yanzu a ina zamu fara neman Amriya "Khadija?, Doct Khadija ta bata amsa da fadin ba zai wuce guri daya bah, ni nasani wajan, inda muka fara haduwa da ita, hanan tace min burin ta, shine ta mutu a chan, yanzu ina da tabbacin cewa tana chan. Yusuf yace, Togo me muke jira, mu tafi kafun lokaci ya kure. Nufar hanyar waje gaba daya suka yi, yayin da kowannen su ya shiga mota, tare da tada motocin, suka fuce daga gidan..... Ana Karima, ta yaya zaki basu wannan zoben, meyasa zaki barsu su tafi?, cewar Zainab, amsa Mom ta bata da fadin, ni kadai nasan abinda nake shirya wa, ke an gaya miki cewa na yafe musu ne, ina sane na bada zoben, sobada abinda zan tambaya saiya ninka na zoben, ni bana ya fiya, fansa ce kawai take guda na a jini na. Maza-maza ku tashi gaba daya, nuni bayan su, mimmike wa gaba daya suka yi, yayin da suke jin jikin su na musu radadi.. Fucewa suka yi daga harabar gidan, sannan suka bi bayan su Kabir. Saida su Kabir suka dau tsawon lokaci suna tafiya, daga bisani kuma suka isa wajan. Koh gama parking baiyi bah, ya futo daga cikin motan, tare da kallon gaba daya jejin. Futowa suma suka yi gaba-daya, yayin da suka fara kalle _kalle, Koh zasu gano Amriya. Parking su Mom suka yi, yayin da suka laɓe a bayan bishiya, Kiran sunan ta suka shiga yi, amma suka ji shiru, cikin karfafa gwiwa, suka cigaba da kiran sunan ta batare da sun sare bah. Sheshekar kukan tane yaja hankulan su baki daya, waigawa su kayi, yayin da suka ga ta zauna a bakin Kogi tayi rufff da ciki. Kabir na ganin aka yayi saurin nufar inda take, karasa wa wajan ta suma su kayi. Zama kusa da ita yayi, tare da ɗago haɓar ta, zaro ido yayi ganin yadda idanuwan ta suka yi jajir duk sun Ku kumbura, uwa uba kuma ta rame tayi baki. Baki na rawa Kabir yace, mene ne ya same ki?, meyasa kika tafi kika barni?, shin kin san irin halin da na shiga da kika tafi, na shiga wani yanayi na kunci da bakin ciki, na roke ki kiya femin kurakurai na, bazan iya rayuwa ba babu ke. Dago kanta Amriya tayi hawaye na sauka kan kuncin ta, sannan ta dora idanuwan ta akan nass, daga bisani ta dauke kanta, tareda maida Kallon ta kan su Ammi. zuwa Ammi tayi kusa da ita, tareda tsugunnawa ta rungume Amriya, sannan ta fashe da kuka!", tana mai fadin, ki gafar ce ni ƴata, tsawon wadanan shekarun bansan cewa kina raye bah, tabbas ban miki adalci bah, na baki dama ki yanke hukunci daidai da laifin dana aikata miki. Rintse idanuwan ta Amriya tayi, yayin da take jin zuciyar ta na mata zugi da radadi, ɓanɓare jikin ta tayi daga na Ammi, Tare da mikewa tsaye, ta maida kallon ta kansu tace, mene ne ya kawo ku?, me kuke nema a gare ni?, Doct Khadija tace, Amriya mun zone domin mu baki zoben ki kada ki mutu, share hawayen ta Amriya tayi tace, shin nace muku ina bukata ne?, banaso ku rike shi a wajan ku, saida lokaci ya kure tukunan zaku kawo min zobe, Togo bana bukatar na cigaba da rayuwa, ku tafi ku kyale ni, Khalid yace, aba Amriya ke kinsan baza mu taba iya tafiya mu barki bah, ki taimaka ki karbi zoben nan, kafin lokaci ya kure. Tafi suka ji daga bayan su, juyawa gaba daya suka yi domin ganin waye, da mamakin su kuwa suka ga Mom rike da Hydar a hannun ta. Cikin baccin rai Ammi tace, Karima mene aka?, ya zaki dauki jaririn, dariya Mom da Zainab suka kwashe dashi!", sannan Mom tace, wannan yaron shi nake so, kamar yadda na fada idan zan baku zobe saina tambayi wani abu, toh jinin wannan yaron nake sonsha. Karya kike!",Amriya ta fada a tsawa ce!, Jinin ɗana bazai shawu bah, domin kuwa ɗaci gare shi, maza_maza ki bani yaro na, in bah aka bah na lahira sai ya fiki jin dadi. Dariya gaba daya yan qungiyan suka kwashe dashi, yayin Zainab tace, Togo zaki karbe shi mana idan zaki iya, kallon yan qungiyan Mom tayi sannan tace, maza yanzu nan ku kashe su gaba daya. Tana kaiwa nan, gaba dayan su suka yi kansu Kabir hannuwan su rike da wuka da takobi, Fada gaba-daya ne ya gauraye wajan, yayin da suka fara fada a tsakanin su ba gaggau tawa. Rintse idanuwan ta Amriya tayi, yayin da ta fasa wani kara!, wanda saida gaba daya dajin ya amsa. Sa'annan tayi amfani da karfin ikon ta, ta fara sama dasu daya bayan daya, tana wurgasu jikin manya_manyan duwatsuna da bishiya, hatake gaba daya kowanne su yake faduwa mutacce. Saida Amriya ta gama dasu tass yayin da ya rage saura Mom da kuma Zainab, ganin AMRIYA na yowa kansu yasa Mom ta cilla jaririn sama, zaro idanuwa gaba daya suka yi cikin tsoro, Amriya na gannin aka tsalle daya tayi ta chafko yaron. Kuka jaririn ya fashe dashi, rarrashin shi Amriya ta shiga yi, yayin da ta mikawa Salma jaririn. Ganin hankulan su nakan Amriya, yasa Mom yin saurin janyo Doct Khadija, sannan ta dora mata wuka a wuya tace, zan kashe ta idan baku bani jaririn nan bah. Maida kallon su suka yi kan Mom, zaro idanuwa suka yi ganin yadda ta dora wuka kan wuyar Doct Khadija, Haɗa hannun ta Amriya tayi, sannan tace dan Allah kada ki cutar da ita, na roke ki. Mom tace indai har bakua so na cutar da ita, toh ku bani wannan jaririn. Kallon su Doct Khadija tayi tace, Aa Amriya karku kuskure ku bata wannan yaron, ni na yarda na mutu, Amma karku bayar, . Zan yanka ta fa idan baku bani yaron nan bah, Cewar Mom. girgiza kai Amriya tayi tace A'a, Aa, karki kashe ta, Dariya Mom tayi tace toh ai shikenen, tana kaiwa nan ta yanka wuyan Doct Khadija. Aaaaaaaaaa!", Amriya ta saki wani razananniyar kara, wanda yasa hadari da walkiya wanzuwa, faduwa Doct Khadija tayi a wajan, kafin kace mee rai yayi halin sa... COMMENT & SHARE PLS🙏🙏 ALKALAMIN✍️ A'ISHA M.B💞💞💞 (Zinariyar 🪙 Jajirtattu) Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JYYV16dbYaX1dykLX7EE9https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89