Chapter 72
Chapter 72
ciki, akan yasa na na dau alwashin cewa saina ga bayan ki, a lokacin na tafi wajan shugaba mu na Qungiyar devilish. nace dashi inason na kawar dake daga duniya, Inason ya zamto cewar ni kadai ce zan kasan ce a rayuwar Habib, Kuma nace da shugaban mu, banason ki haihu a gidan auren ki, inason ki kasance a koda yaushe kina kunci. Shugaba yace min, wannan abu mai sauk'i ne, amma kada nayi gaggawa, na bari lokaci zaizo da zanyi akan, yanzu koh yayi bazai shafe ki bah, domin kuwa a koda yaushe Amina tana yawaita adua tsari daga mutum koh aljan, bazai yu na kusan shi inda take da mugun nufi baht, bazamu iya tura mata aljanu bah domin kuwa akwai kariya a jikin tah. Amma zamu iya Hana ta haihuwa, saina ce mashi shikenen, mu Hana ta haihuwa, aka kuwa akayi, Amina bata taba batan wata, bare Asa ran tana da ciki bah. Lokacin ne Kuma na dauke dan khadija, sannan na ajiye shi a gaban gidan su, saboda kada su je suce a musu Adu'oin samun haihuwa, A gaban idona a lokacin naga kun dauke shi, sannan kuka dunga rainan shi kamar danda kuka haifa. Bayan wasu shekaru kawai naji labarin cewar kina dauke da juna biyu, hankali na bah karamin tashi yayi bah, babu bata lokaci na wuce cikin qungiya, sannan na sanar da shugaban mu halin da ake ciki. Shi kuwa ya tabbatar min da cewa, baza ki taba haifo wannan yarinya ta cikin ki bah, yana kaiwa nan ya dauki madubin tsari, da muke amfani dashi wajan kashe mutane da mukeson kashe wa, A lokacin madubin tsafin, ya hasko Amina a ciki tana kwance akan bed, shugaba na ganin akan ya nemi da daya daga cikin yan qungiyan ya kashe yarinyar dake cikin Amina, Aka kuwa akayi, daya daga cikin mutanen ya dauki sanda na tsafi, sannan ya saita daidai cikin Amina, ya fara magganganu, cikeda mamakin mu kuwa, muka ga ya kwalla uban ihuu, yayin da ancin shi da bakin shi ya fara zubda jini, sannan ya fadi a kasa yafara shure shure, yana kakarin mutuwa, daga bisani Kuma ya mutu a wajan. Hankalin kowa na kungiya bah karamin tashi yayi bah, Hatake shugaban mu, ya Kalli cikin dake jikin Amina, sannan ya ce dani, tabbas kawar da wannan cikin na jikin ta abune Mai wahala, indai har munason mu kasance a raye toh tabbas sai mun bar cikin nan, dole mu barta ta haifo yarinya, domin kuwa alamu ya nuna cewar yarinyar yar baiwa ce. Kuma jinin yarinyar nan zaisa karfin mu, da ikon mu ya karu, ya ninka na da, sai yace dani mu hakura ta haifo yarinyar. Jin akan yasa raina yakai kololuwar bacci, sannan nace Allah ya kawo ta duniya, in har da raina toh bazan taba barin yarinyar nan bah. Bayan wasu watanni, Allah ya sauk'i Amina, ta haifo santaleliyar yarta kyakyawa, son kowa, kin wanda ya rasa. A lokacin danaji labarin ta haifi yarinyar, yasa na fara shirye shiryen Yanda zan dauke yarinyar daga gare ta, Aka kuwa akayi, domin kuwa na hallaci Sunan Amriya, yayinda naga duk fuskokin ku lullube yake da farin ciki da annashuwa. Akan bah Karamin Kara tunzura ni yayi bah, a lokacin nayi kokarin dauke Amriya, amma Allah zai nufa bah, akan yasa naji bah dadi, amma ta bangare guda naji dadi, saboda nayi nasaran bata wani kwayoyin cuta tasha, Bayan watanni, kuwa ta Fara cuta, Tana rashin lafiya wanda ya tsanan ta, har kuka kaita asibity, ni kuma naje asibityn, sannan na dauke yarinyar, na mu sanya Amriya da wata yarinyar, na sanya mata kamanni Amriya sakk, sannan nayi fuce wa ta daga asibityn. Bayan fuce wa ta, nurses suka gano cewar yarinyar da na musanya ta mutu, sannan suka zo suka fada muku cewar yarku ta mutu, hankalin ku bah karamin tashi yayi bah, yayin da aka Baku gawar ta, kuka suturta ta, sannan kuka kaita gidan ta na gaskiya. Ban nufi koh ina da Sabreen wato Amriya Bah, sai fadar mu na cultism. Bayan na kaita, na hajiye ta agaban gunkiyar mu, a lokacin shugaba ya dauki takobi, sannan ya nufi Amiriya da zummar kashe ta, lokaci daya muka ga ya kurma ihuu, sai ji mukayi ya naku da kasa,. Cikin fargaba da tsoro na mikar dashi, sannan nace masa, yanzu me zamu yi mu kawar da yarinyar, a lokacin yake Sanar dani cewar, me kashe yarinyar nan saiya shirya, babu wani mutum koh aljan, da ya isa nufan inda take da zimmar cutar wa, in kuma mutum yayi kokarin yin akan toh shi zai bar duniya bah ita bah. Jin akan danayi yasa gaba na ya fadi, sa'anan nace dashi babu wata hanyar da zamu bi mu nesan ta yarinyar da mahaifiyar tah, shugaba yace mun akwai hanya guda daya, saidai idan sauya mata halitta zamu yi mu turata Chan cikin wasu jinsi daban, sannan shine burin na zai cika. A lokacin nace ayi duk abunda ya kama ta, indai har zata Nisan ci inda Amina take babu damuwa, a lokacin Shugaba na, yafara wasu tsafa ce tsafa ce, inda a karshe yayi nasaran maida ta ALJANAR RUWA. Cikin tsoro da fargaba na kalli Amriya sannan nace yanzu ya zamu yi da yarinyar, shugaba ya bani amsa da cewar, na dauki yarinyar na kaita nesa Chan katuwar teku inda nasan bazasu Kara haduwa da mamar taba, aka kuwa akayi, na dauki Sabreen na kaita tekun garin Lagos sannan na jefa tah aciki. A lokacin nake ta murna cewar burina ya kusan cika, bayan komawa na cikin kungiya, na tarar shugaba ya ruga daya mutu, dalilin yinkurin kashe Sabreen da yayi. Ganin akan yasa, nasa aka kwashi gawar sa aka yi sadaukar wa dashi, sannan aka nada ni a matsayin shugaba na kungiya. Bayan wasu lokacin, na dunga mafarkai munana, wanda ake son daukan raina acikin mafarkin, ganin akan yasa nayi hanzarin nufa kungiya, Sannan nasamu mahaifa na mace, naci daga nan ban kar mafarkai bah. Kuma na bar farautar rayuwar Amina, nayi concentrating akan yadda zan ga bayan wannan ahalin. Hankali na, bai tashi bah, sai lokacin da naga Sabreen ido da ido a wajan kungiya, ta saka mayafi ta rufe fuskan ta sannan tayi mana gargadin cewa kada mukara bibiyar rayuwar Kabeer, hankali na bah karamin tashi yayi bah, ganin cewar tabbas ta dawo duniyar tah, Kuma nasan da cewar itace, A lokacin na Kuma tada makaman yak'i na, dole na kashe mutanen gidan nan, domin na cimma burina da Kuma na mahaifina. Kuma maganin dawo da ita asalin Mutum ni kadai ce nasan shi. Wannan shine. Innalillahi wa innahilahi rajihun! Innalillahi wa innahilahi rajihun, la'ila a'illa anta subha'anaka inninkun tun minan zalumin, Allahumma ajirni fi musibati. Abunda kowannen su ke maimai tawa kenen. Hawaye mai zafi ne ya farabin kuncin Ammi, Kallon Mom tayi cikeda takaici da bakin ciki tace, naji kunyar kiran ki yar uwata, yanzu ke kin rabani da farin ciki na, kina walwalar ki, bakya jin cewa fah akwai hakkin wasu akan ki. Wannan wace iriyar bushashiyar zuciya ce, toh ni yanzu bah wannan bah ki fadamin inda zansamu magani y'ata ta warke please na roke ki, Kwashe wa Mom tayi da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89