Chapter 49
Chapter 49
kidamu da wannan babu abunda zan masa .kinajina idan kinje gida jigsaws mahaifin ki usman cewa dole ya hallarci taro yau domin akwai muhimmiyar abu dazan fada. Zainab tace toh uwar shedanu, ni kinga mah nagaji da kayan likitocin nan Allah, Allah nake na je gida na ciresu, zainab tace yauwa Mom kada kimanta kishafa mata wannan laya abayan tah idan tasha maganin Kuma please kada kimanta maganin bita zaizai dakuma na mallaka dakika ce zaki bani yau a taro Mom tace Duk wannan bah matsala bace kedai kawai ki hada Kai dani mu kashesu domin na zama shugaba a qungiya, idan mukagama toh koh kaina kikace na sare miki zanbaki. Zainab tace banda dai cire kaii, sai anjima sai mun hadu a qungiya, Dan Allah ki kulamin da kabir Dina. Okay mom tace, tareda lashe wayan. Tsaki taja tareda fadin bakuga komai bah wlh yanzu aka fara wannan yakin . Sainasa zaman duniyar nan ta gagari kowanne daga gidan nan. Juyawarta keda wuya taga Ummi, fuskanta Duk shabe shabe da hawaye. Jikinta sai karkarwa yake, Gaban Mom ne yafadi, inda tace kalisat yaushe kika shigo dakinan. Tafada cikin faduwar gaba. Tafara nufan inda Ummi take, Jada baya Ummi tafarayi tace kada... ki matso.. kusada.. Ni, tafada cikin sheshekar kuka. Bantabah tunanin kina neman rayukan ahalin nan ruwa a jallo bah, Bantabah tunanin aka daga gareki bah. Dama ke muguwa ce, Dama ke azzalumace Mara imani Mara tausayi, meye wannan ahalin suka rage ki dashi, mene kike bukata a duniyar nan da DAD baiyimiki bah. Na tabbata soyayyar da yake miki batakai ta aunty amarya bah, amma aka kike so kikashe mana iyaye, sannan muma ki Gama da tamu rayuwar. Wace riba zakici kenen. Me muka tare miki, meyasa saboda me, menene ribarki na aikata aka, tabbas ke macuciya ce, kuma tabbas ke kike cin naman mu batareda kin gasa bah. Dafe kanta tayi Wanda yake mugun sarama mata tace, Meyasa, meyasa zai kasance kace zaki aikata aka, tabbas da labari aka bani koh wuyana za'a kama a yanke bazan taba yarda bah, amma nagani dakaina, Aba Mom ta karashe maganar hawaye na bin kuncinta. Hatta children da kika haifa baki Kyale bah wannan wace iriyar bakar zuciyace dake, tabbas idan aka ganki aka ga maciji toh afara kasheki kafun akashe macijin. Domin ke kinfi maciji illah. Dan Allah koda zaki kashe kowa, meyasa zaki kashe amriya wane laifi ta aikata miki, yarinyarda babu ruwanta, meyasa zaki saka marainiyar Allah aciki,saboda mee, saboda mee. Saboda itace ta Hana na kasheku tuntuni, zaro ido Ummi tayi tace kamar yaa kenen, Kwarai mah kuwa, cewar mom, wannan yarinyar amriya ta taremun abubuwa da dama kujerarda za'a bani a qungiya tasaka aka fasa bani domin, ban cika alkawarin dana daukarwa qungiya bah. Hatta kashe kabir da kwanakin baya dazanyi ita ta hana na kashe tah. Gashi yayi mugun tsananta amma Tana taimakarsa. Kuma batareda yasan itace ta ceci rayuwarsa a teku bah, ita ta hanani kashe shi tun tuni, Domin shine farko a lissafi wadanda zankashe. Tsuman tsaye Ummi tayi batareda ta iya furta wani kalmaba, tafara kukan bakinciki, Tace Allah sarki amriya baiwar Allah dama ita ce yake tsaron rayukanmu agidanan takesa nata rayuwar a hadari. Wannan wace iriyar kyakyawar zuciyace da ita. Tabbas yahya Kabir baiyiwa amriya hadalci bah. Tabbas wannan maganar bani kadaice zanji bah kowa na family saiya san Duk irin muganci dakike kullawa wannan family. Direct hanyar waje tayi, shan gabanta Mom tayi Tareda sakin murmushin mugunta tace kina tunanin bayan kinsan sirrina zanbaki kifuta ne da ranki, toh imppossible. Duk wanda yaruga daya San sirrina toh a ranar zai bakunci lahira, Dan aka, idan kinje Chan lahirar kya basu labari achan. Rike kan Ummi tayi Tareda bugawa akan bango. Kara ummi tasaka tana kokarin cetan rayuwata amma ina akan yagaza. Daukan katon kwalba mom tayi Tareda rotsa wa Ummi akai, faduwa tayi jini yafara zuba akanta. Fasa ihuuuu Salma dake kofan dakin Tana video Duk abunda Mom tafada akan ahalin dakuma abunda tayiwa Ummi, wani ihuun yakara fasawa, wayan datake video dashi ya sabule yafadi. Kallon kasa tayi tanemi wayan ta rasa. Jikinta ne tafara karkarwa, Kallonta Mom tayi tasaki murmushin mugunta tace yata salma kenen,. Kokarin guduwa Salma keyi. Amma kafun tayi wani yunkuri ta chafko Salman. Ihuun taimako salma tafasa inda mom tasa hannu ta buga mata baki, Cikin sheshekar kuka tace Dan Allah mom kada ki kashe Ummi, ni yarki ce ki kasheni tunda kekika kawoni duniya amma Ummi wacce bataji bah batagani bah, kuma sannan yarinya ce, na roke ki, kirabuda itah ki kasheni please mom Tafada tana hada hannayenta guri daya, tareda fashewa da kuka. Dariya Mom ta kwashe dashi tace ke yata ce bazan iya kasheki bah amma kuma idan takama don burina yacika babu Wanda bazan iya kashewa bah hatta kedinnan. Amma for now bazan kasheki bah domin ke yata ce amma Ummi wannan confirm ne saina gamada rayuwarta. Kuka salma takara fashewa dashi tace aba Mom Duk menene wannan Dan Allah ki kasheni ki rabuda ita, itama kamar yar ki fah take. Allah ya kiyaye, wannan bah zata taba zama kamar yata bah, kinga kina batamin lck, kibarni na aiwatar da abunda zan aikata akanta. Daukan wuka tayi tanufi inda Ummi ke yashe cikin jini. Durkushewa salma tayi Tareda rike kafar Mom tafara kuka Tana bata hakuri, amma koh kallo bata isheta bah, saima tureta datayi tafadi kanta yabuge bango. Hawayene yafarabin gefen fuskan Ummi, cikin matsanci ciwo da radadi tace, mom na roke ki, na yarda ki kasheni amma Dan Allah kibari naga mahaifiyata, inason namata kallon karshe, inason na mata sallama kafun na mutu. Yanda ruhi na zaifi kwanciya. Na rokeki dan Allah da manzonsa, kibari Nayi wa mahaifiyata Kallon karshe, nice mafi soyuwa agareta, idan kika kasheni batareda tayimin Kallon karshe bah nasan zata iya rasa rayuwanta, Na rokeki, takarashe maganar hawaye nabin fuskanta, mom bata yi wata wata bah ta tsinka mata mari, tace wato na kyaleki kije kitonamin asiri bah impossible. Daga wukan mom tayi zata soka mata. Ummi tace tabbas karshenki bazaiyi kyau bah, tabbas zaki haduda fushin Allah, Kin kashe rayuka bah adadi, sannan nima yanzu zaki kasheni, bkm ki kasheni bissmillah , rintse idanuwanta Ummi tayi Tareda yin Kalman sha'ada, hawaye na bin kuncinta. Batareda guntun imani bah Mom ta chaka mata wukan, Kara ummi tasaki, daga nan kuma numfashinta ya tsarke, alamun babu numfashin tattareda ita. Innalilahi wa innahilahi rajihun. Ihuun Salma tasaki, Tareda yinkan Mom a fusace, shake mata wuya mom tayi tace indai har burina zai cika banki na kashe kowabah. Buga kan Salma tayi ajikin bango, hatake salma tafadi sumammiya. Wajan wardrobe dinta tanufa, Tareda jan wardrobe din gefe, Hatake wani kofan ya baiyyana, Maganganu naji tafarayi wanda nima bansan metace bah, ba'afi mintuna biyu bah kofan ya bude, tanufi inda gawan Ummi yake tajata Tareda jefata cikin wannan kofan, Takuma daukan Salma tasakata aciki. Hatake kofan yarufe kansa. Azabure amriya ta tashi tareda kwallah uban ihuu dayasa gabadaya gidan ya amsa, sosai su nadira dake kusada itah suka tsorata. Tashi tayi Tareda nufa hanyar waje. Shan gabanta kabir yayi yace ke ina zakije, menene aka, cikin zafin rai da baccin rai tace, ka matsa, Kabir yace
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89