Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 72

Chapter 72

Galadima Family Book 1 Complete Hausa Novel 1,326 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

I will be back soon,zan nemo miki,love yhu ki kula da kanki"cikin kulawa yayi maganar yana duban Ummie yace"Ummie bari na samo mata tuwon ko wajen Ammi ne"yana faɗar hakan yafita be jira jin mezata ce ba,don shi kanshi sai daga baya ya fahimci irin katoɓarar da yayi, Ummie kuwa kallon Zuhra kawai tayi. Da gangar tace mata taje stairs ta ɗauko mata hand bag ɗin ta,miƙewa tayi tana ƙoƙarin dai-dai ta tafiyar ta ta nufi stairs ɗin a fakaice Ummie ta ƙare mata kallo tsaf,sai da takawo mata jakan sannan tace mata"Me yasa mu ƙafar ki ne naga kamar da ƙyar kike tafiya?Cikin sauri Zuhra tace"A'ah Ummie bigewa nayi da nazo saukowa daga stairs ɗazu,amma na samu sauƙi ma saboda yaya ya duba min"sosai Ummie ke mamakin ƙaryan da Zuhra ta lafto take shirga mata amma sai ta wata ce da faɗin"Ayya to Allah yaƙara sauƙi kin shiga sashin Ammin kune?girgiza mata kai tayi,tace"to tashi kije ki gaishe ta ai can ya kamata ace kun fara shiga ma"da to Zuhra ta amsa tana miƙewa cikin sanyi tafita tanajin wani irin fever a dalilin fama ciwon da tayi. Sashin Ammi ta shiga nan ta taradda Aunty Safeena tazo,aiko cikin murna taƙarisa shiga palour, dai-dai lokacin Ammi ta fito daga cikin kitchen, ƙoƙarin dai-dai tafiyar tata tasake yi,ƙamahin dadawa duk ya ɗumi palour, Aunty Safeena ce tayi carab tace"a'ah me kuma ya samu ƙafar naki? Zuhra ta ƙaƙalo murmushi tace"gurɗewa ɗazu nayi a stairs"Aunty Safeena tace"eyya Allah yaƙara sauƙi, Ammi bta ƙariso tana kama Zuhra ta zaunar da ita tace"Son yanzu ya fita yaje siyo nama ninan nama na yaƙare yace tuwo zakici miyar kuka"duƙar dakai Zuhra tayi cikin jin nauyin Ummie,cikin tsokana Aunty Safeena tace"Eyye ya Sauban har ɗan tuwo ya samu?a lallai dole yaje samu nama"Ummie tace"uhum tana miƙewa, Zuhra ma miƙewar tayi tana jin wani nauyi, Aunty Safeena tace"ba kunya za jiki ba magana zakiyi"ita dai Zuhra ba tayi magana ba cigaba da tafiyar ta tayi sai dai azaba takeji don har kan ta sarawa yake mata. Ammi ce ta jiyo tana ƙura ma tafiyar Zuhra kallo,wani tunani ne ya faɗo mata,cikin sauri ta kauda wannan tunanin,Zuhra kuwa shiga bedroom ɗin palour tayi kaitsaye toilet ta nufa fitsari ya matse ta,shaf ta mance ta ɗibi ruwan sanyi tayi tsarki dashi,aiko ta kwala wani azababben ihu tare da mahaukacin zaɓura, Ammi ne da Aunty Safeena suka shigo cikin sauri, Zuhra kuwa kuka takeyi jikinta na rawa don tabbas ta fama ciwon nata, Ammi tace"meyasa meki Zuhra?shiru tayi tana kuka ga uban ciwon kai da takeji, Ammi tace"ki faɗamin gaskiya me yasame ƙasanki?nan ma Zuhra shiru tayi taƙi ma Ammi magana,sai uban zufa da take yi tana gunjin kuka, duban Aunty Safeena tayi tace"ka mata falmata kuyi gefe ina zuwa"cikin toilet ɗin Ammi ta shiga ta haɗa ruwa me ɗan zafi sannan ta fito ta fice bata jima ba tasake shigowa,don ko zama Zuhra ta kasayi, Ammi ce ta fito ta kamo hannun Zuhra tayi toilet ɗin da ita,face ɗin Ammi babu alamun wasa tace ma Zuhra"cire kayan ki"ai ko babu musu Zuhra ta cire tanayi tana kare cikakkun ƙirjinta,kamota Ammi tayi ta shigar da ita ruwan tayi,tana zaunar da ita. Aiko wani zabura Zuhra tayi tana sakin kuka tare da girgiza ma Ammi kai, Ammin sake tsuke face tayi tace"koma ki zauna"Zuhra cikin kuka tace"Don Allah Ammi ki ƙyaleni da zafiiii, taƙarisa maganar tana kuka"falmata! Ammi takira Aunty Safeena,shigowa tayi sai dai taji bala'in nauyin ganin Zuhra a haka,Ammi tace"muka mata mu zaunar da ita cikin ruwan nan"anan Aunty Safeena ta fahimci abinda ke faruwa,aiko kama ta sukayi suka zaunar,inda Zuhra ke sakin wani wahalallen kuka na azaba,sosai ta basu tausayi, Ammi ranta ya ɓaci wato Son ya jima yarinyar nan ciwo kenan?tayi tambayar a zuciyar ta,sake canza ruwan Ammi tayi wannan karan ban da ajiyar zuciya babu abinda Zuhra ke sauke wa don tabbas ta gasu don har wani bacci ne ke fusgan ta a cikin ruwan. Fito da ita Ammi tayi ta kamo ta ta kwantar da ita,sannan tace ma Aunty Safeena suje su bari ta huta,fitan su kuwa babu jimawa wani wahalallen bacci yayi awon gaba da ita tana sauke numfashin wahala. Sauban ko koda ya dawo bega wani face wajen Ammi ba don tsuke face ɗin ta tayi,ɗan shafa kai yayi yace"Sorry Ammi traffic ne yau a garin"Ammi tace"umm to bani"miƙa mata yayi yana fita don ɗauko ma Zuhra magungunan ta da ta mance dasu a gida,koda ya dawo sashin Ummie ya isa, anan Ummie ke ce masa ai tana wajen Ammi,mamaki ne sosai ya kamashi don shi be ganta a wajen Ammi ba,fita yayi ya nufi apartment ɗin,zama yayi akan sofa,a lokacin Ammi ta fito kitchen, Aunty Safeena kuma na ciki, zama Ammi tayi gefensa, Sauban ne ya dubeta"Ammi Babyn Baby nanan ne?cikin rashin fahimta Ammi ta dubesa,cikin sauri yace"Opps i mean Zuhra"harara Ammin ta galla masa sannan tace"me zakayi mata? Sauban ya sosa kai yace"Dama maganin ta zan bata saboda ta manta bata sha ba? Ammi batare da ta dubesa ba tace"Oh dama bata da lafiya ne? Sauban yace"na manta ince miki ɗazu taɗan gurɗe da stairs shine mukaje hospital aka rubuta magani but normal ne"Ammi ta dubesa cikin mamaki saboda yanda yake kafco ƙarya one time,tsarguwa yayi da kallon da Ammin nasa ke masa. "Ba cewa kayi fever ne ke damun ta ba? Sauban ya sosa kai sannan yace"Dama wannan ne ya saka mata fever"Ammi tace"Ok to tana bacci idan ta tashi ka bata"cikin sanyin jiki Sauban yace"Okay Ammi,miƙewa yayi yana ajiye ledan maganin akan stool ɗin side ɗin sofa. Da kallo Ammi ta bishi. Zuhra bata tashi ba sai wajejen magrib,sosai taji daɗin jikinta matuƙa gaya koda ta miƙe sai taji wajen be takura mata kamar ɗazu ba,miƙewa tayi tashiga toilet ta ɗauro alwala,nan ta shiga gabatar da sallolin ta a tsaye ba a zaune ba. Ammi ce ta shigo,ganin tana sallah yasa ta juya tana cewa"dama zuwa nayi na tashe ki cuz anata kiran magrib. Koda Zuhra ta idar ta gama addu'o'in ta kasa tashi tayi tafita saboda nauyin Ammi da takeji,ana haka Ammi ta dawo"Au kin idar shine kuma kike zaune?miƙewa Zuhra tayi Ammi tafita itama tabi bayan ta. Daddy, Aunty Safeena, Sauban da yaran Aunty Safeena mace da namijin duk suna dinning,cikin sauri Zuhra ta ƙarisa wajen Daddy,shima ganin ta yasa gabaɗaya ya dawo da kulawar sa gareta"Daddy barka da gida?sannu da zuwa,murmushi kwance face ɗin Daddy yace"Barka mamana kina nan lafiya? Zuhra tace"ina lafiya Daddy"Daddy yace"Masha Allah,son na kula dake kuwa?ko yana cin zalinki?yayi maganar cike da zolaya yana duban Sauban,shiru Zuhra tayi a kaikace tana duban shi wanda gabaɗaya hankalin sa na kanta,duban Daddy yayi yace"Daddy ina kula da ita itama ta sani sai dai bazata faɗa gaskiya ba. Murmushi Daddy yayi yace"haka nakeso Allah ya ƙara muku zaman lafiya da fahimtar juna,amsawa sukayi gabaɗaya banda Zuhra da kanta ke ƙasa, food flask Ammi ta turo mata dana tuwo dana miya tace"Ga tuwon kinan sannan nasa miki na ɗumame"cikin farin ciki Zuhra taja kulan tana nuna tsantsar jin daɗin ta a fili tace"Nagode Ammi na"hannu takai da niyyar ɗauko plate a lokacin Sauban har ya ɗauko mata,aiko nan ya shiga serving ɗin ta a gaban su

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});