Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 57

Chapter 57

Aljanar ruwa Ce Book 1 Complete Hausa Novel 1,213 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kunci, ga abun farin ciki ya riske ki, toh na taya ki murna kinada juna biyu, Zaro ido Amriya tayi gaban ta yayi mummunan faduwa, tace juna biyu fa kika ce, nidin Kuma, Kallon ta doct khadija tayi tace, me ya faru, kamata ai ace kina farin ciki, da irin wannan abun. Amriya tace, bawai bana farin ciki bah, tunanina daya ne shine nasan Kalb bazai taba son Dan da zai futo daga kar kashi na bah. Saboda nidin ALJANAR RUWA CE, Kuma babu abunda yafi tsana a duniyar nan sama Da jinsi na wato na Aljanar ruwa. Kuma ni ina matukar sonsa. Yanzu Gashi lokaci da ya rage min a duniya kalilan ne. Doct khadija tace kada Ki taba sare wa akan abunda kike so ,dole da jajurce warki da Kuma adua, shine zaisa ki cimma burin ki wanda yake kyakyawa. Bai ka mata ace ki shiga gidan cikin bakin ciki bah, ka mata ai ace kishiga cikin farin ciki da annashuwa, Yanzu ki kwantar da hankalin ki, kije gidan cikin karfin gwiwa, Kuma ki fada masa cewar ki nada juna biyu, Nasan tabbas bazai k'i ki bah. Maza ki tafi, ki Kara karfafa wa kanki gwiwa kada ki saduda tun,kije ki fuskan ce shi, nasan tabbas zai fahimta. Godiya amriya tayi wa doct khadija, cikin farin ciki ta bar wajan. Tareda nufa hanyar gidan su Kabir. Aunty amarya lafiya na ganki acikin wannan lokacin, murmushi Aunty Amarya tayi tace, kwarai kuwa lafiya, Shawara nazo na baka, badan ko bana sonka bah, sai don soyayya da nake maka da Kuma, yan gidan nan. Okay Tom ina jinki Aunty. Aunty Amarya tace , Kabir inason ka saura reni da kyau, inason fada maka abu dake cin rai na na wajan shekara da shekaru, Kabir! Dago wa yayi ya kalle ta sannan yace na'am aunty, Aunty Amarya tace, ina son na fada maka cewar, Duk abunda Amriya ta fada dazu babu karya acikin ta, tabbas abunda ta fada gaskiya ne. Mom itace ta kashe Ummi Kuma.... Bata karasa bah taji yace, Aba Aunty, aba Aunty, koda kowa zai biyi bayan aci dun duniyar mom ai bazaki ciba . Na tabbatar miki da cewar karya Amriya tayi wa mom, so take ta hada mu nida mom dina, Kuma bata San Allah yafi karfin tah bah. Murmushi Aunty Amarya tayi, sannan tace, Allah sarki Amriya baiwar Allah, kina taimako, kina sa rayuwar ki a hatsari amma basu San kina yi bah, Kace ka tabbatar cewa karya Amriya take koh! Kabir yace yes of course, am 100% sure that, karya take yiwa mom. Aunty Amarya tace tunda ka tabbatar, toh menene hujjar kah. Kabir yace ni Banida hujja amma nasan mom can never do such thing, idan mah tayi ribar mee zata ci, Amriya kawai yar leken asiri ce, maybe wani ne ya turo ta gidan nan. Wai kai Kabir Meyasa baza ka yi nadamar abunda kakeyi bah? Saboda mahaifiya ta, ta tsaya min, Kuma Duk mahaifiyar da ta iya tsaya wa domin Kare rayuwan danta, babu wata ma'alukiya da zata iya cin galaba akan tah. Kenen kana nufin Amriya bah mutuniyar kirki bace, Dai dai lokacinda Amriya ta karaso cikin gidan. Jin muryar Kabir tayi, taji yace kwarai kuwa, Amriya bah mutuniyar kirki bace, Chakk Amriya ta tsaya, Tareda jigina ajikin kofan Tana jin abunda yake fadin. Kabir yace tunda yarinyar nan ta dora kafa fuwanta a gidan nan, toh tun lokacin masifa da baka'i suke ta faruwa, tabbas yarinyar nan bah mutuniyar arziki bace. Da nafara dana sani abunda na aikata mata, amma shigowar ki yanzu, yasa na tuna da cewar tabbas mashekiya ce , muguwa Kuma, Mara imani. Baby macen da nafi tsana a duniyar nan sama Da itah. Na tsane ta, na tsane ta, tsana mafi muni, kinga Kare war Ta mah, bana son na kara hada ido hudu da ita, banason na Kara Ganin ta har abadan abada. Hawaye ne suka Fara gangaro wa daga idanuwan Amriya, hannunta ne suka Fara Kar kar wa, kuka ne ke shirin subuce mata Saurin rufe bakin ta tayi, Tareda rintse idanuwanta jin zuciyar take kamar zata futo.. Tashi tayi daga jikin dakin, inda kuka ya ci karfinta. Juyawa gabadayan su sukayi, inda Kabir yace waye a nan. Saurin rufe bakin ta tayi, Tareda Saurin barin gidan. bude kofan Kabir yayi yaga babu kowa, futowa Aunty Amarya tayi tace shikenen, ni zan wuce, ina fatan ka gane gaskiya. Tana kaiwa nan tayi fucewar tah. Ya mutse fuska kabir yayi tareda rufe kofan ya koma kan gado ya kwanta. Tafiya Amriya ta farayi batare da tana cikin hayyacin ta bah. Dafa kanta tayi wanda ke mugun Sara mata. Jiri ne yafara di banta, a daddafe ta karasa wajan junction. Tareda samun guri ta zauna. Kallon kanta tayi, ta fashe da matsancin kuka mai cin rai. Meyasa, Meyasa, wannan wace iri yar jarabbta ce, wannan wace iriyar bakar kaddara ce, Meyasa na ka sance a raye har yanzu. Dama na kasan ce a raye ne don kawai naga wannan ranar bakin ciki, ranar da bata da gobe. Meyasa tun tuni ban mutu bah, na tsane ka Kabir, na tsane ka, bana son sake hada ido dakai, bana kaunar kah, Kuma wannan ajiyar da ka bani, zan Adana tah har karshen rayuwa ta. Zan kula da abun ciki na har numfashi na, na karshe. Tabbas zan Nisan ceka, kamar yadda ka bukata , bazaka sake haduwa da koh inuwa ta bah. Karuga da ka Gina min tsanan ka acikin zuciya ta. Rayuwa tah da komai nawa, nasa a hadari don kawai naga, baka cutu bah, amma akan baisa ka gani bah. Ta karashe maganar tana mai fashewa da kuka, mai ratsa zuciya. 馃ス馃ス馃ス馃ス馃ス馃ス馃ス馃ス COMMENT & SHARE PLS 馃檹馃檹馃檹 ALKALAMIN 馃枈锔忦煐婏笍馃枈锔? BABY ISHA 馃挒馃挒馃挒 (AISHA M.B) 2/28/24, 22:12 - AISHA M.B (Baby isha): https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v JAJIRTATTAU WRITER'S ASSOCIATION 馃枈锔? (J.A.W) Rubutu baiwa ce daga Allah,jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan kasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauk'i鉁忥 ALJANAR RUWA CE PAGE 44?45 WRITTEN & DIRECTED BY BABY ISHA (AISHA M.B). ----------------------------------------- Kallon wajan gidan Amriya tayi tace, ya Allah, kada ka kawo abunda zaisa na Kara sanya kafafuwa na acikin wannan gidan, insha Allah baza ka Kara ganina bah na har abada, har abadan abada. Mike wa tayi, ta Fara tafiya, Chan cikin dajin wajan ta nufa ta tarar da doct khadija a Zaune, Kallon ta doct "khadija tayi cikin rudewa tace, yata Amriya, me yafaru?, Meyasa kike kuka? shin Kabir ya Kara bata miki rai nee? tambayar da doct khadija ta Shiga yi wa Amriya kenen. kuka Amriya ta Kara fashe wa dashin cikin, kuna da bakin ciki, tace doct khadija na aikata wani kuskure mara goguwa a rayuwa ta, wai shin yaushe kuka na da bakin ciki zai zo karshe, Nayi dana sani futowa daga ruwa nazo duniyar mutane, Meyasa banyi za mana a ruwa bah, Kalb ne yayi sanadin futowa ta daga ruwa , abunda na futo karba daban, abunda na tarar daban, Meyasa na tsane shi, banason sa, tunda aka yake so zaiga asalin tsana Daga Aljanar ruwa, wallahi, yanzu ji nake kamar na kashe shi nima na kashe kaina. Saurin rufe mata baki doct khadija tayi tace, Aa Amriya kada

Table of Contents

Chapters

89 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});