Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 49

Chapter 49

Aljanar ruwa Ce Book 1 Complete Hausa Novel 1,199 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kidamu da wannan babu abunda zan masa .kinajina idan kinje gida jigsaws mahaifin ki usman cewa dole ya hallarci taro yau domin akwai muhimmiyar abu dazan fada. Zainab tace toh uwar shedanu, ni kinga mah nagaji da kayan likitocin nan Allah, Allah nake na je gida na ciresu, zainab tace yauwa Mom kada kimanta kishafa mata wannan laya abayan tah idan tasha maganin Kuma please kada kimanta maganin bita zaizai dakuma na mallaka dakika ce zaki bani yau a taro Mom tace Duk wannan bah matsala bace kedai kawai ki hada Kai dani mu kashesu domin na zama shugaba a qungiya, idan mukagama toh koh kaina kikace na sare miki zanbaki. Zainab tace banda dai cire kaii, sai anjima sai mun hadu a qungiya, Dan Allah ki kulamin da kabir Dina. Okay mom tace, tareda lashe wayan. Tsaki taja tareda fadin bakuga komai bah wlh yanzu aka fara wannan yakin . Sainasa zaman duniyar nan ta gagari kowanne daga gidan nan. Juyawarta keda wuya taga Ummi, fuskanta Duk shabe shabe da hawaye. Jikinta sai karkarwa yake, Gaban Mom ne yafadi, inda tace kalisat yaushe kika shigo dakinan. Tafada cikin faduwar gaba. Tafara nufan inda Ummi take, Jada baya Ummi tafarayi tace kada... ki matso.. kusada.. Ni, tafada cikin sheshekar kuka. Bantabah tunanin kina neman rayukan ahalin nan ruwa a jallo bah, Bantabah tunanin aka daga gareki bah. Dama ke muguwa ce, Dama ke azzalumace Mara imani Mara tausayi, meye wannan ahalin suka rage ki dashi, mene kike bukata a duniyar nan da DAD baiyimiki bah. Na tabbata soyayyar da yake miki batakai ta aunty amarya bah, amma aka kike so kikashe mana iyaye, sannan muma ki Gama da tamu rayuwar. Wace riba zakici kenen. Me muka tare miki, meyasa saboda me, menene ribarki na aikata aka, tabbas ke macuciya ce, kuma tabbas ke kike cin naman mu batareda kin gasa bah. Dafe kanta tayi Wanda yake mugun sarama mata tace, Meyasa, meyasa zai kasance kace zaki aikata aka, tabbas da labari aka bani koh wuyana za'a kama a yanke bazan taba yarda bah, amma nagani dakaina, Aba Mom ta karashe maganar hawaye na bin kuncinta. Hatta children da kika haifa baki Kyale bah wannan wace iriyar bakar zuciyace dake, tabbas idan aka ganki aka ga maciji toh afara kasheki kafun akashe macijin. Domin ke kinfi maciji illah. Dan Allah koda zaki kashe kowa, meyasa zaki kashe amriya wane laifi ta aikata miki, yarinyarda babu ruwanta, meyasa zaki saka marainiyar Allah aciki,saboda mee, saboda mee. Saboda itace ta Hana na kasheku tuntuni, zaro ido Ummi tayi tace kamar yaa kenen, Kwarai mah kuwa, cewar mom, wannan yarinyar amriya ta taremun abubuwa da dama kujerarda za'a bani a qungiya tasaka aka fasa bani domin, ban cika alkawarin dana daukarwa qungiya bah. Hatta kashe kabir da kwanakin baya dazanyi ita ta hana na kashe tah. Gashi yayi mugun tsananta amma Tana taimakarsa. Kuma batareda yasan itace ta ceci rayuwarsa a teku bah, ita ta hanani kashe shi tun tuni, Domin shine farko a lissafi wadanda zankashe. Tsuman tsaye Ummi tayi batareda ta iya furta wani kalmaba, tafara kukan bakinciki, Tace Allah sarki amriya baiwar Allah dama ita ce yake tsaron rayukanmu agidanan takesa nata rayuwar a hadari. Wannan wace iriyar kyakyawar zuciyace da ita. Tabbas yahya Kabir baiyiwa amriya hadalci bah. Tabbas wannan maganar bani kadaice zanji bah kowa na family saiya san Duk irin muganci dakike kullawa wannan family. Direct hanyar waje tayi, shan gabanta Mom tayi Tareda sakin murmushin mugunta tace kina tunanin bayan kinsan sirrina zanbaki kifuta ne da ranki, toh imppossible. Duk wanda yaruga daya San sirrina toh a ranar zai bakunci lahira, Dan aka, idan kinje Chan lahirar kya basu labari achan. Rike kan Ummi tayi Tareda bugawa akan bango. Kara ummi tasaka tana kokarin cetan rayuwata amma ina akan yagaza. Daukan katon kwalba mom tayi Tareda rotsa wa Ummi akai, faduwa tayi jini yafara zuba akanta. Fasa ihuuuu Salma dake kofan dakin Tana video Duk abunda Mom tafada akan ahalin dakuma abunda tayiwa Ummi, wani ihuun yakara fasawa, wayan datake video dashi ya sabule yafadi. Kallon kasa tayi tanemi wayan ta rasa. Jikinta ne tafara karkarwa, Kallonta Mom tayi tasaki murmushin mugunta tace yata salma kenen,. Kokarin guduwa Salma keyi. Amma kafun tayi wani yunkuri ta chafko Salman. Ihuun taimako salma tafasa inda mom tasa hannu ta buga mata baki, Cikin sheshekar kuka tace Dan Allah mom kada ki kashe Ummi, ni yarki ce ki kasheni tunda kekika kawoni duniya amma Ummi wacce bataji bah batagani bah, kuma sannan yarinya ce, na roke ki, kirabuda itah ki kasheni please mom Tafada tana hada hannayenta guri daya, tareda fashewa da kuka. Dariya Mom ta kwashe dashi tace ke yata ce bazan iya kasheki bah amma kuma idan takama don burina yacika babu Wanda bazan iya kashewa bah hatta kedinnan. Amma for now bazan kasheki bah domin ke yata ce amma Ummi wannan confirm ne saina gamada rayuwarta. Kuka salma takara fashewa dashi tace aba Mom Duk menene wannan Dan Allah ki kasheni ki rabuda ita, itama kamar yar ki fah take. Allah ya kiyaye, wannan bah zata taba zama kamar yata bah, kinga kina batamin lck, kibarni na aiwatar da abunda zan aikata akanta. Daukan wuka tayi tanufi inda Ummi ke yashe cikin jini. Durkushewa salma tayi Tareda rike kafar Mom tafara kuka Tana bata hakuri, amma koh kallo bata isheta bah, saima tureta datayi tafadi kanta yabuge bango. Hawayene yafarabin gefen fuskan Ummi, cikin matsanci ciwo da radadi tace, mom na roke ki, na yarda ki kasheni amma Dan Allah kibari naga mahaifiyata, inason namata kallon karshe, inason na mata sallama kafun na mutu. Yanda ruhi na zaifi kwanciya. Na rokeki dan Allah da manzonsa, kibari Nayi wa mahaifiyata Kallon karshe, nice mafi soyuwa agareta, idan kika kasheni batareda tayimin Kallon karshe bah nasan zata iya rasa rayuwanta, Na rokeki, takarashe maganar hawaye nabin fuskanta, mom bata yi wata wata bah ta tsinka mata mari, tace wato na kyaleki kije kitonamin asiri bah impossible. Daga wukan mom tayi zata soka mata. Ummi tace tabbas karshenki bazaiyi kyau bah, tabbas zaki haduda fushin Allah, Kin kashe rayuka bah adadi, sannan nima yanzu zaki kasheni, bkm ki kasheni bissmillah , rintse idanuwanta Ummi tayi Tareda yin Kalman sha'ada, hawaye na bin kuncinta. Batareda guntun imani bah Mom ta chaka mata wukan, Kara ummi tasaki, daga nan kuma numfashinta ya tsarke, alamun babu numfashin tattareda ita. Innalilahi wa innahilahi rajihun. Ihuun Salma tasaki, Tareda yinkan Mom a fusace, shake mata wuya mom tayi tace indai har burina zai cika banki na kashe kowabah. Buga kan Salma tayi ajikin bango, hatake salma tafadi sumammiya. Wajan wardrobe dinta tanufa, Tareda jan wardrobe din gefe, Hatake wani kofan ya baiyyana, Maganganu naji tafarayi wanda nima bansan metace bah, ba'afi mintuna biyu bah kofan ya bude, tanufi inda gawan Ummi yake tajata Tareda jefata cikin wannan kofan, Takuma daukan Salma tasakata aciki. Hatake kofan yarufe kansa. Azabure amriya ta tashi tareda kwallah uban ihuu dayasa gabadaya gidan ya amsa, sosai su nadira dake kusada itah suka tsorata. Tashi tayi Tareda nufa hanyar waje. Shan gabanta kabir yayi yace ke ina zakije, menene aka, cikin zafin rai da baccin rai tace, ka matsa, Kabir yace

Table of Contents

Chapters

89 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});