Chapter 78
Chapter 78
ta fara yi, daga bisani sannan ta fara tafiya....... Saida tayi tafiya mai nisa sosai, sannan ta isa gidan Ammi, karewa gidan kallo tayi, race ga sabon duniyar ka nan, wannan gidan aciki zaka cigaba da rayuwa idan na tafi, rufe idanuwan ta tayi, hatake kamar walkiya ta bace batt.. Ba ta tsinci kanta a ko ina bah, sai Cikin gidan Ammi, parlour ta shiga batare da ta bari kowa ya ganta bah, hajiye yaron tayi, hawaye nabin kan kuncin ta. Sannan ta nufi kan drower, ta samu biro da kuma paper, tayi rubutu aciki sannan ta nan nada takardar, ta saka shi a jikin yaron, Kallon sa tayi yayin da kuka yaci karfin ta, sosai take kuka mai ratsa zuciya, saida tayi mai isar ta sannan, tace yau ganina dakai na ƙarshe kenen, ina fatan ka samu ingantacciyar rayuwa, ina fatan kayi tsawon rai a rayuwar ka. Tana kaiwa nan ta fuce daga gidan. Ficewar Amriya keda wuya, Ammi tajiyo kukan jariri a parlour, da sauri ta nufi hanyar parlour domin ganin wanene, Tsayawa tayi chakk, ganin jariri akan kujera ga takarda a gefen sa, kwallah wa abba kira tayi, sannan ta kwalla kiran doct Khadija, da kuma Yusuf, babu bata lokaci gaba daya suka hallara a parlour. Yusuf yace Ammi meya faru mukaji kin kwallah mana kira?, jiki a muce Ammi ta nuna jaririn da ɗan yatsarta, bin yatsar ta suka yi da kallo. Da mamakin su, suka ga jariri kwance akan kujera, sai faman kuka yake, gaban kowannen su ne ya fadi, yayin da kowa ya rasa ta cewa. Doct Khadija ce tayi karfin halin fadin, Wannan jaririn kuma daga ina?, tayaya ya shigo gidan nan?, kuma meyasa aka kawo shi nan gidan?, tambaya data shiga yi kenan. A tsora ce Ammi ta kara sa inda jaririn yake, tare da kurawa jaririn kallo, hatake gaban ta ya fadi!, jikin ta ya fara bari, baki na rawa tace, kuzo ku ganshi, Karasa wa su Doct Khadija sukayi wajan, yayin da gaba daya suka dora idanuwan su akan jaririn, gaban su ne ya bada wani sauti, yayinda zuciyoyin su ya fara duka uku -uku. Baki na rawa Yusuf yace, wannan yaron baku ga yana mugun kama da Kabir bah, Doct Khadija tace, kamar mah harta ɓaci, Ammi tace idan hakane kenan wannan dan yata Amriya ne, kenen akan yana nufin tazo gidan nan, share hawayen ta tayi, sannan ta dauki jaririn tace, such a cute and handsome baby, tabbas kayo kyan mahafiyar ka, domin kuwa kyakyawa irin tace zata iya haifo kyakyawa yaro kamar kai, because itadin makura ce a kyau. Yanzu kaidin jikana na ne, nima an kusa fara ki rana da Grandma, tsuch a wonderful and great day, how I wish you were here amriya, da farin ciki na bazai misaltu bah. Daukar paper dake kan kujera Yusuf yayi, sannan a hankali ya fara bude takardar, daga karshe yayi nasaran bude shi baki daya, kurawa takardar ido yayi sannan ya fara karan tawa kamar aka. "Assalamu alaikum wa rahmatullahi ta'ala wa barakatu", ni'imar Allah, gafarar Allah, tausayi da kuma imani su kara tabbata a gare ku da Kuma ni baki daya. Ammi ina fatan kuna cikin koshin lafiya kamar yadda nake, wannan yaron da kuke gani, tabbas shidin ɗana ne, kuma Kalb ne mahaifin sa, ina fatan zaku kulamin dashi, ta yadda bazai san cewa ya rasa mahafiiya a rayuwar sa bah, Ammi inason ki zaba masa suna wanda ya dace dashi, domin kuwa ni bazan samu damar yin akan bah, saboda yaune rana ta, ta karshe a duniya, zan bar duniya kamar yadda na fada muku tun farko, ina fatan zaku gafarce ni kura kuran da nayi wanda na Sani da wanda bansani bah ina fatan kuya femun, kuma ina fatan suma su ahalin kalb su gafar tamin, sannan inason bayan mutuwa ta ku nemi gawa ta, sannan ku suturtani ku kaini gida na na gaskiya, naso ace naga asalin mahaifiya ta da kuma mahaifina koda so daya ne kafun na mutu, domin kuwa saina fi samun salama, amma akan bai yu bah, na roke ku, idan kuka ga asalin iyaye na, kuce yarsu ta bar musu wasiha cewa, meyasa suka rabu dani?, meyasa mahaifya ta, ta tafi ta barni, ba tare da ta waigo taji ya nake bah, ya nake ci nake sha bah. koda so daya bata taba nema na bah, amma ni koda yaushe cikin tsimayi zuwan ta nake, kuce musu ni banji haushin su bah samm, ko kadan banga laifin su bah, saboda bansan dalilin su na rabuwa dani bah, amma dan Allah kuce wa Iyaye na, tunda basu taba jin ya bugun zuciya ta ke tafiya bah, basu taba jin koda murya na bah, basu taba ganina bah, kuce su taimaka su zo jana'iza ta, domin bazan cigaba da kasan cewa a raye bah, zan mutu ba tareda nayi ban kwana da kowa bah, aka tawa kaddarar tazo, aka zan amashe ta, dan Adam baya taba guje wa kaddarar sa koh yayane, duda nima bah mutun bace, amma nima ina da tawa kaddarar. hakika ahalin Kalb da kuma Ammi mutane ne na gari da kuma amana, samun irin ku a wannan duniya da wuya, bansan da wace kalma zanyi amfani wajan gode muku bah, domin kuwa kunyi min abubuwa mara misaltuwa, na hajiye dana, kuma ina fatan zai samu kulawa da tarbiya kamar yadda uwa ta gari take bawa ɗan ta koh ƴar ta, Zanyi kewar ku baki daya, Ammi zanyi kewar murmushin ki, gaba daya zan yi kewar ku, ina fatan zaku ga wannan sakon, inaso wannan sakon ya isa ga ahalin su Kalb, ina fatan gaba daya kuyi tsawon rai, zanyi kewar ahalin Kalb, Allah sarki, yanzu aka zuciya ta zafi take min, na nemi kuka na rasa, zuciya ta tana yimin radadi sosai, yadda nake rubuta wannan sakon, gabadaya kaina da jikina suna min ciwo sosai , ina jin radadi da kuna sosai, yanzu aka saura sa'o'i biyar kafun na mutu, zan mutu ba tareda na kawar da faruwar akan bah, hmmm duniya rumfar kara, wanda ya bita a sannu zai dace, ni na tafi, zanje na tsimayi jiran mutuwa ta, domin babu wanda zai dakatar da faruwar akan, ina son kusan cewa ina sonku sosai, da ace mutane suna mutuwa su kuma dawowa rayuwa, da zanso ace na dawo a matsayin mutun, kuma na kara haduwa daku a Karo na biyu. Nasan da cewa mutuwa ta zata girgiza ku sosai, za kuji zafin mutuwa ta, amma kuma karku damu zafin na zuwa wasu lokaci kalilan ne, nan da wasu kwanaki zaku manta da komai, dama kowa mamaci ne, koda yau ban mutu bah, toh watarana yana nan dazan mutu, babu wanda zai zo duniya ba tare da ya koma ga mahaliccin sa bah, dan aka kada kusa kanku a damuwa, zama daku yasa na gane banbamcin soyayya da kuma kiyayya, yasa na gane banbamcin rikon amana da kuma cin amana, na koyi abubuwa da dama masu kyau a wajan ku, cikin ta harda sallah da kuka sa na fara yi, yanzu ina alfahari kasance wa ta musulma, mai rikon addini da kuma ibada, bansani bah ko ku, kun karu dani, amma tabbas ni na karu daku da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89