Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 53

Chapter 53

Aljanar ruwa Ce Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

daga bakin kii, sbd kin rainamin hankali shine zakice wai kece, toh duk wanda ya turo ki wajena domin ki zo ki yaudareni toh ki koma wajansa kice inji ni na ce hakan bazata taba faruwa bah impossible." "Dan Allah ka saurareni, ka saurari abunda zancemaka, a halin yanzu ma rayuwarka dana Hosanna tana cikin hatsari, dan Allah kabani zobena domin na ceci wannan ahalin." Kabir ya ce "A matsayinki nawa kenen? Ke wace? da zaki iya hana abunda zai faru, Kuma insha Allah babu wani abu dazai samu family nan, insha Allah duk wanda yake da mugun nufi akan wannan ahalin Allah ka mayar masa da niyarsa. wanda ba shine alkhairi bah agaremu. Ke a matsayinki nawa zaki ce zaki taimake mu?" Amriya ta ce," A matsayina na ALJANAR RUWA." Kallonta ya yi da sauritare da yi mata Kallon up and down, ya saki dariya saida yayi mai isarsa sannan yace "Ke ALJANAR RUWA, wow, Kuma kinaso na yarda dake." "Hmmm toh bara kiji wlh, kada mah ki fara fad'an haka sbd nidin nan babu abunda nafi tsana a duniyar nan sama da amin magana aljanar ruwa, banaso, dan haka maza kafucemin daga d'aki." Tashi Amriya tayi tana shirin nufan inda yake, dakatarda ita yayi da fa蓷in "Kada ki kuskure wallahi, maza leave my room or else, I will show you my true colour.." "Me yasa ba zaka yarda dani bane?" Ta k'arashe magana tare da fashewa da kuka. Jin ana bubbuga k'ofa yasa tayi Saurin share hawayenta, tareda nufa hanyar d'akin, ta murda handle din k'ofa, tare da bud'ewa, fatima ce tsaye hannunta rike da flask ta ce "Gashi inji Mom ta ce na kawo muku, na rana ne, Kuma na sanar miki cewar su Mami sun koma Lagos." "Toh" Amriya ta ce, Kallonta fatima tayi tace, "Amriya lafiya kuwa naga kamar kinyi kuka meyafaru?" Kabir dake cikin d'aki ya tashi tare da nufa hanyar waje inda ya bangaje amriya ya wuce. 'Daga ta fatima ta yi ta ce, "Sannu Amriya, menene aka yake faruwa ki fad'amin, yau Kuma wane laifi kika masa?" fashewa Amriya ta yi da matsancin kuka ta ce "Allah sarki babu komi wlh." Fatima ta ce "Toh amma me yasa kuke samun sa'bani kinga wlh Tunda su Docyor Amina da Aunty Amarya suka zo suka yi mana nasiha tun lckn nakeyi wa yaya Khalid biyayya. Kuma yanzu na koyawa kaina sonsa." "Toh yanzu damai zamuji ga mutuwar Ummi, ga batar Salma da haryanzu jami'ai nemanta suke amma ace mutum bazai fauwala Allah komai bah? Ki k'ok'arta ki Rike mijinki hannu bibbiyu." Kallonta Amriya ta yi tace "Tom insha Allah zan k'ok'arta, fatima dan Allah kinada abun rubutu.?" Fatima ta ce "Eh ina dashi me zakiyi?"Amriya ta ce, "Abu zan rubuta ne, ki aramun." Kallon kan table Fatima tayi ta ce "Yauwa ga wani bairo nan mah kinga saiki rubuta duk abunda kikeso." Wajan table din Fatima ta nufa tare da d'aukan bairo din ta mikawa Amriya, kar蓳a aAmirya tayi tare da yi mata godiya. Daga bisani fatima ta fuce daga d'akin. Hajiye flask din abincin Amriya tayi, tareda goge Hawayen dake shirin zubo mata akan kuncinta. Daki ta shige koh takan abincin bata bi bah, ta d'auki littafi, tafara rubutu. Sai wajan karfe Tara 9:0 clock na dare Kabir ya shigo, tarar da ita yayi a Zaune tayi tagumi, tana ganin shi ta mike tare da fad'in "Sannu da zuwa, abinci ka yana kan dining." Koh takanta baibi bah, yanufi toilet tare da yin wanka ya futo yafara shafamai inda suman jikinshi suka kwanta sukayi luff gwanin sha'awa . Bayan yagama shafa mai ya mike tsaye tareda nufa kan gado zai kwanta. Da sauri tace masa baka ci abinci bah fah, dan Allah kaci abinci kafun ka kwanta na safe mah baka ci bah yanzu bazaka ci bah." Kallon ta yayi ya ce, "Ina ruwanki cikin ki konawa? me yasa wai ke kinfiye nacin jaraba, wannan mata aka auramin koh annoba?" Banza kawai, kinga ki futo kifad'a idan saki kike bukata toh ko yanzu zan dambara miki shi, so please don't disturb my life. Ni zuwanki gidanan mah ba abunda yayi sai jawowa mutum mafisa da bala'i , banza kawai mai farar kafa." Kukane yaci karfin Amriya, hawaye mai zafi suka fara bin kuncinta, ta ce n"Ni 蓷in, ni ce mai farar kafa, nice masifa koh, Allah sarki, 蓷an Adam butulu ne." Bayan gwagwar maya da wahalar da nake sha a sanadiyan kawai domin na tseratar da rayuwarku, shine zaka cedani mai farar kafa, wannan wace iriyar rayuwa ce?" Dafa kanta ta yi wanda yake mugun saramata ta ce, "Tabbas na aikata kuskure, meyasa ban tsaya acikin ruwa bah ankashe ni? Meya futo dani ya Allah me yasa na ceci wannnan bawan Allah naka, meyasa banyi zamana bah?" Da nasan zan kasance a raye ne dan kawai naga wannan bakar ranar, da nasani na tsaya an kasheni." Kallonsa tayi tace "Ko dan ina zamane a gidanku yasa kake min irin wannan rashin mutuncin? kodan an aura min kai ba tareda nak'i bah, koh sbd Banida kowa nid'in marainiya ce yasa ka ke aibata ni kake zagina da zalunta tah yadda kakeso." Sosai jikin kabir yayi sanyi inda yaji tausayinta yayi mugun kamashi, tashi yayi yanufi inda take a zaune yace "Kiyi ha茩uri, kinji nasan na aikata kuskure Kuma hakan bazata sake maimaita kanta bah." Rungumeta yayi a jikinshi, inda itama ta rungumeshi, kallonta Kabir yayi yace yanzu kin yafemin, girgiza masa kai tayi tace "Eh, amma inason ka yarda da... " Shiiiiii yayi mata nuni da yatsanta. "please dan Allah kada kayi min zance d'azu abar maganan. Muje mu kwanta kohh, Yauwa kintuna min zamuje muyi alwala muyi sallah, yau ina son na sauke hakkin ki dake kaina. Koda yake mah ni na riga da nayi alwala sbd aka kije kiyi alwala." Rasss gaban Amriya yafad'i, hanjjin cikinta suka kad'a, ta ce, Kamar ya?" Kesta mata ido daya yayi yace aikin gane abunda nake nufi ko saina futo na baiyyana kije dan Allah." Mikewa Amriya tayi inda gabanta bai daina bugawa bah, shiga cikin toilet tayi, tace "Nashiga uku yanzu ya zanyi, so yake muyi mu amala na ma'aurata." "Taya hakan zai yiwu a matsayina na ALJANAR RUWA, shikuma BIL adama, wannan bazaiyuba, dole ne nasan yadda zanyi na kawar masa da hankali." Tap din ta kunna Tareda Dauro alwala, Tana gamawa Tafuto waje, Jikinta sanye da towel. Kallonsa tayi taga ya sauya shiga, cikin jallabiya yana kan sallaya yana lazumi, saka kaya tayi tareda daukan hijabinta, tace "Nagama ma." Tashi Kabir yayi inda, ya tada musu sallah, bayan sun idar da sallah, yayi musu addu'a, inda ya Rike goshinta yamusu aduan saduwa da iyayi. Shaketa tayi jikin bango, Hatake matar tafadi, inda Mom taja gashin kanta, Kara matar ta saki, yana mai fadin "Ki rabu dani, muguwa, mara imani, Me kikeso namiki, kin rabani da farinciki na, kin raba ni da d'ana, kusan shekaru 37. Kin azabtar dani son ranki kin kulle ni a wannan dakin wajan shekara da shekaru. toh meya ra ge, kawai ki kasheni na huta.." Dariya Mom ta kwashe da shi tace "Ke a tunaninki, narabaki da d'anki ne sbd kawai ina sonsa, toh barakiji, babu abunda nafi tsana

Table of Contents

Chapters

89 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});