Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 80

Chapter 80

Aljanar ruwa Ce Book 1 Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

54 TO 55 ,___________________________________ Idan ran Mom ya kai dubu, toh ya ɓaci?, cikin baccin rai tace, naga alamin kuna da mai tsaya muku Koh?, domin banga alamin tsoro a tattare daku bah, kuma ni akan bai min dadi bah, dole ne na dawo da wannan tsoron cikin zuka tanku. "Khalid yace, sai dai mu, mu dasa miki tsoro, amma ke dai baki kai bah, domin kuwa kunkuru ba zai ce zaiyi gasar gudu da barewa bah. Dan aka ki koma inda kika fito, domin kuwa bamua da bukatar ku. Gyaran murya "Zainab tayi tace, like seriously!, oh wait a minutes, kuna tunanin da mun zone domin muyi sulhu, that's impossible, idan kuna ma tunanin akan toh ku maida ta tatsuniya, domin kuwa bala'i, ne ya kawo mu, kuma kowa saiya ɗaɗana kuɗar sa. Maida Kallon ta kan yan qungiyan tayi tace, maza _maza, ku daddaure su yanzu nan, babu bata lokaci suka nufi kansu Kabir da zimmar daure su, A hassale gaba dayan su Grandma, suka dunkule hannu sannan suka kai musu naushi, ganin akan yasa gaba-dayan su yan qungiyan asirin suka yi kansu, kokawa gaba daya suka shiga yi, babu abinda kake ji a gidan sai karan naushi. Yayin da gefe guda Grandma ta daura ɗan kwalin ta ƙugu, sannan ta kama kan daya daga cikin yan qungiyan, sannan ta gantsara masa cizo a kai, ihuu ya saka, yayin da yake kokarin guduwa, amma ina karfin tsohuwa ya wuce wasa. Saka kansa grandma tayi a hammata, sannan ta fara zuba masa rankwashi ba kakkautawa, sannan ta ɗauki iron mai zafin jaraba, ta ɗoɗana mai a duwawu ta fara ironing din duwawu nasa. Sannan tace, Yoo, wallahi dani kuke zance, Ni halimatu sadiya, za'a kawo wa hari ina cikin gidan ɗana, toh a yau saina nuna muku fushi na, dan wallahi gaba dayan ku yau saina gasa muku duwawu, sai naga duwawun ya gasu sosai, ta yadda Koh da zama ba zaku iya yi bah. Tana kaiwa nan ta cigaba da gasa musu duwawu daya bayan daya. Ihuun!, yan qungiyan Mom ne gaba daya ya cika gidan, yayin da aka rasa mai ceton wani. Faduwa Nadira tayi kasa, yayin da daya daga cikin yan qungiyan ya nufe ta da wuka, wai gawa tayi bayan ta domin ta dauki abinda zata kare kanta dashi. Idanuwan ta ne suka sauka akan wayan electric, da sauri ta mike tare da daukar wayar, sannan ta dauki bottle water akan dining ta watsa wa yan qungiyan. Daga bisani kuma, tayi wa su Kabir alamun su matsa daga wajan, babu bata lokaci a tare gaba-dayan su, suka yi saurin barin wajan suka hau kan dining, Ganin yan qungiyan Mom na ƙoƙarin haurowa, ya sata saurin sakin wayar, ihuun! tsoro gaba-dayan su suka saka, yayin da suke kokari guduwa!, cikin rashin sa'a lantarki yaja su, ji kake pass, girrr, pass. Ganin babu sarki sai Allah, yasa Mom da Zainab yin kurin guduwa, hatake gaba dayan su, suka sha gaban su. Murmushi Grandma tayi!, sannan tace, "Karima ina kike shirin zuwa?, wato yau kinga fadan yan China Koh, toh mun gama dasu, yanzu ku ya rage zamu yi fadan bahubali daki. Tana kaiwa nan, ta janyo rigar Mom, hatake Mom ta fadi kasa, yayin da ta saki wani kara mai razanar wa!, yayin da zoben dake sanye a yatsar ta yayi haske. Kwashe wa da dariya Mom tayi!, sannan tace, Allah sarki ita wacce ta bada rayuwar ta akan ku mah baku damu da ita bah, tana chan tana mutuwa, Ni kuma gani nan na mallaki zoben ta, yanzu shikenen zan zamo sarauniya gaba daya aljanun da Mayu, zan samu karfin iko mai dimbin yawa, zan zamo shugaba wacce babu kamar ta. tana kaiwa nan ta kuma fashe wa da dariya. Gaban kowannen su ne ya fadi!", yayin da zuciyoyin su ya fara dukan uku -uku, jin budewar kofa yasa gaba-dayan su kallon kofar shigowa, ganin su Ammi" ga jariri rike a hannun ta, yasa kowannen su yin mamaki. Kabir ne yayi karfin halin fadin", Ammi meyasa na ganku a firgice, kuma sannan wannan jaririn waye?, ya karasa maganar yana mai kallon jaririn. Bashi amsa Doct Khadija tayi da fadin, wannan jaririn ba dan kowa bane, sai naka, kuma a halin yanzu muna da lokaci kalilan daya za muyi amfani dashi wajan cetan mahafiyar sa daga mutuwa. Zaro idanu, gaba-daya suka yi, yayin da Kabir yace kenan wannan ɗana ne?, Ammi da muryar ta ya ruga ya dashe tsabar kuka, ta bashi amsa da cewa kwarai kuwa dan kane, yanzu mah ba wannan bah, dan Allah ka taimaka, ka futo da wannan zoben, domin cetan matar ka, if not we are going to loose her. Aaaaa!, Kabir ya fada a tsawa ce!, dafa kansa yayi tare da fadin, she will not die, ba zata mutu ta barni bah, dole ne mu ceci rayuwar ta, meyasa zata tafi?, bayan kina bukatar ta, ina buƙatar ta, ɗan ta mah yans bukatar ta, bazai yu ta tafi bah, we need to do something. Karban yaron Nadirah tayi daga hannun Ammi, sosai su Grandma ke ya bawa da irin kyau da Allah ya ba shi, ba suyi mamaki bah sai yadda suka ga jaririn yana matukar kama da kabir, yadda kasan kamar an tsara kara. Kallon jaririn Momsy tayi tace, kenan wannan Grandson dina ne, Allah yayi wa rayuwar ka Albarka, menene sunan sa? Momsy ta tambaya, Ammi ta bata amsa da cewa, tukun nan dai, ba'a saka masa suna bah , ku nake so ku ku zaba masa suna. Maida kallon ta Momsy tayi kan jaririn sannan tace, from now henceforth sunan ka Aliyu hydar. Sunan mahaifina, mutum mafi soyuwa a gare ni, shidin ba ya kasance iya uba a wajena bah, shidin ya kasan ce rayuwa ta ne, ya kasance shidin duniya ta tane, dan aka kai zan rada wa sunan sa, domin kuwa Is only a special person i can give that name. Farin ciki ne gaba ɗaya ya lullube fuskokin su, hawaye Kabir yaji na ƙoƙarin zubo masa, da sauri ya sharw hawayen shi, sannan yace Hydar ina matukar sonka sosai, yanzu zamu tafi domin muje mu tseratar da rayuwar mahaifiyar ka. Kallon Mom yayi, sannan yace, Mom please ki bamu wannan zoben, dan Allah kinji wlh duk abunda kika tambaya zamu baki, but Please ki fara bamu zoben nan. Dariyar mugun ta Mom ta kwashe dashi!", tare da fadin impossible, kana tunanin wannan zoben zan bar shi shi, toh ku tsaya kuji tunda wannan zoben ya riga ya shigo hannu na, toh bazai futa bah, dan aka bazan bayar bah. Daukar takardar da Amriya tayi rubutu akai Yusuf yayi, sannan ya fara karan ta musu, jikin kowannen su ne ya dau sanyi, yayin da tsoro da fargaba gaba daya ya cika cikin zuka tansu, hatake suka ji wani irin tausayin Amriya ya kama su, yayin da hawaye ya fara sauka akan fuskan kowannen su. Kallon Mom Ammi tayi, hawaye na sauka kan kuncin ta tace, "Karima, tunda nake ban taba tunanin zaki yi min aka bah, kada ki manta kefa yar uwa ta ce, yanzu abun duniya mah zai iya raba tsakanin mu Karima, Hada hannayen ta guri guda Ammi" tayi, sa'annan tace, na roke ki,

Table of Contents

Chapters

89 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});