Chapter 30
Chapter 30
kujerun yana America karatu. **** *NIGERIA* **** Ummie kuwa a natse tafito daga bayin bayan ta kammala wankan,cikin nutsuwa tashirya tasanya wata Dubai gown fara tass tare da mayafinsa mai Kama da hijjab don har hannayenta ya rufe mata, gadon ta nufa tafara dube-dube sai dai da alama bataga abinda take nema ba, dai-dai lokacin Zuhra tayi sallama tashigo hannunta dauke da basket din kayan abinci,ajiyewa tayi tare da nufo inda take saboda ganin yanda taketa bincike. "Ummie lafiya?ko wani abun kike nema ne? dagowa Ummie tayi fuskar ta dauke da alhini tare da mamaki tace"Wai casbaha na nake nema amma ko sama ko kasa babu shi kuma akan bed din na ajiye don ko sanda nayi sallan magrib anan na aje gefen pillow dinnan amma kinga babu,gashi na kaku dana tada sallar,tayi maganar tana cilla pillow din gefe guda. "Ummie please kije kiyi sallan bari naduba kafin ki idar angani. "Ok my baby! Ummie ta ambata tare da tayar da sallan,nanfa Zuhra tayi dai- dai da gadon harda su yaye bedsheet da duvet din sai can gefen saqon tsakanin matress din da gadon tagani aiko tajawo tare da kokarin maida duvet din,fasawa tayi tare da sake yaye kayan shimfidan ta kakkabe kan katifar sosai tayi mai tatas sannan tadau bedsheets din da duvet din taje can corridor dinda zai sadaka da toilet tabude laundry basket ta saka su,adai dai nan Ummie ta idar da sallan. Ikon Allah Zuhra daga neman casbaha sai Kuma a bige da gyaran gado? murmushi kwance akan fuskar ta tace"Ummie wallahi sunyi datti ne naga sosai ga kuma datti harda kasa-kasa akan katifar shiyasa nacire"takarisa maganar tana bude closet,wanda bangare guda yake shake da bedsheets colours mabanbanta,duvets nd etc. Jawo wani tayi colour daya da wancan sai dai zane ne ya bambanta shima sai kalura ne zaka gane,wannan karan bata dauko duvet ba dama akwai wanda take lulluba dashi still a gefen bed din,shinfidawa tayi takuwa liliye gadon tsaf tare da sake gyaggyara pillows din,bayan ta kammala tajawo stool gaban kujeran da Ummie ke zaune ta ajiye,tana kokarin dauko basket dinne takatseta"Kinga ai kan carpet zan sauka naji kafata nayimin tsami,kije kikira addan ku kice nace suzo ga abincin idan kuma a kawo musu ne to.Zuhra tace. "Ok bari nasanar dasu,tayi maganar tare da fita,jingina ummie tayi da jikin gadon tare da rufe ido a haka taji sallamar zuhra. "Ummie sunce gasunan zuwa,babu kuwa jumawa da shigowan ta sai gasu suma sun shigo,da sauri Adda zainab tanufo ummie fuskanta cike da murmushi tace"bilkisou har kin fito wankan ne?Ummie tace"aiko nafito Adda ai ko kafin nafito naga kuntafi. "Ea muma munje muyi sallan ne,hajiya Aliya tace"sannu hajiya bilkisou ya jikin naki? Ummie tace"Alhamdulillah ai naji sauki wallahi. "To Masha Allah Allah dai yakaro mana lafiya dai,ubangji yabarki da diyarki"tayi maganar tana me shafa kan zuhra tana dariya. "Hajiya Aliya kenan Amin nagode. Nan Zuhra ta shiga zuzzuba musu abincin kowa na zabar abinda zaici, kallonta Ummie tayi tace"baby ke kinsa abincin kinci? "Ea Ummie naci tare dasu Bodejo da Amma aimu faten alkaman Bodejo mukasha,Kinga kuma itama Amma tanada diabetes in so sai yau akayi danan yawa,kuma fa nasa musu wadataccen kayan ciki. Adda zainab tace"ah lallai diyar albarka kinaji da wadannan kakannin naki,nikuwa bilkisou yanzu kindena cin dan gauda ne?dariya Ummie tayi"mekika gani Adda? "A'ah tambayace kawai naga kwana biyu banjin labarin dan gaudan. "Uhummm Adda kenan shekarun da yawa inaji rabona da cin dan gauda tun sanda nakeda cikin Zuhra,kuma Allah inaso cinshi sosai. Kama baki hajiya zainab tayi"cabb!gaskiya shekarun da yawa,Anya kuwa wannan ko kingani zaki iya ci kuwa ma? Dariya ummie tayi tace"ci kuwa sosai,inafa son shi don kawai bansamu bane,kai duk da haka ma nina mance da wani abu wai dan gauda. "Aikuwa insha Allah gobe da sassafe zan dauki driver muje kasuwa munemo garin dan gauda don acan zan siya masara ta kuma nabada nika a hada min komai da komai sai dai dana tashi nazo nayi miki,yajin ma musamu wanda yaji tafarnuwa don nasanki da son tafarnuwa,takarisa maganar tana dariya zuciyar ta fal nishadi. Nan ko suka cigaba da hirarsu suna dinner abin gunin sha'awa. Washegari kuwa kamar yanda hajiya zainab ta alkwaranta haka ne tafaru don wajen karfe sha daya na safe tafara kwabin dan gaudan ta tayi na ummie daban sannan ta kwaba nata dasu Bodejo daduk dai me sha'awan ci, zuhra na tayata,babu bata lokaci ta cewa zuhra tacigaba da zuba dan gaudan da wannan yayi za'a zuba na ummie ne. _____________ "Tab ai wallahi kinbani kunya Akeela kitsaya wannan yarinyar ta farfada miki magana haka?babu abinda ke cinta sai bakin ciki da hassada dole tasan kika mallaki guy dinnan kin mata fintinkau,na gaba yayi gaba na baya ai sai tsintar hula,aike dai kibari kawai zamuyi maganin tane karamar 'yar iska"Suby tayi maganar tana karkada kafafuwa. Akeela tasauke wani ajiyan zuciya tace"ni ba wannan nake tsoro ba kada watarana tace zata tonamin asiri kunsan fa tasammu farin sani ta kuma san abinda muke aikatawa. Tabe mouth zuleey tai tace"to sai mene?su da babu abinda suka sani sai Shan minti da samari fa?abi wannan saurayi abi wancan. "To ai inaso kisan nata me sauki ne akan namu namu yafi nata muni,wallahi ni da ace wani a cikinsu zaiji wannan labarin to nida shiga GALADIMA FAMILY matsayin mata wallahi sai gani sai hange don bazasu taba bari na aure ya Sauban ba,shiyasa nakeso Allah nadena wannan harkan fa don ni duk abinda zai shiga tsakanin aurena da ya sauban gudunsa nakeyi don rasa sa wallahi babban asara ne kuma bazan jura ba,wallahi na rasasa zan iya mutuwa. Wani harara zuleey ta watsa mata a ranta tace" _Hmmm indai ina raye bazaki taba auren saurayin da nake mafarkin aura ba tunda nataso nasan waye Muhammad Taleeb Muhammad Sauban yatafi da imanina,muddin bazan sameshi ba wallahi kema bazaki taba samun saba._ Suby tace"Lallai Akeela keko wani irin so kike ma Sauban haka?kinmance ba'a hada soyayyar mommy data kowa?ina guje miki randa zaki juyama mommy baya don kuwa kinsan sai kinshiga cikin gagaruman matsala. "Huhhhh! Suby don Allah kukasance koda yaushe cikin yimin fatan alheri ba fatan tsiya ba,meyasa kuke kokarin fasamin kwanya ne?inaso kugane cewa ko wanne da matsayinsa a waje na,amma banaso Kuna hada soyayyar ya Sauban data kowa please"takarisa zancen tana bata face. Da mamaki duk suka dubeta,zuleey tace"harda ta mommy?wani banzan kallo Akeela ta watsa mata tace"bansaniba mtsewwww,wallahi zuleey kwana biyu kaman kina neman zama munafuka ce,inafa lure dake kina kokarin shiga tsakanina da Mommy wallahi shiru kawai na miki,hmm kicigaba. "A'ah dakata mana Akeela"zuleey tayi maganar tana mikewa"akan me zakice min munafuka?menamiki na munafunci?kidubi tsaban ido na kicemin munafuka?ko a girme na girmeki kibar ganin ina binki kamar rakumi da akala wallahi bashi zaisa na dauki cin zarafi ba. Itama Akeela a fusace ta hayayyako mata"kada Allah yasa kidauk...... "Guys!guys!! Haba meye haka?kun manta mudin suwaye?meyasa kuke kokarin bawa haters damar shiga tsakaninmu?gaskiya banji dadi ba,gaskiya banson haka inkuwa ba haka ba sai atafi wajen mommy. "Bama sai anje ba!!duk su biyun suka hade baki,murmushi Akeela tasaki tace"Shikenan kiyahakuri zuleey,fuskan zuleey kadaran kadahan itama tace"Allah yabaki hakuri tana kare fadar haka tamike tare da daukan jakanta tadubi Suby tace"ni zan wuce gida yanzu Suby. Murmushi Suby
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87