Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 85

Chapter 85

Galadima Family Book 1 Complete Hausa Novel 1,278 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

so taji ya....a ciki,shiyasa ya koma yi a waje. Sai wajejen magrib sannan ya maido ta gida,hararar kawai Ammi ta masa inda tace"to lallai Zuhra ta koma ɗakin ta don ba za'ayi abin kunya a sashin ya ba. Laulayin cikin na damun ta don ma ta samu sauƙin jirin sannan Dr jamila tana iya ƙoƙarin ta wajen bata kulawa,ranar Laraba Sauban yayi mata kyautar motar ta ƙirar MERCEDES_BENZ G - CLASS G500 MODEL 2022,babu wanda beyi farin ciki ba don motar babu ƙarya ta haɗu iya haɗuwa,ƴan uwa hakan suke kira suna taya Zuhra murya,da yake su Aunty labeeba duk basu tafi ba,kai kowa da murna yake, Zuhra kuwa jitayi kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta shiga,don koda wasa bata taɓa kawo za'a siya mata mota nan kusa ba,ba wai don babu ba a'ah sai don ko maganar sam basuyi dashi,ya bata a matsayin tukwici akan abubuwa da dama a cewar sa ma harda baiwar da Allah ya mata. ******* After one week gidan kamar ba'ayi sha'ani ba don duk sun wawwatse,inda Sauban shi ya cigaba da rainon cikin Zuhra tare da yimata duk abinda takeso,aikin gida ma kuwa tare sukeyi,shi yake kai ta school ya ɗauko inda da haka yake mata dubarin koya driving,weekend kuwa me gasken sukeyi, sosai Sauban ya dage da koya ma Zuhra driving Kuma lokaci guda ta iya,duk wanda ya gansu sai yaso kasancewa tare dasu,ranar da zata dawo daga school haka suka ci karo da Akeela inda wani me daidai ta sahu ke ta mata rashin mutumci kan kuɗin da tabashi be kai ba,har yana kiran ta ƴar maɗigo sai wulaƙata ta yake mutane har sun fara taruwa. Akeela kuwa sosai take kuka,idan ka ganta duk tayi laushi tunda bata rame ba,kawai da ka kalle ta zakasan lallai Akeela ta tuba tayi nadama,long hijjab ne a jikinta , gabaɗaya tayi sanyi, Zuhra da kanta tafita taje ta ƙwato Akeela don Sauban hanata yayi ita kuma taƙi, a motar tazo ta sanya ta,inda kuka sosai Akeela keyi, ta buɗe hand bag ɗinta takaima me adaidaita kuɗin da ita kanta bata san ko nawa bane, sannan tazo ta shiga sai lallashi Akeela take, sauvan ko yayi kicin kicin da face,babu alamun rahama ko kaɗan,nan Zuhra ta shiga bata baki har gida suka kaita, Zuhra na ƙoƙarin fita Sauban ya galla mata uban harara hakan yasa dole ta haƙura, Akeela buɗe motar tayi sannan ta zagayo ta dubi Sauban tace"Don Allah Sauban ka yafemin nasan ni mai lefi ce a gare ka,naci amanar ka amma Allah sheda ne na tuba,tuba irin na taubatun-nasuha don Allah ka yafemin"tayi maganar tana fashewa da kuka, Sauban yace"Allah ya yafe mana,ai ke yanzu duniya ma ta isheki"yana gama faɗar hakan ya zuge glass's ɗin motar ya mata key,beyi wata² ba ya fisgeta ya bar layin,wani irin kuka Akeela keyi don harga Allah tasan cewa lallai ta cuce kanta rashin Sauban matsayin miji asarar ne. 1months Sauban yayi suna zuba soayyayn su daga ƙarshe ya tattara yana shi ya nashi ya koma,wanda Zuhra taji kamar tayi ta kururuwa. ____________ Sauban koda ya koma sau biyu ya dawo a lokacin har anyi azumi har anyi babban salla don lokacin Zuhra cikin ta kusan six months ne dawowar da yayi na farko,cikin yayi girma na hankali duk wanda ya gani sai yayi magana,a lokacin da ya cika seven months wani kumburi Zuhra tayi kota ko ina,ga damuwa da ta sanya ma ranta na mutuwa,ita a kullum gani takeyi mutuwa zata yi hakan yasa lokaci guda jininta ya hau,sosai su Daddy ke mata faɗa don ransu ya ɓaci,gashi wannan karan da yake sun samu hutu har na wata guda hakan yasa duk inda ta zauna sai ta tsaya ma kowa a rai kowa na jinta,ita kanta Boɗejo wani nan nan takeyi da ita,haka Ummie itama sosai ke nuna mata kulawa, ɗaki guda suka cika da kayan baby unisex,don Sauban duk kayan da akasaa ɗakin daga abrod ne. A lokacin Mashahuda ta haihu baby boy ne hakan yasa yaci sunan Abbie suna kiran sa da Ashraf, hakan yasa tadawo gida bayan anyi suna acan,don ko sunan Zuhra bata je ba Sauban ya hanata,shiyasa bata da aiki kullum sai na tambayar Mashahuda yaya haihuwa yake da zafi ko kuwa? Sometimes Mashahuda murmushi takan mata tace"kada ta damu idan lokaci yayi zataji don shi haihuwa ba lallai wahala da wancan ya sha ba shi wannan ke sha,wani yana zuwa masa da sauƙi"kowa cikin tattalin ta da nuna mata kulawa. Sai alokacin Muneefa ta samu ciki na wata huɗu,inda daga Laila har Nihal ke ƙunshe da cikin su ɗan wata bibbiyu. Rammat itama haihuwa yau ko gobe. Haka rayuwa ta cigaba da daɗi babu daɗi har Rammat ta haifi Baby boy inda mahaifin Kareem ya sanya masa sunan Daddy suna kiran sa Aslam. ******** Bayan wata biyu lokacin Sauban ya dawo gida gabaɗaya saboda Zuhra cikin ta ya shiga watan haihuwa,sosai ta sake kumbura sai dai anci Sa'a jinin ya sauka,kullum da la'asar sai Sauban ya jata zuwa struggling hakan yasa yake ɗan jin dama dama. Wata ranar Lahadi ƙarfe 11 na dare naƙuda ya sako ta gaba,tun tana abinta ita kaɗai har Sauban dai ya tashi dama baccin sa rabi da rabi ne hankalin sa na kanta always. "Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un"ta furta tana yarfe hannu tare da duƙewa,cikin azama Sauban ya diro daga kan gadon a gigice ya nufeta yana faɗar haihuwa ce Baby? ɗaga masa kai Zuhra tayi ta kasa magana saboda azaba. Hakan yasa a gigice Sauban ya fice daga gidan ƙoƙarin fita yake but ya kasa hakan, gabaɗaya ya gama ruɗewa da gigice wa lokaci guda. Wayan shi ya ɗauka ya lalubo number Ammi,kusan 2misscall sannan ta ɗauka muryan ta da alamun bacci tace"Assalamu alaikum Sauban ya akayi? "Ammi Zuhra kizo don Allah"cikin sauri Ammi ta miƙe tace"haihuwar ce? Sauban yace"i think cuz tana shan wahala"Ammi ce tayi hanging call ɗin, Daddy ma tashi yayi,hakan yasa cikin sauri ta nufi apartment ɗin Mom ita da Daddy, Daddy da kanshi ya kira Baba Hasheem a waya ya sanar dashi,babu jimawa suka fito shida Mom ko wacce zani ɗaure akan kayan bacci tasa hijjab. Wayan Ammi ne yayi ringing cikin sauri ta ɗaga Sauban yace"Ammi ganinan a mota a waje". Amsa mishi tayi sannan suka fice wajen su suka shiga inda su Daddy suka ce duk halin da ake ciki su sanar dasu. Sauban kiran Dr Ahmad ya sanar dashi,inda akayi Sa'a Dr yana asibitin cuz night duty zaiyi. Suna Isa cikin hanzari aka karɓe ta sai labour ward. Nan fa aka shiga bata kulawa gabaɗaya Sauban ya ruɗe,cikin yardan Allah wajejen 3:00 ta sunkutu yaran ta biyu mace da namiji,ihun su ne ya cika ward ɗin. Aifa nan su Ammi sukaji sanyi ya ratsa musu,babu jimawa Dr jamila ta ƙarisu hannun ta ɗauke da Baby wata nurse ma ɗauke da Baby,atake anan Sauban yayi sujudur shukur,inda banda hamdala babu abinda su Ammi keyi, Sauban cikin sauri yace"yaya take?zan iya shiga na ganta?cikin sanyin jiki Dr jamila tace"dama tace"akira mata kai, Ammi tace"muma zamu iya shiga? Dr Jamila tace"Ea ai angyara ta". Koda suka shiga a kwance suka taradda ita inda sai murmushi takeyi,hannu ta miƙa ma Sauban tace"Yaya kaga Babyn mu ko?nasan ni ba

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});