Chapter 67
Chapter 67
ganin aka, suka nufi inda take tareda ririke ta, Grandma tace yauwa ku rike ta, shegiya annamimiya, munafuka, da sauri Adeef ya futa, ba'a fi mintuna bah, ya shigo da doguwar igiya. Kwace kanta daga garesu mom ke sanyi amma ina akan ya cutura, daddaure tah sukayi, saida sukayi mata d'aurin rago, sannan suka rabuda ita. yayin da Grandma ta wafce dorinan daga hannun ta, tace Wato ke nan uwar shedanu koh, bah uwar shedanu bah, in mah kece kakannin mayu da aljanu, wannan bai shafeni bah, munafuka mai hanci socket, bamu zaki daka bah toh ni barana nuna miki salon yadda ake jibgan karnuka da akuyoyi irin ki, Tana kaiwanan, bata yi wata wata bah, ta fara shauda mata ajiki, ihuu Mom ta fasa, da sauri Amar ya toshe mata baki da zani, ya yinda yayi mata alama da hannunsa tayi shiru, Tattaro karfin ta gabadaya Grandma tayi, ta fara zuba mata dorinan Ajiki bah kakkautawa, ihuu Mom keyi da iya karfin ta, yayin da takejin dorinan na Shiga har cikin kwakwal war ta da Jikin ta, cigaba da zuba mata dorinan Grandma tayi, tana mai fadin, Bake uwar shedanu bah, toh yanzu ki ceci kanki a wajena,ai yau koh wallahi Mai cetan ki a wajena sai Allah. Tausayin Mom ne ya Kama kowannen su na dak'in, Dad yace Mama ki rabu da ita kawai, Kibari Allah yayi ikonsa akanta, Grandma tace, bazan barta bah, Tunda ita uwar shedanu ce, toh ta kira shedanun tah zuzo su ceceta a wajena, Saida Grandma taga Mom ta cigata, sa'anan ta rabuda ita, tareda danna mata rankwashi akai, gabadaya Mom ta zama abar tausayi, idanuwanta sunyi jajir kamar tsohuwar mayya. Kallon shi gabadaya tayi, yayin da take hayyana irin azabtar war da zata musu . ------------------------ Ammi bara naje nasha magani, naji kamar zazzabi nason kamani, Tom shikenen yusuf amma ka tabbatar kasha fah, Tom shikenen Ammi insha Allahu zansha. yinkurin tashi yusuf keyi amma ya kasa, inda a karshe yayi nasaran tashi, Hatake jiri mai karfi ya dauke shi, luuu ya tafi tareda faduwa a wajan sumamme. Innalillahi wa innahilahi rajihun! Ammi ta fada tareda nufan inda yusuf ke yashe a kasa tafara jijigashi, ganin koh motsi Bayayi, yasa ta kwalla wa baban yusuf kira,, Cikin kankanin lokaci, baban yusuf ya bayyana a wajan, ganin yusuf a kwance bah alamun motsi a tattare dashi ga kuma Ammi Tana ta faman kuka, akan yasa yayi Saurin isa inda suke. Amina meyafaru da yusuf? Ammi ta Bashi amsa da fadin wallahi bansani bah kawai muna Zaune yace min yanajin zazzabi, shine yace min Zaije ya shafa magani, ban hankara bah naga ya fadi, dan Allah kayi wani abun. Jin kamar Hana kuka yasa Amriya futowa daga cikin daki, tareda nufan hanyar falo, abunda ta gani ne ya girgiza ta, da sauri ta nufi inda su Ammi suke, tana mai fadin, Ammi meyafaru? Tun daga abunda yafaru harkashe Ammi ta zayyane wa Amriya. Kallon yusuf Amriya tayi tareda shafa kansa ta rintse idanuwan ta. Da sauri ta Bude idanuwan ta tace, yana bukatar taimakon gaggawa, ya ka mata mu kaishi asibity yanzu nan. Mikewa Ammi tayi tareda hawa kan upstairs da sauri, ta dauko hijabin ta da kuma na Amriya. Daukan car key baban yusuf yayi, sanya hijabin Ammi tayi, sannan ta bawa Amriya itama hijabin, karba Amriya tayi tareda sanya wa ajikin ta. Yinkurin daukan Yusuf babansa keyi amma ina akan ya cutura, wani dabara ne ya fadowa Amriya, saita hannun ta tayi daidai inda yake yashe, sannan tayi amfani da karfin ta na ALJANAR RUWA. ta Fara ju yashi, Bah bata lokaci, yusuf yayi sama, hanyar waje Amriya tayi da gangar jikin sa, su Ammi naganin akan suka biyo bayansu, Masu tsaron gidan na ganin aka, sukayo wajan da sauri, yayin da kowannen su ya tada mota, shigar da yusuf sukayi cikin mota, bah bata lokaci suma suka Shiga mota. in da masu gadi suka bude musu kofar gate, daya bayan daya, motocin suka Fara futa har suka gama futa baki daya. motocin gidan ne suka jeru akan titin, ganin goslow yayi yawa, babu hanyar da zasu bi, gashi bangare guda Kuma trailers sun tare hanya, yasa Ammi dora hannu a Kai tace shikenen zan rasa dana kamar yadda na rasa y'ata, Amriya tace insha Allahu babu abunda zai faru dashi, da yardar ubangiji babu abunda zai same shi. Kallon motocin da suka tare hanyoyin Amriya tayi, ta rintse idanuwan ta ,tareda saita hannunta daidai wajan motocin, tafara yin wasu abubuwa da hannayen ta, Hatake motocin suka Fara rarrabuwa, ya yinda trailers din suka samu hanyar wucewa, Sosai mutanen wajan suka Shiga yin mamaki, daya daga cikin masu tuka trailers din yace, taya akan ta faru motoci su raba kansu, kuma ta bada hanya ba tareda wani ya tu kasu bah, tabbas abun al'ajabi baya karewa. Barin wajan su Ammi sukayi, direct general hospital suka nufa, inda nurses suka futo tareda bawa yusuf gado suka Shiga dashi cikin emergency room, bah bata lokaci suka Shiga bashi taimakon gaggawa. Zama Ammi tayi ta kafa tagumi, zuwa Amirya tayi inda Ammi ke Zaune tareda rungume ta tace, Ammi Dan Allah kada ki sa kanki cikin damuwa. Aduar ki kawai yake bukata. Kallon Amriya Ammi tayi tace, wallahi Amriya tsoron abunda yafaru baya nakeyi, banason tarihi yakara maimaita kansa, kanwarsa cutar Asma ne ya kashe ta, Yanzu shima gashi yana cuta, ina tsoron kada shima ya tafi ya barni kamar yadda itama ta tafi ta barni. Amriya tace ki kwantar da hankalin ki, Kisa a ranki cewar danki yasa mu lafiya. Daya daga cikin nurses din ce ta futo, Ammi na ganin aka tayi Saurin mikewa, tareda nufan inda nurse din ke tsaye, shima abban Yusuf ya nufi wajan. Amriya tace ya jikin Mara lafiyan, Nurse din ya basu amsa da cewar da sauk'i, amma danku yana bukatar jini sosai saboda jinin shi yayi kasa, kuma akan kan iya sa wani Bangare na jikin shi yasamu matsala. Dole dai hana bukatar blood group wato (Onegetive) in bah aka bah, am sorry to say, zamu iya rasa shi. Rass gaban Ammi ya buga, yayin da Abban yusuf yace nurse dole ne sai irin jinin sa za'a bashi? Nurse ta bashi amsa da cewar yes of course and we need the blood urgently, Tana kaiwa nan, ta shige ciki. Dafa kanta Ammi tayi, yayin da takejin kanta na mugun saramata , Abba yace toh mu bashi mana jinin koh, Kallon Abban yusuf Ammi tayi tace, ka manta mu bah O negative bane, ka manta bazamu iya bashi jini bah, Abban yusuf yace but why?, Ammi ta bashi amsa da cewar wato har ka manta yusuf Adopted child ne, ka manta da cewar yusuf bah dan mu bane, Sai a yanzu Abban yusuf ya tuna da cewar tabbas yusuf bah dansu bane adopted child ne. Kallon su Amriya tayi cikin rashin fahimtar maganganun su tace, Tunda yana bukatar jini ku bashi mana koh Kuma ni na bashi nawa. Kallon ta Ammi tayi tace, ke Amriya kina dauke da ciki bazai yu ki bashi jini bah, muma Kuma bazai yu mu bashi jinin mu bah, amma saboda me? Amriya ta tambayi Ammi, Ammi ta bawa Amriya amsa da cewar,
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89