Chapter 79
Chapter 79
abubuwa da dama mara misaltuwa, ya Allah mai yafiya mai jinkan bayin sa, ina fatan ka dalmiyar da dauwamammiyar farin ciki a wajan wannan ahali biyu, ka basu hadin kai a tsakanin zuka tansu, kada ka hane su da komai, kamar yadda nima basu haneni da komai bah, ya Allah ka kara musu hadin kai da qaunan juna. Ina fatan rayuwar ku ta zama ingantacciya, Allah yasa rabuwar ku dani, itace alhkairy. NA TAFI, FATAN KUYI DOGUWAR RAYUWA. "BSALAM"........... Zama Ammi tayi, yayin da kuka yaci karfin ta, ta fashe da kuka, gaba dayan su, hawaye suke yi, yayin da suke jin tausayin Ammi da kuma Amriya na shigar su. Cikin sheshekar kuka Ammi tace, ki gafar cemu yata, ba laifin mu bane, ba muda niyar rabuwa dake, rabo ya rantse cewa ba damu zaki karashe rayuwar ki bah, danasan da cewa kina raye, da tuntuni na bayyana kaina a gare ki. Tana kaiwa nan ta kuma fashe wa da wani matsanancin kukan. Doct Khadija ce ta dafa ta, sannan ta ce, Amina yanzu bah kuka ne ya kama ki yi bah, kama ta ai ace muje mu fara neman zoben nan, sa'annan mu ceto Amriya daga shiga hallaka, in bah aka bah komai zai iya faruwa. Share hawayen ta Ammi tayi sannan tace, hakane, maganar ki gaskiya ce, ya kama ta muje gidan su Kabir yanzu nan, if not am going to loose my only one and beloved daughter. Mike wa tsaye tayi, tare da ɗaukar makullin mota, ta nufi hanyar waje da jaririn. Ganin aka da su Yusuf suka yi yasa su saurin bin bayan Ammi, Ammi na isar baƙin mota, ta bude kofar motan sannan ta hajiye jaririn, daga bisani ta nufi driver seat, ganin aka yasa Yusuf sauri. Karasa wa wajan yace, Ana Ammi, ya zaki tuka mota da kanki bayan kina da ni, Please ki koma back seat Ni zan tuka motan, jin aka yasa Ammi futowa daga cikin ta nufi back seat ta zauna. Shiga ciki baki ɗayan su suka yi, yayin da Yusuf ya tada motan, sannan masu gadi suka wa gale musu gate, suka bar harabar gidan. ------------------------------ Kwance yake akan kafadar ta, yayin da gefe guda tana shafa masa sumar kansa. Ɗaga kansa yayi ya kalle ta, sannan yace,Momsy bansan meyasa bah tun sanda kika dawo cikin rayuwa ta nake jin kaina so special, i really love you my momsy, murmushi tayi sannan tace, Kabir kenen, duk soyayyar da k min ba zata taba kaiwa nawa bah. tsawon shekaru kenen nake buri da fatan ganin ka, yanzu kuma ta dalilin Amriya, Allah ya dawo min dakai gareni, tabbas Amriya yarinya ce ta kwarai wacce koh wace mahafiya zata yi fatan samu irin ta. Duda cewar bah mutum bace, amma dabi'un ta, komai nata na mutane take yi, gaskiya Kabir kayi dacen mata. Hawaye Kabir yaji yana shirin zubo masa, da sauri ya share hawayen sa, sannan yace, hakane "momsy, tabbas nayi dace mata, amma a rashin sani da kuma rashin tausayi irin nawa, na kore ta, na yarda ni mugu ne, koda yaushe burina shine naga na kuntata mata, saboda tsananin tsana da tsangwama da nake mata. Da'ace yau tana a gaba na, toh da babu abunda zai hanani durkusa na bata hakuri, sannan na bayyana mata irin tsananin sonda nake mata. Kwan kwan kwan, suka ji hana bubuga kofa, tashi Kabir yayi ya nufi kofar parlour, tareda fadin waye?, bude kofan yayi, da wani irin sauri yaja da baya, ganin Mom da kuma yan qungiyar ta, sai kuma Zainab wacce tayi zuru_zuru kamar mayya. Ganin Mom ce da yan qungiyar ta, yasa Momsy kwalla wa Dad da kuma sauran yan gidan kira. Fitowa gaba dayan su suka yi, da mamakin su suka ga Mom da yan qungiyan ta. Alama Mom tayi wa yan qungiyar nata da fadin ku kama su, sannan duk ku daure su. Mom na idda magana, suka shiga yin abunda ta saka su, saida suka daure gaba dayan su, sannan suka rabu dasu, Kallon Mom Dad yayi yace, Karima me ya dawo dake kuma?, mene ne kike so?, koh har yanzu baki gama daukar fansar taki bah. Dariya Mom ta kwashe dashi, sannan tace, kwarai kuwa, da'a tunanin ku wannan tafiyar da nayi na tafi kenen bazan dawo bah, toh wannan tafiyar da nayi badan kowa nayi shi bah saidan ku, inaso naga na kashe gaba daya wannan ahalin sannan hankali na zai kwanta. Kuma a yau bah gobe bah, zan hallaka kowa na wannsn family, duk abinda nasan ya rabe ku, yaci sannan yasha daku, toh shima saiya bakun ci lahira. A fusace Grandma tace, toh me kike jira, ki aiwatar da abinda kika zo aiwatar wa mana, Ki kashe mu, idan kuwa baki kashe mu ba, ni da kaina zan shekeki, sannan na bawa karnuka gawar ki su cinye. A fusace Mom ta nufi inda Grandma take tare da shake mata wuya, kuka su nadira suka saka, suna ihuun taimako!, Kumin shiru, ta daka musu tsawa!, sannan tace, duk wata shegiyar data karamin kuka hanan, saina sadaukar da jinin ta wa qungiya, idan kuma kuna ganin karya nake, dan hallak ka fasa. Tana kaiwa nan ta maida Kallon ta kan Grandma, tareda fadin, ke dama wannan tsohuwar ke yaka mata na fara kashe wa, domin kin tsule min ido, wane irin kisa kike so na miki, shin na harbe ki da bindiga har lahira, ko kuwa na chaka miki wuka, koh na rataye ki, ko kuma na shake miki wuya har lahira. Grandma ta bata amsa da cewa, duk wanda kika zaba matsiyaciya, dama irin ku talauci ne ke janyo wa kuke shigs cikin qungiyan asiri, sannan ku dunga cin kuɗin haram, kudin da bata hanyar halal aka same ta bah. Nuna Mom Grandma tayi tace, ke Karima karki dauka zaki iya tsora tani da wannan bindigar wasar da kika rike a hannu, wallahi banki na kunce kaina nayi miki tsinaniyar duka bah, ko mene zaki fada baki isa kin tsora tani bah, saidai mah ni na tsorata ki. Dariya Mom ta kwashe dashi, ji kake, hahahahaha. Saida tayi mai isar ta, sannan tace, "nidin wai, tsoro, na rasa tsoron wa zanji saina tsohuwa, toh bara kiji har yanzu ba'a haifo wacce ta isa ta sakani na tsorata bah. Kallon ta Nadira tayi tace, karya kike, tabbas an haifo wacce ta isa sakaki tsoro harda firgici, domin kuwa Amriya daya ce tamkar dubu, kuma ita din ce zata kawo ƙarshen zalin cin ki, dama duk inda aka samu mugu, wanda yake takama da tsantsan zalunci, toh tabbas mai maganin shi yana bayyana. Kamar dai yadda itama Amriya itace zata yi maganin ki, domin kuwa babu inda zalinci yake dorewa, Amriya itace ajalin ki. Kamar hadin baki gaba dayan su suka ce, "kwarai kuwa, Amriya itace zata yi ajalin ki. COMMENT & SHARE plxx🙏🙏🙏 ALKALAMIN✍️ A'ISHA M.B💞💞💞 (Zinariyar 🪙 Jajirtattu) Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JYYV16dbYaX1dykLX7EE91 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ 🌹BISSMILLAHI RAHMANI RAHIM🌹 ALJANAR RUWA CE 🧜♀️🌊🌊 PAGE 5️⃣4️⃣▶️5️⃣5️⃣ WRITTEN & DIRECTED ✍️ BY AISH'A M.B💞 (Zinariyar 🪙 Jajirtattu)
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89