Chapter 26
Chapter 26
har wani irin sara masa yakeyi. Haka malam baba ya cigaba da aikinsa. Zuwa can yadubi galadima yace"Alhamdulillah malam Muhammad nayi nasarar magance matsalar nan sannan na hada musu wani dafa'i wanda insha Allah babu abinda zai sake faruwa a tsakanin su,komin tsafin me tsafi kuwa da yardan Allah. "Sannan akwai wasu addu'o'i da zan basu da ita da 'yan wanda zasu lazumci yinsa da yardan bi'iznillah babu abinda zaifaru. Duban Sauban yayi yace"Shima takwaran ka na hada mishi wasu zan bashi domin tabbas za'ayi kokarin bibiyar wanda ya lalata aikin koda kuwa ba'a gano shiba sai sunyi kokarin sabauta ko wanene. "Mungode malam baba Allah yasaka da alkhairi ubangiji yaja kwana Allah yayima rayuwa albarka. Cewar Daddy kenan cike da tsananin jin dadin yadda malam baban ya warware musu komai da yardan Allah da temakon sa. Godiya sukayi sosai inda Galadima yake cemai ga sadakan abinci nan yayi ma almajiran sa sannan anbiya mishi kujeran hajji. Nan yashiga godiya duk da ya nuna musu sunfi karfin haka a wajenshi Amma ina. ********* Sai yamma lis suka isa qauyen wajen bokan inda shima driver hajiya Aliya dan gari ne don suna shiri sosai ita dashi don har aikoshi tanayi wajensa a sirrince. Gidan da suka saba sauka a dan quyen gefen gidan boka nan suka sauka,zuwa bayan sallan isha'i suka shiga wajenshi. Da wani banzan kallo ya tarbe su,nan danan hajiya Aliya tasha jinin jikinta,a dan tulluwan kasan da suka saba zama suka nufa zasu zauna. "Kulllll! Ahirrr dinku Aliya ka kasa nan ku zauna. Jikisu har tsuma yakeyi saboda yanda yayi maganar. "Aljanu su huci zuciyar ka,shedanu su huci zuciyarka yakai mebiya mana bukatun matsalolin mu( _wa iyazubillah_) "Ya isa hajiya Aliya kunfi kowa sanin abinda kukamin kun batamin aikinda tunda nake babu aikin da nasha wuya akansa sama da wannan,me kuke zaton yafaru?yayi maganar yana zaro musu mummunan idanun saasu kama da attarugu saboda ja. Kunsan aljanu nawa aka konamin a aikin nan?tabbas wadanda sukayi aikin nan ba kananun bane,duk sharrin dan dagiya da masanu sai da aka konamin su,duk cikin aljanuna babu jajirtattu irin su. "Wallahi bazan kyale ko waye ba sai na dauki fansa akan abinda akayi musu koba yanzu ba. Su dai su hajiya Aliya sun kasa magana banda rawar jiki ba abind sukeyi. Duban dayan yayi yace"yanzu me kikeso a musu?don shiryawa sun ruga sunyi itada diyar ta sai dai wani zancen ba wannan ba. Jikinta na rawa tafara magana cikin rawar murya. "Duk da 'yar uwata ce ubanmu daya amma nayi mata wani irin tsana mafi muni, duk da cewa mahaifiyar ta tafifitani akanta tanuna min soyayyar da bata nuna mata ba amma inajin muguwar tsanar ta a zuciya ta, takasance ta taso da soyayyar mutane da dama ne a zuri'ah mu harda mahaifinmu,wallahi boka hatsabibi bana sonta kuma ba zan taba sonta ba,inason ka sabauta min bilkisou yanda ba zata moruba. "Hhhhhhhh boka hatsabibi ya shiga qyalyqala dariya,zuwa can ya daure face. "Aikin ki sai na sake nemo wasu aljanun kuma shedanu saboda kinsanta da rukon addini bata wasa da azkar to zanyi shiri na musamman akanta,don yanzu haka tana kwance a asibiti jinita ya hau a dalilin karya sihiri nan da akay ......... "Allah dai yakashe ta ma kihuta aminiya,cewar hajiya Aliya. Wani kallo boka ya watsa mata. "Ba Amin ba nine nan ajalinta,mutuwar ta a hannu na take,sai dai wannan aikin ba kamar ko wanne bane don inada tabbacin duk me zatayi se yaci,amma kema zakiyi wani aikin daga bangaren wasu ayyukan. "Ni Kuma?tayi tambayar tana zaro idanuwa. "Eah ke!wannan karan mata biyu zasuyi amfani dake,bi ma'ana zasu mu'amalance ki. "Kamarya yaya boka? Duban hajiya Aliya yayi yace"kiyi mata cikakken bayani. Nan hajiya Aliya tashiga yima aminiyar ta bayani yanda zata fahimta,ai bata bari rakarisa ba tadafe kirji tace. "Ni Zainab bantaba madigo ba kuma banjin zan iya aikatawa. Daga hajiya Aliya har boka daure fuska sukayi. Boka yace"to duk inda zaki babu me yimiki maganin matsalar ki muddin baki aikata wannan abin da nace ba. "Mtsewwww!hajiya Aliya taja tsaki tace kika ma aikata wadanda sukafi wannnan muni da sabo wannan ne bazaki iya aikatawa ba lallai baki shirya ganin nasara ba. "A'ah ba haka bane aminiya da girma na da komai aganni ina madigo? "Waye zai ganki?cewar hajiya Aliya. "Boka hatsabibi yace a gabansa za'ayi fah 😥 "Mtseww Kinga idan bazaki iya ba tashi mu tafi makwancin mu zuwa safe mu tafi gida. "A'ah matsalata dake saurin fushi aminiya,cewar hajiya Zainab. "Toh ai ke dince da kayan haushi,idan kin shirya kiyi magana. Da sauri ta daga kai alamun ta amince. Nan boka hatsabibi ya rufe ido yana wasu yare kafin kace wani abu wasu katta kattan mata biyu bakake sun shigo ta kofan,babu sutturan arziki a jikinsu. Ba hajiya Zainab kadaiba,hatta hajiya Aliya sai da ta hadiye wani irin miyau na firgita. ***** *KADUNA* **** Ansamu Ummie ta farfado tana tare dasu mommy, Amma da kannen ta maza, Abba ma yana asibitin don su Daddy ance suna hanya. Hawaye kawai takeyi tana ambatan sunan Zuhra. "Amma na manta da Zuhra a babin rayuwata wallahi ni naman ce wai bayan Taufeeq inada wata diyar,meyasa na aikata mata hakane fisabilillah? Takarisa maganar tana zubar da hawaye masu dumi da zafi. "Ba laifinki bane Ummie wannan duk wanda yagani ko yaji labari yasan aikine na sihiri akwai farraqu a lamarinku,ba gashi ba yanzu da akayi magani komai ya warware? Mommyn yara bazaki gane me nake nufi ba,Abbie ya rasu batare da na cika mishi burin shi ba naganin naja diyata a jiki,ya rasu yana tausayin diyar shi da fargaban halinda zata shiga na kiyayyata bayan bashi,kuma hakan baitaba shafan zaman mu ba. "Allah yasani duk wanda da sa hannunshi akan wannan lamarin ban yafe ba kuma sai Allah ya bimin hakki na. "Wallahi kuwa bazamu yafe ba, Amma tafada tana kuka. Dai-dai nan ne kuma su Daddy, Galadima, Bodejo, Ammi, Mom, Sauban, Zuhra suka shigo dakin bakunan su dauke da sallama. Ummie jikinta har rawa yake ta sauko daga bed din ta nufosu,zazzaro idanuwa takeyi kawai tana laluben ta inda zata ga Zuhra. Zuhra kuwa ganin ta nufo inda take ne yasa jikinta kama rawa ta runtse ido tare ruqunqume kwankwason Sauban gam,fadi take. "Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un don Allah Ummie kiyahakuri babu abinda na miki please bazan kara ba,na hadaki da Allah please kiyahakuri wallahi. Shesshekan kukan da tadinga ji daga maban bantan bakuna ne ya sata bude ido. Ummie tagani a durqushe tana kuka mai sauti, Amma ma da Bodejo kukan sukeyi. Duk da haka jikinta rawa yakeyi takasa sakin Sauban don ita batasan tama rikeshi haka ba,Ammi ne ta matso tare da kamota tazo da ita har gaban Ummie inda take durkushe. "Zuhra Ummien ki tadawo gareki, Ummien ki mai sonki tadawo gareki dama banace miki ba?kidena jin tsoro kinga kinsata kuka koh? Kamar wawuya haka zuhra takoma tana kallon Ummie tana kallon Ammi. Kamo hannunta Ummie tayi wanda gabadaya ilahirin jikinta yashiga rawa tafara magana. "Zuhra diyata kiyafemin bansan abubuwan da nake mikiba a baya hasalima nina mance ma na haihu tun washegarin sunan na manta ki a shafin rayuwa ta,don Allah kiyafemin. "Ni maisonki ne,ni me kaunar kine,ina tsananin begenki,please diyata forgive me my babe. Xahratty CE🥰
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87