Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 39

Chapter 39

Galadima Family Book 1 Complete Hausa Novel 1,304 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

wayarsa,wani me suna Ashur shankeer ya kyalkyale da dariyan mugunta yace"lallai iska na wahal da me kayan kara sufa familyn su Oga da alama basu bama bare aure,auren zumunci sukeyi gabadaya,duban Sauban yayi yace"please Oga idan zakayi fighting din bamu ita nizaka mawa don ni nafi dacewa da wannan bby doll di.....dogon tsaki Sauban yayi tare da daure face babu alamun wasa ko kadan yace. "Look niba dan iska bane da zanje na tare yaran ciki na da shirme,inbanda abinku ai ku yafi dacewa dakuje kuyi ma kanki fighting,babu wanda ya isa ya siyamin raini wajen yarinya,ya karisa maganar yana mikewa tamkar ba shine yayi maganar ba domin kuwa face dinsa ko alamun bacin rai babu,toilet ya shige ya barsu sai surutu sukeyi, Taufeeq ne yashigo tare da sallama bayansa,zuhra ce da katon basket a hannu,shima hannunsa basket ne da flask na ruwan zafi suna tafi suna hiran nishadi,shigowan su parloun yasata dan tsuke face,cike da girmamawa ta rissinawa tafara gaishesu da turanci,ko wanne na amsawa cikin nishadi suke amsawa,tana ajewa ta musu sai da safe tafita cikin sauri,kicibus tayi da Aseef rataye da hakan baya,cikin sauri taja baya,shikuwa marairaice fuska yayi yana duban ta,takowa yafara yi zuwa inda take yana kanne mata ido irin na cikakkun 'yan barikin nan. Da wani irin gudu zuhra ta kwasa don harga Allah ita tana tsoron sa,tasan mummunan halinsa Wanda ba kow ya sani a family din ba,karasawa tayi apartment din Ammi don banda haki babu abinda takeyi. Su Adda Zainab da hajiya Aliya ma sunzo,sashen Ummie sosai ya cika da 'yan uwa da abokan arziki,haka sauran sashisshikan. ******* A gidan Guggo Laure kuwa shima gida yafara cika sosai da 'yan biki,Akeela sashin Baba sani ta koma da kawayen ta,inda banda hirar batsa babu abinda suke a tsakanin su,tare da kosawa gobe tayi domin kuwa an dauki buri a bikin nan musamman ma Akeela,banda dirkan magungunan mata dana matsi babu abinda takeyi,tagigita kanta a banza a wofi tana tsananin bukatan mijinta a cewar ta. *𝑨𝑺𝑨𝑩𝑨𝑹* π‘Ώπ’‚π’‰π’“π’‚π’•π’•π’š π‘ͺ𝒆πŸ₯° π‘³π’‚π’π’π’‚π’Š π‘¨π’π’’π’‚π’π’‚π’Žπ’ŠπŸ–ŠοΈπ’€π’‚π’‡π’Š π’•π’‚π’Œπ’π’ƒπ’Š.πŸ—‘ ️[6/9, 22:33] Xahratty (OUM AJMAL): πŸ‘¨πŸ½β€πŸ¦³ *_GALADIMA FAMILY_*πŸ‘¨πŸ½β€πŸ¦³ Story&Written By *FATEEMA ZAHRA LAWAL* Marubuciyar‡️ A DALILIN'YAR TSINTUWA. MIJIN ZAHRA. DIAMOND LADIES ( Daukar fansa)paid book. RUHIN AMRITA (FATALWA CE). Now *_GALADIMA FAMILY_* Page 45/46 ______Allah yasani tatsani Aseef hakanan tarasa dalilin da yasa take kokarin shiga rayuwata ita tama mance dashi a shafin zuri'ar su,to ina ya shiga kwana biyu da ba'a ganin sa yabace bat?tambayar da tama kanta kenan batare da tana tunanin samun answer ba,ajiyan zuciya ta sauke mai karfi tana karisa shiga apartment din na Ammi. *π˜ˆπ˜šπ˜ˆπ˜‰π˜ˆπ˜™* Washe gari wajejen 11:30 babu abinda ke tashi sai muryoyin maroka suna sanar da daurin auren nasu Muhammad Taleeb Muhammad(Sauban) & Akeela Mansir,Taleeb Abubakar Muhammad(Taufeeq)&Mashhudat Taleeb Muhammad sai Ma'aruf Kabeer Mainaera&Habiba Hasheem Muhammad(Muneefa) sosai marokan nan suka saki makoshi asake,kafin kaceme sai guda shima kansa ya fara tashi,tsintar kanta tayi cikin wani irin bacin rai a hankali zazzabi yafara shiganta,fitowan ta kenan daga apartment din Ummie tana kokarin shiga apartment din Bodejo ne taji an fisgota,jitayi ta fada jikin mutum a tsananin rude tare da tashin hankali tadago,ido biyu tayi da Aseef,kirjinta ne ya shiga bugawa jikinta ya soma rawa,bude mouth tayi da niyyar sakin ihu,hannu yayi maza yadora a saman pink lips dinta yana furta"Shiiiii don't say anything baby,yakarisa maganar yana bin jikinta da wani irin mayetaccen kallo,karfin hali tayi na fusge jikinta sai dai ko kadan be bata damar hakan ba don ba rikon wasa ya mata ba,cikin rawar jiki tasake dagowa hawaye na sirnano mata cike da bacin rai da tsiwa tafara magana"ka sakeni please,niba 'yar iska bace wannan mummunan habits din da kake boyewa da yardan Allah wataran sai asirin ka ya tuno,murmushi yayi kamar ba dashi take magana ba yafara matso da bakinshi kan nata bakin,fusgewa tayi cikin karaji ta furta"ka sakeni la'ananne,kasakeni I hate you,natsaneka natsane halayen ka da yardan Allah nafi karfin ka bazaka taba samun galaba a kaina,yakarisa maganar tanajin wani mahaukacin karfi yazo mata lokaci guda,dagewa tayi ta turasa baya,aiko tasamu nasara don sai da yayi tagaΒ² zai fadi abinka da mashayi dama ba wani karfine a jikinsa ba,da gudu ta kwasa tana me sake zaginta. Karkada kai Aseef yayi yana mebin jikinta da kallo,idanun sa sun kada sunyi jajir,yaji zafin zagin da ta masa,alkawari ya dauka duk bala'i sai ya dandana yarinyar kalmar da ya fada kenan yana me juyawa tare da wucewa,kaitsaye bedroom dinta apartment din Bodejo. Kuka ta fashe dashi me tsuma zuciya tana sake me tsinewa halayyan Aseef"natsani gidan natsani kowa, Allah ya jikanka Abbiey na am always miss yhu,I love yhu lovely father da kananan da ka sharemin hawaye na,ina begenka da kauna me tsanani,wani ciwon kai taji me tsanani ya saukan mata,kukan ta tacigaba dayi tana fadawa kan gadon ta kwanta,tanajin sanyi na ratsa ko ina na jikinta. Da kakalle fuskokin su angwayen zakasan lallai suna cikin farin ciki,hotuna aketa tayi dasu,kowacce budurwa burinta tayi pic da Sauban da abokansa musamman Saif da ishaq don sunfi kyau a bisa Ashur,shikuwa Taufeeq wurga idanuwa yake ko zaiga ta inda Zuhra zata fito amma sam be ganta ba,sosai yadan damu haka ya saki aka cigaba da hotunan,shima Shuraim yazo gidan sai laluben numbers dinta yake amma is not reachable ake cemasa, Aunty safeena ya tambaya tace bata ganta ba amma yabari zatasa a dubo mata ita,biki yayi biki taro yayi taro harga Allah Saif ya kamu da son Zuhra shiyasa ma yaketa wurga idanuwa ko zaiga gilmawar ta amma be ganta ba. A can sashen Bodejo ko Zuhra taci kukanta har ta gode Allah,a take anan wahalallen bacci yayi awon gaba da ita,Saboda zazzabi da ciwon kai dake neman zautata. Anci ansha anyi shagulgula karfe hudu aka Kai amare sashen Galadima inda suka hadu da Daddy, Abba, Baba Hasheem suka hadu suna ma amaren nasiha mai shiga jiki sosai,daganan aka kaiso sashen iyayen su mata, Mashahuda kadai za'a wuce da ita don haka tayi kuka sosai,gefenta Rammat ne keta lallashinta,nanfa motocin daukar amarya suka iso da ita da Mashahuda aka dauka don Mashahuda zata rakata gidanta. Wajejen biyar angama kwashe duk wanda zashi gidan amarya anwuce dashi, Mashahuda kuma sai gobe za'a wuce da ita tare dasu Aunty Maryam, Aunty falmata(safeena)sai wasu 'yan uwan Ammi. Dangin Ma'aruf sun tarbe amare da 'yan uwanta cikin mutumci da kulawa,kai tsaye sashen mahaifin Ma'aruf din aka kaita,babban mutum mai cike da dattaku nan fa yafara mata nasiha mai shiga jiki tare da Ma'aruf don babu kwana,daganan sashen mahaifiyar Ma'aruf din aka nufa da ita,itama tamata nata nasihar. Bayan magrib akafara dawo da mutane,inda acan kuma masu kawo Akeela suma sun iso,ana tafe da amarya wanda babu abinda ke tashi sai kida a MP3,manyan mata wsu ma duk sun haifeta sune keta kwarkwasa,sai dai ba wanda ya fahimci wani abu,yan mahaifiyata kuwa mamaki yacika ta don bata sansu a dangi ba,ganin rashin da'an na neman yayi yawa tadaga murya"Meye haka?Wai wacece me mp nan da take cika gidan mutane da kida?haba bayin Allah meyasa muke hakane mutane? za'a fa kaita sasan sirikanta ne ba dakinta ba,yo ko dakinta nema ai be kamata a shiga da ita da mp ba,takarisa maganar cikin bacin rai,wacce mp ke hannunta ne tafara magana"wallahi mama hakan ba wani Abu

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});