Chapter 76
Chapter 76
to go. Kallon sa Sadiq yayi, sannan yace, wani wajan bashi da sunane, ka fada mana Kabir, meyasa kake kokarin boye abubuwa wanda ya shafi rayuwar ka, Takaici ne ya ishi Kabir, ganin Sadiq bai gifta daga inda yake bah, yasa shi fadin, Kirana Sani yayi, sannan yake sanar min cewa yaga Amriya, what! Gaba daya suka fada, yayin da Kowa ya mike, Doct Khadija tace, kana nufin anga Amriya, a ina aka ganta?, ya kama ta kuyi sauri kuje ku nemo ta, inbah aka bah, toh ina mai tabbatar muku da cewa, tana gano cewa mun san inda take toh na tabbata saita bar wajan. Yanzu bakuda ishashen lokaci, Kabir kuje, sannan ka dawo da matar ka cikin rayuwar ka. Kabir bai jira Doct Khadija ta inda magana da ya fuce da sauri, ganin akan yasa su Khalid da kuma Yusuf bin bayan sa. Mota gaba-daya suka shiga, yayin da Sadiq ya tada Mota, suka fuce daga gidan. Location din wajan suka fara bi, bai dauke su Lokaci bah suka samo address din wajan. Fitowa Kabir yayi daga mota ya hangi Sani a tsaye sai sharfe zufa yake. Da sauri ya isah wajan su Sani, Sani da gaba-daya hankali shi baya tattare dashi, ya hangi Kabir yana nufo inda suke. Ganin Kabir yasa shi saurin nufa wajan su, kallon sa Kabir yayi, sannan yace dashi tana ina?, ka kaini wajan ta, ina bukatar ganin ta, yanzu ka kaini wajan ta Please, ya karashe maganar hawaye na sauka kan kuncin sa. Tausayi Kabir ne ya kama kowannen su, kallon Kabir Sani yayi cikin tausaya, yace, ka kwantar da hankalin ka Sir Kabir, ina mai tabbatar maka da cewa babu inda taje, a wajan muka barota, dan aka, kasha fawa zuciyar ka ruwan sanyi. Yusuf ne ya kalli Sani sannan yace masa, toh me zai hana ka kaimu, kaga bamu da isashen lokaci. Kallon su Sani yayi yace, eh mana mezai hana na kaiku, amma mu fara maganar kudin da kuka ce za'a bawa duk wanda ya ganta, dole mu fara maganar kudin tukun nan, dago rinannun idanuwan sa wanda suka kada sukayi jajir, cikin muryar sa wanda ya ruga ya dashe saboda kuka yace, Ban taba rokan wani alfarma bah, amma yau zan roke ka, na roke ka Sani ka taimaka ka kaimu inda take, indai maganar ku?in ce ba kada matsala, zan ninka maka akan wannan million ?ayan, amma first thing shine ka fara kaimu inda take Please and please. Kin Kabir yace zai ninka ku?in akan nada yasa sani, fadin Tom shikenen tunda kace aka, ku biyoni, yana kaiwa nan ya fara tafiya. Kabir dasu Khalid naganin aka suka bi bayan sa, Duk inda Sani da abokin sa Dini suka yi nan suma su Kabir ke yi, saida suka yi tafiya mai nisa sosai, sannan Sani ya dakata. Kallon bishiyar da Amriya ke zaune dazu yayi yaga wayam bata nan. Hankalin Sani ne ya tashi ganin ba Amriya a wajan, zagaye bishiyar ya fara yi koh zai yi nasaran ganin Amriya, amma ina koh gizon tah bai ganin bah, Cike da takaici Sadiq yace, ka kaimu inda take mana, kazo nan sai faman zagaye bishiya kake, dafa Sadiq Kabir yayi, sannan yace Aa Sadiq kayi hakuri, kayi masa magana a hankali, Kallon mamaki Sadiq yabi kabor dashi, wai yau Kabir ke cewa ayi wa wani magana a hankali, tabbas ya yarda soyayya tana iya chanza mutum. Kallon su Sani yayi yace, kuyi hakuri ta ruga ta bar wajan, da hanan take amma yanzu bata nan, munyi rashin nasara. Dafa kansa Kabir yayi, yayin da yake ji jiri na diban sa, zama yayi a bakin bishiyar, tareda cewa why Amriya?, Why?, wannan azabtar War da kika min ya isa aka, dan Allah ki taimaka ki dawo gareni, bazan iya rayuwa bah babu ke, nayi dana sanin abubuwan dana dunga aikata miki a baya, nasan nayi kuskure, amma meyasa ba zaki bani last chance bah, me yasa zaki tafi ki barni cikin wannan halin, ya karashe maganar hawaye sabon kuncin sa. Tausayi sa ne ya kama su baki daya, tabbas babu abinda so ba zai iya yi bah, dafa shi Khalid yayi yace kayi hakuri Kabir ka taso mu tafi, ta riga data bar wajan nan, kaji ka taso mu tafi, in Allah ya yarda wata rana zata dawo gare ka. Girgiza kai Kabir yayi, yana mai fadin, ni babu inda zanje kawai ku tafi, ni bazan bar nan wajan ba, bah tareda naga Amriya da idanuwa na bah, kuma sannan ta furta cewa ta yafe mun bah, kuje kawai ni zan zauna a nan wajan, ya fa?a hawaye na sauka kan fuskar sa, Kallon sa Sadiq yayi yace, Aba Kabir, ba zai yu mu tafi mubar ka hanan wajan kai kadai bah, na fada maka cewa Allah zai bayyana tah, bansan cewa mace zata iya chanza ka bah kabir, ka kwantar da hankalin ka, koh so kake wani abu ya faru dakai, kana tunanin idan wani abu ya same ka zamu kasance a raye ne, Please kada ka kashe kanka da tunanin, ga hawaye mah kullum yanzu yazamar maka ruwan dare, Dan aka mun fauwalah wa Allah komai kaji, Murmushi wanda yafi kuka ciwo kabir yayi, sannan yace, duk abinda ya faru laifi na ne, da tun farko na aminta da Amriya mun zauna lafiya da ba'a kai ga taki haushi ba, har tazo kuma ta tsaneni. Kawai ku tafi, ku barni a nan, Inason na kasance hanan har sai lokacin da naji cewa ta dawo gareni, bazan bar wajan nan bah har sai lokacin da bayyanar ta zai zo. Kuje kawai, kubar ni hanan, nasan yadda zan lallaba na rayu a wajan nan. Cike da tausaya wa Yusuf yace, Allah sarki Kabir kayi hakuri ka tashi mu tafi, Allah ya ruga daya rubuta cewa abunda zai faru kenen, ka daina ganin laifin kanka, babu wanda yazo duniyar nan sannan yace bai taba laifi bah, so kaga Amriya zata dube ka da idon rahama kuma sannan ta yafe maka, kaji. Maza taso mu tafi, mikar da Kabir Yusuf yayi, inda Kabir ya soma tafiya, amma cikin rashin sa'a jiri ya dibe shi ya fadi a wajan sumamme. Hankalin su Sadiq ne ya tashi! ganin Kabir cikin mawuyacin halin, jijjigashi suka soma yi amma koh gizau baiyi ba, su Sani na ganin aka suka salallaba sannan suka harce. Cikin tashin hankali! suka Cincibi Kabir, sannan suka fara tafiya, saida suka kai bakin titin, sannan suka nufi wajan motar su, yayin da gefe guda idanuwan jama'a akansu, Dire Kabir suka yi acikin mota, sannan Sadiq ya tada mota suka bar wajan, basu nufi koh ina bah sai hospital. Direct reception suka shiga dashi, inda nurses suka bawa kabir gado, aka shigs emergency room dashi. Daukar wayar sa Khalid yayi, ya sanar da su Dad da kuma su Aunty amarya halin da ake ciki. Cikin kankanin lokaci, gabsdyaa family suka bayyana a wajan, fuskar Mommy mahaifyar Kabir ne yayi shabe shabe da hawaye, sannan tace, shidai dana tun da yazo duniya cikin fuskan tar kalubale yake, Allah ka kawo masa agaji, kwantar mata da hankali Dad ya shiga yi, . Kallon su Khalid Doct Khadija tayi,sannan tace mene ne ya faru a
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89